Showing 78001 words to 81000 words out of 154779 words
mata baki. Sai dai bai san me ya saka ya yi mata haka ba ko ta masa wani laifi ne. Duk da ko da laifin ta yi masa ya dace ya hukunta ta irin wannan faduwar idan ya zo da tsautsayi za ta iya karyewa.
*Prison/Gidan yaro*
Gabaɗaya ya kasa zaune ya kasa tsaye. Sai zirga-zirga yake yi a ɗakin. Ya rasa me yake masa daɗi. Ya so ya haɗa hannu da ɗan ta'addan dake cikin gidan yari. Sanin hakan ba zai amfane shi da komai ba ne ya saka ya fita harkarsa.
Wayarsa dake kan gadon ya ɗauka, tare da lalubo wata lamba ya danna kira.
Bugu ɗaya aka ɗaga.
"Ka zo."
Shi ne iya abinda ya ce sannan ya katse kiran wayar ya ajiye.
Ba'a fi mintuna biyar ba sai ga wani ma'ikacin gidan yarin ya shigo.
"Tura mani account number ka?"
Take mutumin ya faɗa masa in da ta yi masa transfer na kuɗi.
"Ina son a kawo mani katon ɗin ruwa don ruwan sha na sun ƙare. Ina son sabulu da omo da dai abubuwan da ka siyo Mani last time. Sauran canjin sai ka rike."
Godiya mutumin ya yi masa tare da yi masa addu'a.
_Jidderh_
Bayan ta shirya zuwa wajen aiki ta biya ta wajen Yayanta dan su karasa maganar da suka yi da shi.
Bayan ta yi sallama a kofar ɗakin ya ba ta izinin shiga ne ta shiga.
Yana zaune a bakin gado ta gaishe shi. Ya amsa tare da cewa.
"Har kin fito za ki wuce aikin kenan?"
"Eh Yaya dama ina son ne na ji ya ka ji shawara da na kawo?"
"Ban ƙi ta ki ba Jidderh kamar yadda kika ce za ki Sanarwa amintaccen bodyguard ɗin sa in da aka tsare shi a cikin gidan kina ganin ba zai iya yiwuwa da shi aka haɗa baki ba?"
Shiru ta yi tana nazari kafin ta ce
"Na san zai ya aminta da shi kuma shi ne wanda kai tsaye yake iya shiga duk in da yake a cikin gidan."
"Idan da hadin bakinsa a ciki kika tunkare sa da zancen fa za ki saka kanki a matsala ne?"
"To sai dai idan jami'an tsaro zan fadawa zancen."
"Tab kina ganin jami'an tsaro za su iya shiga cikin irin wannan gidan ne kai tsaye su fara bincike ba tare da sun nemi izinin mai gidan ba ko sun sanar da su shi abinda ke tafe da su?"
Shiru ta yi cikin ɓacin rai ta ce.
"To ya kake so na yi wallahi ba zan iya barinsa cikin wannan halin ba."
"Kuma duk hanyar da kike ɗaukowa ba mai ɓullewa ba ce."
Ganin duk sanda ta kawo shawara kowace iri ce baya bata goyon baya ya saka ta tashi tana tuninin hanyar da za ta bi."
Rai a jagule ta nufi ƙofar fita ko sallama ba ta yi wa mutanen gidan ba.
Keke napep ta tare ta shiga mutane biyu ne a ciki ita ce ta ukun su.
Sai da aka sauke su ya kai ta har ƙofar gate ɗin *Asadullah mansion* ɗin tana sauka ta biya mai napep kuɗinsa ta nufi gate ɗin. Security na ganinta suka bude mata gate ta shiga.
Kai tsaye main house din ta nufa. Mummy ta tarar a Falo, ta gaishe ta ta amsa mata ba yabo ba fallasa.
Shiga ciki ta yi don gudanar da aikinta. Don sauran ma'aikatan gidan nan suke kwana ita kadai ce take zuwa daga waje. Da Mom ta nuna in dai zata dinga fita za'a sallame ta, Asadullah ne ya tsaya akan cewa a barta sannan Mom ta bar ta.
Jidderh ta juya ta kallo Mom kamar ta sanar da ita cewa ga in da Asadullahi yake sai ta fasa sakamakon ta tuna Mama mai aiki ta taɓa sanar da ita cewar Mahaifiyar Asadullah ta rasu. Hakan ya durƙusar da yinƙirinta. Don a wannan gabar ba ta son ta aikata abinda zai iya janyo wa Asadullah ya shiga wani hali.
