Showing 183001 words to 186000 words out of 190762 words

Chapter 62 - Farkon Ganin Idona Book Compelet By Sajida Nijar.txt

21 Apr 2026

4019

da nata hadi da lumshe idannuwansa ya shiga kisssing din leben pasionatly ............., clmly, swly, a hankali ya cire leben nasa idannuwansa a kashe sosai ya tura hannunsa cikin rigarta yayi sama da shi a hankali har kan dan kululun abin kirjinta ya dora yar yatsarsa ya shiga zagayawa a hankali a hankali a hankali , wanda hakan ya saka ta ɗan lumshe idannuwanta kirjinta na amsawa , jikinta na daukan salon takunsa....yannayinta na amsar sakonsa, ta bude raunanun idannuwanta tana kallon lumsasun idannuwansa wa'inda take jinsu kamar zasu ja ta su hadiyeta a cikin su......, a hankali ta sauke ajiyar zuciya a lokacin da ya furta" Ina so ki so Ni"

"Anmy.....ina da bukatar ki so Ni..... plz"

Da sauri ta kai hannunta ta rike gefen fuskarsa lebenta na dan rawa........a hankali ta furta " I love You......i really lv U johan"

Idannuwansa ya lumshe kafin ya sakar mata murmushi a nutse ya kai lebensa wajen wuyanta ya ringa sinsinawa yana lasa....a hankali a hankali har ya kai wajen kirjinta.......

Gaba daya a wata duniya take mai wuyar fasara, mararta kuwa har wani dumi ta dauka mai kyan gaske, saima da ta tsinci lebunansa a balagagen kirjinta ta idasa yarda cewa kadararta mai kyau ce......, lokaci daya ta ringa kai hannaye tana gabatar da aikin da babu wanda ya koya mata haka ta tsinci kanta a ciki, a hankali a hankali ta ringa karbar lamarin nan har ya zamo an zo baban fagen da har yanzu bata idasa gogewa da sabawa ba, Allah ma ya taimake ta abokin tafiyar ya gama gane cewa motar tasa nada bukatar lalabawa kafin a darza da gudu, sai kawai yake bi a hankali har sai ta gama yarda cewar ba za'a haki rijiyar da karfi ba sannan ta saki jiki an gama sabawa sannan ake haka , a lokacin kuwa ita da kanta burinta ta ga ta birge maza sai kawai ta jure ta cize da bada kai bori yayi ta ci gaba da hawa.

Asuba ta gari matar baban kurma.




Washe gari da wuri ta gama duk wani abinda ata ɗorawa kanta na hidimar gida, cike da farin ciki da tarin zumudin irin alkhairan da mijinta ya baibayeta da shi da sanyin safiyar nan ta hanyar mallaka mata wasu manyan plazas dinsa guda biyu dake jere na harkar kayan daki da kuma kayan kicin....., ga ganleliyar mota, ga zabi da ya bata a kan lamarin makaranta, shi yace da so samu ne ta bashi dama su je su dawo Sai ya je da kansa a kan karatunta Ama ta yiwa su aba shawara, wannan lamari shi ya sake bata wata irin kwarin gwuiwar gama girkinta, ta dauki na mama Khadeeja ta kai da kanta, ta samu Aunty shareefat ta shirya direba take jira ya Kaita , nan ta ji cewar tare zasu je idan suka yi mata rakiya sai a Kaita gida saboda ta jiyo shawarar da su Aba zasu yanke a kan batun tafiyarsu da ake cikin shirinta wace mama Khadeeja zasu fara saukewa a likitar da za'a rike ta na dan lokaci sannan su wuce shi da ita mosku, wannan dalilin ya sa ta wuce ɓangaren Hajiya Inna ta bata abincinta, ta bata maganinta sannan ta saka man zafin da take yi mata massage da shi ta yi mata na adadin minti talatin cike da kula da kiyaye dokokin aikinta sannan ta musu salama ta koma ta ɗora abayarta a saman suturarta ta je ta gaisar da baba Hamza sannan ta kama hannun kurma da aka shirya sunna tafe sunna fira da su khalisat wa'inda gaba daya zasu tafi rakiyar Aunty Shareefat din


