Showing 213001 words to 216000 words out of 219669 words

Chapter 72 - So Makamin Cuta Complete Hausa Novels Compelet By Surayyams.txt

14 Mar 2026

4110

zai tsine miki bazaki taba shiga inuwar yafiyar ubangiji ba ta cigaba da kuka

Abun ya ma mrs hidayat zafi kam amma sai ta danne tace zahida pls stop blaming me,ki tuna kinada Lokaci har yanzu zaki iya daukar fansan ki akan sa Tunda baisan kin san shi waye bane yanzu

Zahida sai ta mike tsaye a zafafe tace kikace mene?
Na dauki wani fansa akan sa?ke asuwa? Wai a matsayin shawara ko me kike fada min?kin cuce ni hidayat, kin koya min munannan hali ,kin shayar dani mugunta Da da kyamAr mutane, mutane nawa na kashe a rayuwa ta nawa kika sa na tozarta?
And yet ke ce kika kashe min uwa da uba ,ke kika sa ni muka salwantar da rayuwan lateef da lailah..

and now look at me
Ki duba iirin rayuwar da kika jefa ni aciki,
Kinsa nayi soyyaya da wanda nafi tsana a duniya, monster da kika haifa acikin ki ,kanin kanin baya na kinsa na so shi na mutu masa,
nayi masa biyayya ya wulakanta ni na tayyara rayuwata akansa kinsa ya wulakantamin zuciya hidayat i was truly in love with ash ko baki sani bane..
Sai ta durkusa kasa ta cigaba tana kuka muryqn ta na rawa tace

Ya zalunce ni kinsa na dandana zafin soyyayr da bata da riba har abada kin jefa ni A kazama kuma kaskantacciyar rayuwa.
Kin sa Tun tuni yana kallo na a matsayin wawiya mahaukaciya. duk ke kika jawo min"
Ke ce ke ce kika fara komai kece.. tayi nuni da ita da bindigan a zuciye tana kuka tana karkarwa



Mrs hidayat sa da ta riga ta firgita ta karaya gaba daya da yanayin zahidan amma ganin a lokacin zuciyan zahida yayi weak sai tace just shut up and mind ur words ki dena gaya min haka zahida ke ya ta ce, kuma duk abunda nayi nayi ne don na kare ki,

Wato Har Kin manta lokacin da kike kuka baki so kije prizon na tura dana lateef at young age don nayi saving din ki ko?

kafin nan ma sau nawa ena ceto rayuwar ki daga fada wa kasa don naka sa miki wannan ? Wani irin hali ne ban shiga ba don na daga rayuwar ki ta yi kyau a duniya

Naji nayi miki rashin adalci akan mahaifiyar ki
Amma ni sadaukrwa nawa na miki a rayuwa zahida?
Yayan ciki na ne fa ance miki ban ji zafin kashe min yata da kikayi bane? Ko sadaukar da rayuwar lateef danayi akan ki ba komai bane.

Zahida ta cigaba da kuka a kasa batace uffan ba
Duk jabeer na labe najin su,

Mrs hidayat tace,look i know we hurt each otther Alots,amma toh ki sani don nace ki dauki fansa akan ashween ena nema miki sauki ne
don nasan nikam bazaii taba yafe min ba im har kema kina so ki zauna lpya a rayuwar ki ki kashe sa ki huta in munje lahira sai ayi mana sharia,.

Cikin kukan zahida da ta fashe da wani irin mahaukacin dariya mai dauke da kunci da bakin dacin rai... tace a duk inda yake yanzu nasan yana neman matar sa don kuwa tana hannu na na daure ta a gidan gonan sa gadon sa daya sa na tono asirin ki da shi..
ta sake fashewa da dariya tace ma mrs hidayat
Na gode da shawarar ki my dear wicked mom.

Amma ki sani lateef dinki yau ne zai yi asalin tafiya lahira ya sami lailan sa achan don kuwa in yazo sai na kashe shi.

Ke kuma ki saurare abunda zan miki don bazan barki ba .

Bana kaunar ki bana kaunar ki sake numfashi mai dadi a duniya prizon anan zaki wulakanta sannan ki mutu kaskantacciya.

Nan jabeer ya sullube ya bar gidan a hujajan ya nufo hanya a guje yana danna kira ma ashweenn

Shikuma Lokacin wayar sa na mota yana tare da jamal wanda tuni yazo wajen da aka sanar da shi halin da suke ciki da kamal

Sai shi ash yayi zaman jira kamal ya farafado tare da salma shi kuma jamal ya bi police aka shiga neman jasmine..