Sai dai yadda gidan nan ke da matakan tsaro ta ya ya za ta iya fitar da shi ba tare de kowa ya ganta ba. Ga shi baya cikin hayyacinsa ballantana ta ji ta bakinsa ya bata mafita.
Abun da Jidderh ba ta sani ba shi ne an daina yi wa Asadullah alluran gusar da hankali da magunguna da za su yi masa illah. Saboda yanzu an zo gabar da suke so.
A hanzarce ta gama ayyukan da take yi sannan ta fara tunanin hanyar bi wajen da za ta je ɓangaren da aka ajiye Asadullah.
Har za ta bi ta ƙofar kitchen ta fice sai ta ji Muryar Hajiya Zulaihat wacce suke kira Aunty ta ce.
"Ke ina za ki je kike wani sanɗa?"
A firgice ta juyo don ta tsorata jikinta har rawa yake yi .
"Kallo ɗaya ta yi mata ta fahimci ba ta da gaskiya. Don haka ta sake tamabayarta a karo na biyu.
"Amm uhm amm zan je wajen Mama ne na taya ta aiki?"
"Wace Mama? Mama da ta gama aikinta ta fita kitchen."
Dawowa ta yi tana sunkuyar da kai ta nufi ɗakin masu aikin gidan.
Da kallo Aunty ta bita kafin ta ce .
"Zan gano ki ne yarinya."
Bayan kamar mintuna talatin ne ta sake fitowa cikin ikon Allah har ta bar sashen na wamdabya ganta.
Ta baya ta zagaya har ta isa bangaren da aka ajiye Asadullah.
Sai dai ƙofar a datse. Glass din window ta zuge sai suka hada idanu. Gabanta ta ji ya fadi rass.
Ganin kallon da yake yi mata. Don duk ganin da take masa cikin wani yanayi yake amma yau ga shi zaune yana kallonta sai dai an daure masa hannaye da ƙafa suka an rufe masa baki da salatef.
Ƙwalla ne suka cika Idanunta har suka gangaro. Ga mamakinta sai ta ga yana girgiza mata kai alamar ta daina kuka.
"Yallaɓai kana ji na kana gani na?"
Kai ya jinjina mata alamar eh. Farin ciki ya saka ta saki murmushi tana goge hawayen dake Idanunta.
"Yallaɓai ta ya zan iya fitar da kai ko na je na sanar da Mom kana nan?"
Kai ya girgiza mata alamar
"Aunty fa na sanar da ita?"
Nan ma kai ya girgiza mata alamar a'a.
"Na sanar wa Dad?"
Nan ma kai ya girgiza.
"Na sanar da amintaccen bodyguard ɗin ka?"
Sai a lokacin ya ɗaga mata kai alamar eh. A guje ta bar wajen tana murmushin jin dad'i.
Tana tsaka da gudu ta ji an finciko mata hijabi ta baya wanda har ya shaƙe mata wuya. Kafin ta ankare sai ta ji ta faɗi ƙasa tim.
Rai a ɓace Ammar ya kalli Hilal da ya tabbatar shi ya harɗe ƙafar Zahrah ta faɗi. Haba Man don Allah me ..."
Ɗaga masa hannu ya yi alamar dakatarwa. Dada da a tunaninta Zahra Faɗuwa ta yi ne ta kama ta daƙyar, ta iya tashi ga ƙafarsa zafi ga kabbnta da ya ɗilla da yatsarsa sai zugi suke mata.
Hawaye ne kawai take tsiyayarwa, don ita kanta ba ta san me ya yarda ita ba ta ɗauka ko da plate dake gabanta ta yi tuntuɓe. Sai dai lokacin da ta ji zafi a bakinta ta ga abinda Hilal ya mata sai ta danganta hakan da ihun da ta yi ne kasancewar baya son hayaniya.
Kuma ya saba cin uban duk yaran gidan idan sun yi hayaniya a in da yake. Hakan ya saka in dai yana wuri kowa ke kama kansa ya shiga tausayinsa. Don haka Zahra ta ta ga ya dakar mata baki ta ɗauka karar ihun ne baya so ba ta san shi ya harɗe ta da ƙafarsa ya yarda ita ba, don Idanunta na kan Ammar.