Aéroport suka nufa , a cen suka samu AL'WALED da abokinsa sunna fira, cikin mutuntawa suka gaisa ya karra gaisar da Khadeeja da mutuntawa harda yar tsokanar da bata wuce misali ba sannan suka yiwa Aunty rakiya har wajen da ake dakatawa idan banda kai za'a yi tafiya ta rungume su daya bayan daya sunna yin salama, da kula sosai ta ce" Daughter, a yi ta hakuri, Allah ya baku zaman lafiya, sannan ki yi kokari ki kiyaye lafiyarki fa, dan kuwa Ni zan zamo kishiyar da bata da kishin kishiyarta ko kuwa Amaryar dake zumudin jiran ango, Allah ya baki lafiya"

Khadeeja ta sada kai cike da jin kunya, su khalisat kuwa banda zarro ido babu abinda suke yi, AL'WALED kuwa yayi murmushi suka gaisa da Aunty SHAREEFA a tausashe ya furta" Safe flt mam "

Aunty SHAREEFA ta yi masa murmushi ta furta" In sha Allah, tk cr big son, sai mun hade a whatsup"

Daga haka suka yi hanyar da zasu shiga jirgi ita da yarinyar ta, su kuwa suka juya wajen motocinsu

Sai da ya rufe bangaren da ta shiga ya dan ja baya yana kallo suka tafi sannan ya juya ya nufi tasa motar suka daga shi da abokinsa saboda abinda zasu je su yi da ya shafi kasuwanci


Kusan karfe tara tuni sun iso gidan Aba, a lokacin Aba na falo tare da su Mama da su Karima ana ta maganar harkar kayan daki ya sa sun zauna dole dan ya nunawa gimbiya shi mai adalci ne, sunna iya zabar kalar kayan da suke so ma, dan ya fada mata baba Hamza yace shi zai yi gara ta ringa faman fadin ko yayi shima sai ya musu irin yadda ya yiwa Anmy, kiri kiri ana son nunawa kamar baida adalci

Jin irin kirarin da mai aiki ke yiwa Khadeeja tana faman yi da marabartarta ya saka shi zabura, har zai mike ya koma yana dafe kirji ya furta" Na shiga uku, gimbiya idona zai rufe, bana gani da kyau, bana ji da kyau innalilahi wa akace a gidan nan da sanyin safiyar nan? Gimbiya masu kuɗi fa barcin safe suke yi uban me ya tado anmy daga gadonta warhaka? Gimbiya uban me anmy ta zo nema gidan nan da safiyar Allah? Iyi? Ina mijin nata? Kar dai yar nan Ni zata sakawa hawan jinni ta kashe auren nan? Innalilahi wa Inna ilaihi raj'une"

Sai kuma yayi wufff ya mike ya tsallake Lubna ta hanyar dirawa ya leko Khadeeja dake kwasar kariyar kurma da mai aiki a dole sai sun yi magana, yan matan baba Hamza kuwa sunna mota sunna tsegumi kafin su shigo yau sai duniya ta ji sunna jiran jika kwana kusa, shi yasa basu shigo ba

Wuf yayi ya janyo abayar Tata ta baya ya janyota ciki yana zarro ido yace" Anmy ki yiwa Allah ki ce min ba ke bace? Ke dan ubanki me ya kawo ki gidan nan da safiyar Allah???"

A guje ta yi wajen su lubna tana zarro ido ta ce" Kai, me kuka yi za'a hada da Ni? Wallahi Ni yanzu na zo Aba babu abinda na aikata a gidan nan"

Mama takaici ya sakata tafka tagumi tana kallon su

Aba ya ce" Na sani, zuwan naki nake son jin dalili, inace jiyan nan kuka bar gidan nan? Warhaka ai Elhaji karami bai motsa Bama bale ya sauko , shine ke shashasha zaki sauko? Ba'a koya maki sai ya sauko zaki sauko ba???"