Ita kanta salma tasan hankalin sa a tashe yake matuka amma sam ya kasa nuna mata ya nace sai ya jira yaga abokin sa ya tashi kafin ya je neman matar sa dakan sa.

Jamal kuma ana chan ana zaga gari ana bincike da shi ko za'aji labarin jasmine

Da shike lokacin rana yayi an fara hada hadan dauko yara daga makarantu sai Mummunan Traffic ya rike jabirr a hanya
Gashi baisan da zuwan jamal ba bare ya kira shi ga wayar ashween na ringing a mota amma sam ba ayi picking ba

sam sai basira ta dauke masa ya kira jummai wacce take tare da su tuntuni
Don Yagama shiga qani yanayi hankalin sa yayi mummanan tashi.

Zahida ta daga bindiga kan mrs rod ta nuna ta dashi tace kar kiji komai zan tura details din kisan saminu da kika zo kikayi
Confessing da bakin ki a office dina
yanzu ma yan sanda zasu zo su kaiki gidan ki na gaskiya.ta fashe da dariya abun tam


Mrs hidayat ta rusuna kasa ta sake wani irin Kara ta dauka ko zahida zata fahimci abun su juya kan Ashween tare amma sai taga daban ne yanzu

Ko ajikin zahida cikin sauri sauri ta juyabta shiga mota ta bar arean gidan baki daya

A cikin motar ma kamar mahaukaciya take sai ta shiga tura sakon voice note emergency direct ofishin SSpolice..
daga nan ta kashe wayar ta gaba daya ta nifi inda jasmine take.

Shirin ta tsaf tayi cikin bakaken kaya ta daure kanta da bakin dankwali yau kam babu kwalliya don revenge ne zallah a zuciyan ta,

Jasmine ta wahala ga yunwa ga tsamin da hannun ta yake mata ga bakin duhu
Tayi kukan har ta gaji tayi shiru

Cikin haka ne zahida ta zo ta bude ta ta kwance mata baki,
Nan jasmine sai da ta sake wani numfashin wahala tare da hawaye

Wani murmushin takaici zahida tayi tana binta da kallo sai ta dauko ruwa mai sanyi ta bata ta sha
Tace yau zaki ji abunda nake ji jasmine.

Yau zaki ji zafin dafin soyayyar da Mijin ki kuma kani na ya dan dana ma zuciya ta
Ba ya dauki SO MAKAMIN CUTA ba?

Ya cuna ma zuciyata wutar soyayyan da har na mutu bazan mallaka se ba.?

Yau sai na sake kashe masa soyayyya a rayuwar sa kamar yadda na masa tun da chan akan wata banzar yar uwan sa da yake ikirarin ita ta fara son shi a duniya.

Cikin kuka jasmine tace kiyi hakuri dan Allah,
Wallhy yaya ba hakan yake nufi dake ba dan Allah ki nemi gafarar sa ku sasanta junan ku nasan zai yafe miki
Pls dont hurt him kiyi hakuri.

Zahida ta mayar mata da dan karamin murmushi tace jasmine kenan na san kina son shi sosai nima haka.
Ke In har zaki iya zama dani a matsayin gf dinsa a gidan sa kina gani yana ce miki ke cousin din sa a gaba na kuma kika zauna dashi hakan kiyi tunani
Wani irin sace zuciya kike ganin ashween bai iya ba?

He fooled me,ke ai yarinya ce ba a wasa da feelings so bazai taba zamowa makamin cuta ba jasmine,

can you believe dat har yanzu enajin ena son shi a raina?wannan natural ne saboda feelings ne...
wani irin wulaknci yayi ma zuciya ta duk akan na kashe masa soyayyar sa na farko a duniya?

Jasmine ta dago ta kalle ta kalar tausayi tace,kinyi gaskiya yayi kuskure aunty,a duniya kar ka taba dawowa da so makamin cuta wanda ya so sai ka so shi da gaskiya.

amma ki sani ke fa babba ce ke ce agaba da shi dan Allah ku sasan ta kanku, you can still make it..pls pls dont hurt him na roke ki dan Allah kiyiii min rai kar ki kashe min shi shika dai nake da shi a duniya kiyi hakuri.