*Maman Ihsan ce*✍️
09065327995
[11/2, 7:57 PM] My Uwar Ɗaki: *GABAR CIKIN GIDA*
*NA*
Zainab Abdullahi K.N.T
(Maman Ihsan ce)
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
Page4️⃣0️⃣
Kuma ya saba cin uban duk yaran gidan idan sun yi hayaniya a in da yake. Hakan ya saka in dai yana wuri kowa ke kama kansa ya shiga taitayinsa. Don haka Zahrah da ta ga ya dakar mata baki ta ɗauka karar ihun ne baya so ba t san shi ya harɗe ta d ƙafarsa ya yarda ita ba, don Idanunta na kan Ammar.
Hawaye ne ke bin fuskarta yana gangarawa wajen ƙunnenta.
Taisayin ta ya saka Ammar ƙarasowa wajen ya kai hannu zai taimaka mata ya ji Muryar Hilal na cewa.
"Kada ka taɓa ta tun da ba Muharramarka ba ce."
Jin haka ya saka Ammar janye hannunsa rai a ɓace. Dada ce ta taimaka mata ta miƙe tana ɗingisa ƙafar suka shiga ciki. Dada sai jera mata sannu take ta yi.
Ammar ya kalle shi fuska babu walwala ya ce.
"Man me hakan ke nufi, idan ta karye ko ta yi targaɗe ko gocewar ƙashi fa? Ko da ta yi maka laifi ya kamata ka hukunta ta ne ta hanyar faɗa, ko duka ma yanzu ba kowane laifi ta yi za'a ce ayi mata duka ba, don ba yarinya ba ce ƙarama ta san me take yi."
Ko kallonsa bai yi ba idanunsa akan wayarsa kamar bai yi komai ba.
"Ga shi ina son na gabatar da kaina a wajan iyayenta kafin na koma London ga shi ka ɓata mani komai."
Ganin bai yi magana ba ne ya saka shi sake cewa.
"Yauwa sai ka raka ni mu je tare kai za ka yi mani jagora babban Yaya."
Wani kallon ba ka da hankali ya yi masa sannan ya tashi ya bar part ɗin.
Har ya kai bakin kofa ya ce.
"Zan fita yin wani aiki me yiwuwa na kai yamma kafin na dawo."
Bai tsaya jiran amsar sa ba ya fita, don shi ma Ammar ɗin baya da niyyar amsa masa. Don ya ji haushin abun da ya aikata.
Dada ta gasa wa Zahra ƙafa sosai sannan suka fito. Mai aikin Dada Inna Ladi ce ta shigo da sallama. Tattare kayan da suka ji breakfast ta yi ta kai kitchen.
Sai sannan Ammar ke jerawa Zahrah. Magani Dada ta bata ta sha sannan ta koma ɗakinta ta kwanta da taimakonka Dada.
Hilal kuwa zuciyarsa wasai ya nufi harabar gidan. Fita suka yi shi da sojojinsa a tare. Mota uku suka fita da ita.
_Mansur_
Bayan ya gana program din da zai gabatar ne kasancewarsa ɗan jarida ne. Yana zaune a office ɗin sa yana hutawa aka yi knocking. Izinin shigowa ya bayar yayin da abokin aikinsa mai suna Auwal ya shigo. Bayan sun gaisa ne ya ce.
"Mansur Adam Tafarki."
Kallonsa ya yi yadda ya kira cikakken sunansa sannan ya ce.
"Me kake so?"
"Fatima Zahrah Salis Tafarki."
Wani banzan kallo ya masa tare da tsuke fuska ya ce.
"Tashi ka fice mun daga nan."
Murmushi ya yi tare da cewa.
"Calm down my friend me ya yi zafi, walalhi ba da wasa nake ba Allah ya jarabe ni da son wannan sister ɗin taka ce."
"Wace ce sister ɗin ta wa?"
"Kamar yadda kowa ya san cewa daga familyn Muhammad Tafarki kuke wato kakanka, kowa ya san sunanka ne Mansur Adam Tafarki, kuma Zahra Salis Tafarki ƴar ƙanin mahaifinka ne ai ƴar uwarka ce ."
"Ba na da alaƙa da ita don haka ka fice ka bani waje, kuma kada ka sake zuwa Mani da makamancin wannan zancen, idan ba haka ba wallahi sai na maka rashin mutunci."