Da sauri ta ce" Wallahi Aba ya sauko, daga aéroport fa muke, mama Shareefat muka raka shine yace a kawo Ni a ji shawarar da zaka yanke a kan maganar karatuna, wai zamu yi tafiya yana so ace sai mun dawo zan ci gaba da zuwa makaranta Ama idan ka amince in kace a'a sai in ci gaba da tafiya shi ya je ya dawo , kuma Aba plazasss dinsa biyu na harkar saide saiden kayan daki da na kicin ma wai ya bani gama takardun da komai"

Aba ya zarro ido yana kallon ta sai kuma ya kalli mama lokaci daya yana sakin murmushi hadi da dariya ya karaso inda suke zaune su duka ya'yan a kassss ya zauna hakan ya sa du suka zarro ido

Ya talabe haba sai kuma ya dago ya sake kallon Mama da ta zarro idon itama yayi yar dariya ya ce" Ikon Allah, ashe dai da ake cewa ya'yan nan watarana kawayena ne haka ne?"

Mama ta Dube shi da kyau ta ce" Kawayenka kuma?"

Aba ya ce" Eh mana, kin ga fa da na zauna din nan sai na ga du shawararmu daya da su, Allah mai iko"

Sai kuma ya kalli Anmy ya ce" Uwata, kika ce mema? Wai tafka tafkan shagunan nan na bakin baban titi masu walwalwal tagwaye su biyu su ko wadine?"

Khadeeja ta ciro takardun da litafinsu ta mikawa Aba

Aba ya mikawa mama ya ce" Karanta min da kyau, bana son bata koda ta digo ce"

Mama ta bude ta duba, gayanan hatta sunanta da komai, ga dukkan alamu an gama komai kawai bata aka yi, ta karanta masa din kuwa yana kallon takardar kamar shima karantarwar ya iya

Sai kuma ya talabe haba kafin ya ja hanci ya ce" Innalilahi kai innalilahi, gimbiya kina tune da marigayiya tace a cikin ya'yan nan da nake gani in rungume su du dukiyata ana iya samun wanda ya dame Ni? Kin ga zancen manya ya fito.... Allah jikan marigayiya yau ga abin cikin kwan ya fi kwan dadi? Wallahi na haifo atajira, y'ar nan zata fi mai nema ba dare ba rana, yanzu Hajiya uwata wannan din naki ne???"


Mama da tarin gannin ikon Allah ta ce" Haba Aban su "

Aba ya kalle ta ya ce" To yan sa ido meye"

Mama ta ce" Ba fa ita kadai bace, dan Allah ka tashi ka hau kujera kuma ka saka albarka ya wadatar"

Aba ya dubeta da kyau kafin ya ce" Ke kam harda bakin ciki inaga a lamarinki yau ga balaki, ke gwara in maido abokiyar zamanki ta ringa tayani murna, wai menenene Ni ake son wulakantani ? Kin kuwa san me shagunan nan ke nufi? Ko dan mijin Anmy ya fi mijinki kudi zaki mana ba daidai ba? Kai a dai cenza hali wallahi...."

Sai kuma ya dubi Khadeeja da mamaki ke son kashe ta ya ce" Uwata......."

Daga ita har su lubna suka kalli junna, wannan shine sabon salo La'ila ha ilalahu

Aba ya wani tausasa murya ya ce" In ce kin karya kafin ki fito?"

Khadeeja ta daga kai da sauri

Aba ya mike ya zauna yana wani girgiza kaffafuwa sai kuma ya daki murmushi ya ce" To in ba abin uwata ba , ina ke ina wani karatu na bata lokaci da mana talauci? Saboda karatun boko fa har hauka ake yi, ke dai ai kin iya allura kin iya abubuwa da yawa, kya yiwa mijinki da yayanku, ki wuce ki bi mijinki ku sha yawon ku mu kuwa sai mu tsare shagunan, to ai karatu na talaka ne gaskiya , kuma matar talaka ke aiki!"