Mamaki ne ya kama shi don haka ya mike tare da cewa.
"Allah ya kyauta ."
Tsuki Mansur ya ja tare da bin bayansa da harara.
"Da ka san yadda na tsani yarinyar nan da ba ka zo Mani da wanann zancen ba. Mtsww."
_Ammar_
Kasancewar yana son barin garin ya saka ya yanke shawarar zuwa part ɗin su Zahrah da kansa.
Knocking ya yi a ƙofar falon, Sadik ne da ya shirya cikin kayansa na lauya yana sauri zai je kotu. Yana shirin shiga yin sallama da Ummi ne ya ji knocking ya nufi kofar ya buɗe. Ammar ya gani a bakin ƙofar duk da ya ɗan yi mamakin ganinsa kasancewar sa abokin Hilal. Kuma Hilal shi kansa ba gaida Abbi da Ummi yake yi ba ballantana wata alaƙa ta shiga tsakanin abokinsa da su.
Murmushi Ammar ya sakar masa tare da mika masa hannu. Gaisawa suka yi sannan ya ce.
"Suna ciki?"
"Eh bisimillah."
Shiga ya yi yayin da Sadik ya mayar da kofar ya rufe. Ammar ya zauna a kujerar yayin da Sadik ya shiga ɗakin Abbi tare da sallama. Ya same shi yana duba wasu file.
Abbi ya masa masa sallamar tare da cewa.
"Barrister ka fito kenan."
"Eh Abbi zan tafi ne sai ga wannan abokin Yaa Hilal ya zo yana falo."
"Wane abokinsa wanda ya zo daga Ingila ?"
"Eh Abbi yana falo yanzu haka."
Shiru Abbi ya yi kafin ya ajiye file ɗin hannunsa ya bi bayan Sadik zuwa falo.
Abbi na fitowa Ammar ya sauka daga kan kujerar da yake zaune ya durƙusa har ƙasa ya gaida Abbi.
Abbi ya amsa masa cikin sakin fuska da walwala tare da tambayarsa gajiyan hanya.
Amsawa ya yi da Alhamdulillah yayin da yake komawa ya zauna.
Ummi ce ta fito daga cikin ɗakinta ita ma kallon Ammar take yi tare da yi masa barka da shigowa.
Ita ma sai da ya durƙusa ya gaida ita kamar yadda ya gaida Abbi. Ita ma Ummin amsa masa ta yi cikin sakin fuska da walwala kamar yadda Abbi ya masa.
Ammar ya fahimci cewa iyayen Zahrah suna da mutunci da karamci. Kasancewar ya san ba zaman dad'i suke yi da iyayen abokin nasa ba, duk da sun san alakar dake tsakanin sa da Hilal sun tarbe shi da kyau .
Shiru ne ya biyo baya in da Ummi ta shiga kitchen ta kawo masa cake da ta haɗa sai kuma lemun kwali ta ajiye masa, kasancewar yau girkin mai aiki suka ci su ma .
Haka kwai Ammar ya tsinci kansa da jin kunya irin na surukai. Ya kasa ci ya kasa sha sai sunkuyar da kai ƙasa ya yi .
Abbi ne ma ke ɗan jan sa da fira, wanda ganin haka ya saka shi ma ya fara yin fitar. Sadik ne ya masu sallama ya wuce . In da Ammar ke cewa.
"Allah ya bada sa'a barrister."
Da Amin ya amsa yana murmushi ya fice.
Ɗan jimawa kaɗan Ammar ya yi masu sallama ya fice daga part ɗin. Duk da su ba su san me ya kawo shi ba amma ba su kawo komai a cikin ransu ba.
_Jidderh_
Jin ta a ƙasa ya saka ta saki ƴar ƙara tare da cewa.
"Wayyo Inna ta ."
Kallon tuhuma Aunty ta yi mata tare da cewa.
"Wace ce ke, kuma me ya shigo da ke cikin gidan nan?"
Sai a lokacin ta ɗaga kai ta kalli Aunty tare da cewa.
"Ni ba kowa ba ce face marainiya."
"Me kike ƙullawa a cikin gidan nan?"
"Wallahi ba a abinda nake ƙullawa sai alkhairi."
Tsuke fuska Aunty ta yi tare da cewa.