Da takaici mama ta ce" Elhaji Ni kake yiwa habaici?"

aba ya dubeta sai kuma ya dafe haba ya ce" Allah ya baki hakuri, Ni kam du bana wani son rigima wallahi"

Mama ta dubi Khadeeja da kyau ta ce" Anmy, Allah ya saka da alkhairi ya karra budi, Ama kin ga karatu kam sai kin yi shi yarinya , da yake a cikin hutu Yan section dinki suke kina iya sanar masa sati Uku gareki na hutu, a yi abinda za'a yi a gama a sati ukun idan Allah ya aminta a ci gaba da karatun, saboda shi karatu ai yana da anfani, ilimi ne, koda ba zaki yi aikin gwamnati ba kya iya jagorantar asibitinki idan kina da rabo, daga ke har yan uwanki babu wace zan yarda a dakatar da karatunta , kun dai ji na fada muku karma wani abu ya shiga kanku , du kudin y'a sai ta yi karatun talaka!"

Aba ya dubi Mama a zabure ya ce" Gimbiya da Ni kike?"

Mama ta dauke kai tana turo baki

Aba ya mike yana kokarin rage murya saboda su khalisat da suka nufo ya ce" Baki isa ba, ai ni ba dan boko bane, Ni dan a bi dokokin addini ne, ban yarda da bokon banza bokon wofi ba, ai idan mijinta yace ya haramta bokon an gama magana ko? To zan same shi ya Hanna in ga tsiya, aikin banza, bani ki takardun mu "
Ya warce takardun ya bi ta dogon layin corridor yana bude takardun yana kallo kamar wanda ya iya karantawa

Gaba dayansu bayansa suka bi da kallo har ya bacewa ganninsu kafin su juyo su kalli junna, lubna ta fashe da dariya tana rike ciki ta ce" Cabdijan, uwata ya hanya"

Anmy ta kai mata duka tana kwabe fuska, Mama kuwa ta saki murmushi ta ce" Kai, mijin nawa kuke kwaikwayo???"

Gaba dayansu suka saka dariya har maman saboda wallahi sai yanzu abin ya tukota da dariya, kai mutumen nan ko? Mutumen nan tashin hankali ne, Allah ya kyauta masa, Ama lamarinsa ko? Sai addu'a, nan mama ta Dube su da kula ta ce" Ina fatan kin yi godiyar wannan kyauta?"

Khadeeja ta gyada kai tana dan sada kai alamun jin kunya

Mama ta ce" Allah ya anfana, Allah ya sanya albarka, ya buda maku baki daya....."
Ta ɗan dakata ta ɗora da fadin" In ba abinsa ba, ai yanzu shi yake da iko da hukuncin da ya dace ya yanke da rayuwar ki,.... koda yake hakan da yayi ya saka na ji nutsuwa sosai a zuciyata, ya tabbatar min ko muna nan ko Bama nan zai kula da iliminki da tarbiyyar ki, Allah ya da kuma mazanku su nuna min wannan adalcin, Allah ya da su yi tsaye a kan lamarin ilimin ku da tarbiyar ku, dan zan so ace gaba kuka kara ci daga hannuna "

Murmushi kawai suke yi, ita ke yin addu'ar tana amsawa saboda nauyin da maganar ta yi musu, sannan ta mike tana nufar waje tana fadin" Bari dai in gano wannan kishiyar da zulai ta rike min a waje, litle zo mana....."

Daga haka ta bar su sunna ta fira da dan iface ifacensu har sauran yan matan suka shigo aka hadu da su ana ta fira, daga nan ma suka shirya suka wuce gidan hajiyar larabawa bayan ta yi masa texte ya bata izinin tafiyar, su dinma du sun samu izinin hakan tun da safe saboda tun a jiya kowace ta samu dankareriyar waya daga Aba.


....................................................