"Duk yanayin rashin gaskiya ya bayyana a jikinki, ɗazu na fito na hange ki kina saɗa kika ce Mani Mama kike nema bayan kin san ba ta wajen. Bayan na koma ɗakina na hange ki kina biyiwa ta nan kina juye-juye alamar ba ki son wani ya ganki. "
Shiru ta yi don ba za ta iya fada mata abinda ya kawo ta wajan ba, musamman da Asadullah ya ce kar ta faɗa mata. Yanzu ya za ta fitar da kanta take tunani.
Maganar Aunty ce ta katse mata tunini.
"Ina saurarenki me kike yi a nan, wajen da ba kowa a wajen me kika je yi?"
"Kawai dai na ce bari na zagaya ne na ga Asadullah mansion ɗin na da girma ban sani ba sai...."
"Ke raina mani hankali za ki yi ne?"
Jan hannun Jidderh ta yi suka koma in da ta ga Jidderh ta fito, ta ce sai ta nuna mata abinda ta zo yi nan. Jidderh kuka ta saka mata tana cewa ba komai zagayawa kawai take yi.
Ganin wurin ba wani abu na daban ya saka ta kalli Jidderh ta tare da sakin hannunta tana mata gargadi akan ta tsaya iya abinda ya kawo ta gidan.
Jidderh ta wuce ciki tare da shiga ɗakin masu aikin gidan. Kallonta Mama ta yi tare da cewa.
"Jidderh Lafiya kuwa?"
Murmushi ta ƙakalo ta ce.
"Lafiya lau Mama."
Wayarta ta ciro daga cikin aljihun dogon rigarta ta nemi wani lamba ta tura sakon text message.
Ba jimawa kira ya shigo wayar. Ganin mutanen dake cikin ɗakin suna kallonta ya sa ba ta ɗaya ba. Har Larai ta ce.
"Ba kiranki ake yi ba?"
"Uhm"
Katse kiran wayar ta yi sannan ta tura text message.
Kusan sau uku ana turo mata da messages tana mai da reply kafin ta tashi da sauri kamar wacce aka tsikara ta shiga ɗakin Mom."
Sanin Mom ba ta gidan ya saka ta hau bincike a cikin ɗakin na ta. Ganin ba ta samu abun da take nema ba ya saka ta saki tsuki cikin takaici.
Har ta nufi kofar sai ta juya ta kalli wani dorowa wanda sam hankalinta bai kai gare shi ba.
Buɗewa ta yi sai ta saki murmushi lokacin da ta yi tozali da keys ɗin da ke cikin dorowar. Da sauri ta kai hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin makullan dake cikin drawar ɗin.
Saka shi ta yi cikin aljihunta sannan ta nufi ƙofar fita.
Daidai lokacin da Mom take dawowa daga unguwa. Tana sanye da mayafin take sai handbag ɗin ta daje riƙe a hannunta.
Gaban Zahrah ne ya fadi sakamakon ganin irin kallon da Mom ke yi mata.
"Me kike yi a ciki?"
"Mom na je na gyara maki ɗakin ne?"
"Ina tun safe kika gyara Mani ɗakin ko?"
"Eh na duba ko akwai abinda zan kara yi ne?"
Wani kallo Mom ta yi mata na rashin yarda kafin ta ce
"Shi kenan je ki."
Ajiyar zuciya ta sauke ta fice da sauri daga ɗakin.
Da kallo Mom ta bita zuviyarta cike da tarin tambayoyi.
Sai da ta ga ta ɓacewa wa ganinta ne ta shige cikin ɗakin tare da tura ƙofarta ta rufe.
Sulaiman take ta raba idanun nemansa amma ba ya nan. Sai dai sauran guard ɗin da wasu security.
Komawa ta yi ta nufi wata hanya. Can sai ta fito dauke da wani galam na fetur da ashana a hannunta.
Wannan karon ba ta bi hanayar da Aunty ta gan ta ba sai ta bi wata hanyar daban ta zagaya.
Sai da ta ɓulle in da take son zuwa sannan ta buɗe galan ɗin fetur ɗin ta watsa a plate ɗin da ke wajen, sannan ta watsawa a na kusa da shi. Duk ta watsa bayan ta zuge glass din window har ciki ta watsa .
Ja baya ta yi daga wajen sannan ta ƙyasta ashana ta jefa ciki.
Take wuta ya tashi