Bayan kwana biyu suka daga zuwa kasa mai tsarki, su uku ne kawai suka yi tafiyar , a nan ne suka bar mama a baban asibitin lafiya karkashin kulawar Docter Nawell, saboda a asibitin ba'a yarda da yan jinya, kuma adadin lokacin da suka dauka zasu kula da ita sati biyu ne, bayan sati biyun zasu ga idan zasu karra wani lokacin ko zasu salameta daga haka, daga nan su kuwa suka shiga yawace yawacensu kasashen waje dan shakatawa da yayada manufa ta sati biyu kacal saboda tuni sun cinye sati dayan a Saudiya


Sati biyun nan sun yi shi cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, sati biyun da ya sa suka sake shakuwa da junna fiye da tunani, domin ko waya zata yi da gida ta whatsup da lokacin da take yi, haka idan suka yi kiran gida suka yi fira da baba Hamza da su Hajiya , sannan ta tatauna da likitar da ta kawo da kanta wace ke kula da lafiyar Hajiya kafin ta dawo shima da lokacin da suke yin call din nan sunna gamawa suke kashe wayoyin su koma ibada mai zaman kanta mai daraja wace ta ringa saukar mata da zazzaɓi kala kala da sirfa iri iri wace ke karra tabbatar masa da zancen mama shareefat harma ya ji hankalinsa ya sake kwonciya cike da zumudin irgen kwanaki a zuciyarsa tare da Binta da addu'ar samun lafiya

A lokacin da wa'adin lokacin da suka diba ya cika na lafiyar mama Khadeeja Hajiya zainab ce ta zo ta dauketa suka juya saboda shi ogan basu gama nasu hutun ba, sai waya da yayi da likitar ta tabbatar masa cewa alhamdulilah jiki da sauki, a hankali a hankali ana iya samun abinda ake so, dumumuwan nan babu yanzu, idan aka ci gaba da kiyaye dukkan abinda akace in sha Allah zata samu sauki sosai, magungunanta na tsayin wata uku ne, tana gama shanyewa a dawo da ita su karra dubata su gani.... Hankalinsa ya karra kwonci a lokacin da suke yin waya da ita ya zamo bata ringa rigimar ya zo ya zo ba kamar yadda take yi da farko farkon baro ta da yayi ba.


Cikin ikon Allah duka gama hutunsu suka juyo gida, a nan kuma anmy ta shiga cikin lamarin laulayi sosai da sosai wanda a dole aka bata hutu a makarantar saboda ita kam tana da laulayi har sai da kowa ya ringa tausaya mata , hatta yan uwanta da suke gidajensu bini bini sun lekota, Lubna ce kawai dake wani garin sai dai su yi VIDIO callll


A cikin wannan tsannin na watanni hudu kafin cikinta yayi kwari ta ga soyaya da kula daga wajen AL'WALED da danginsa baki daya dukkan lalurar laulayinta sunna tare da ita sunna nan nan da ita....., a kullum Aba zai miko mata kosai da koko da take sha harda rubutun addu'a na samun lafiya, baba Hamza kuwa zai shigo mata da guzurin aya ne, da sauransu harda goro na tashin zuciya ......, mijinta kuwa hannayensa a bude suke har ya zamo ta rasa bakin magana sai dai kawai ta rungume shi a jikinta ta yi ta sauke ajiyar zuciya, Uwa uba kakaninsa da iyayensa kanana a zo kan mama Khadeeja wace bini bini zata leko ta ga jikin KHADEEJA saboda halin galabaita da take ciki ya Hanna mata zuwa ta leko su sai in ta gaji da dakunan ta ɗora masa rigimar ita zata je ne sannan yake yarda ta lalaba su je ita da kurma wajen Hajiya Inna su zauna su yi mata fira daga nan su leka sauran da kuma mama Khadeeja, har yayi kwari ta fara samun ƙarfi, inda shekarar karatunta ya zamo sai dai wata shekarar ta sake saboda wata hudu cirrr ta yi ba a aji ba, karatun likita kuwa ya fi karfin ka tsallake ranaku ka ce zaka ci gaba da ganewa........





Kwonci tashi kayan Allah


Kwonci tashi mai cinye kwanaki....., an wayi gari Mama ta sauka lafiya a asibiti , ta samu baby boy dinta, wanda suka yi tafiyar su asibiti asirinsu rufe ita da kanwarta ta haihu suka kunso abinsu suka dawo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login