Zahida tayi shiru tana saka wani abun aranta don harga Allah ta so ta kyale jasmine ta fuskan ce shi
Amma ena Tayi tayi ta dena jin diigon zafin abun aranta amma ta kasa
ji take kamar komai karya ne har yanzu ashween nata ne ita kadai.

Ji take in ma ta bar komai ya wuce ta rusuna don a shirya ta sani sarai
Ba zata iya cire shi arai ba soyayyar sa tamkar ubangiji ne ya dasa mata ita kanta bata iya control

Gashi duk da abunda yayi har ila yau a zuciyan ta ba abunda ya sauya na son shi
tasan kuma soyayyar su zallan cutarwa ne har abada shiyasa take ganin ba wani mafita sai dai wannan din da ta zaba a ranta

Kawai sai ta tashi ta cigaba da zuqan cocaine dinta saboda ta cire sauran imanin dake damun zuciyar ta akan maganar da sukayi da jasmine din yanzu..


Anan ma ta bugu ta bugu ta cire makanta hankali sosai sai ta shiga ta fito da hot acid da tayi niyyar zata watsa ma jasmine din tun da chan.

Sannan ta sa a ranta sai tayi hakan kafin ta kira ash tace ya zo ya gani da idon sa da ganan sai ta kashe sa ta huta.





*hmmm SO MAKAMIN CUTA ,So mugun wasa๐Ÿ˜‚*

*Leeme hear your views please๐Ÿ‘‚๐Ÿป๐Ÿ‘‚๐Ÿป๐Ÿ‘‚๐Ÿป๐Ÿ‘‚๐Ÿป๐Ÿ‘‚๐Ÿป๐Ÿ‘‚๐Ÿป*







*surriem*
[23/08, 05:43] โ€ช+234 806 071 2446โ€ฌ: *โšœBRILLIANT WRITERS ASSO๐Ÿ–Š*



๐Ÿ’”

*SO MAKAMIN CUTA*
_'the sword of evil love'_


_Story and written by_
*SURAYYAHMS*๐Ÿ”ฅ



*DEDICATED TO-*@UMMERHERNY NERSALLAH.



*ENA MIKA GODIYA TA NA MEMBERS Na SURAYYAHMS fans page musamman enda aka shirin musan juna jiya your beautifl words of prayers, love and encouragement is what keeps me blowing Allah ya sada ku da farin ciki da kwanciyar hankali All members of my fans groups 2.3 ena kaunar ku sosai nagode.*


*Sadaukarwa na musamman ga๐Ÿ‘‡๐Ÿฟ*

*Maman khayr tawaje na my admin*
*Saffah one*
*mom khadija ena mika sako ma dan baba*
*Haulat bawa Allah ya dawo dake lapya ya bada ladan aikin hajj*
*ummu farhan na cikin asmaluv fans*
*Maimunat muhammad na sureehrny fans*
*fatima tijjani*
*Hurul aynn my admin*
*Real maryam noble*
*Da rukayyaht BB*
*And lastly my*
*Meenah luv meenaauwal marubuciyar sanyin idaniya ke da members din ki*





*Pageโ–ถ91*




Mamy bata bude ido ba sai a gadon asibiti anan ma da wani irin kuka ta tashi
Yar uwan Abban Ashraf dake gefe itace kawai ke faman danne mamy tana cewa kiyi hakuri insha Allah komai zai zo da sauki ashraf bazai mutu ba.

Mamy tace na shiga uku,wannan bala'i da me yayi kama? zaynab na dade ena gaya masa ya gyara halayen sa musamman akan biye biyen matan nan amma sam ashraf yaki ji na
Yau ba ga irin ta ba,yaje garin neman ido gashi an rasa gira?

Ga mata nan na sha kawowa ya zaba acikin su amma ya ki
Sai ya zabi wannan rayuwa gashi tana neman raba shi da duniya baki daya,yanzun ya yake ciki?

Gaskiya ena so naje na duba sa sunce min an sashi a emergency plane an dawo da shi kasar nan

Zaynab tace eh, kiyi hakuri ki kwantar da hankalin ki ,ai case din ma da yar gidan wani senator ne shiyasa ma iyayen ta suka kashe maganan tun akasan waje aka dawo da komai nan gida don ance yarinyar ta masa raunuka munana ajikin sa.

Dole muma muyi hakuri mu karbi wannan kaddara don Bamusan gaskiyan labarin ta ba
Ta dai ce ma media yaje raping dinta ne shiyasa ta cahhaka masa wuka ta kuma sokale masa kwayar ido da shi don ta samu ta kubutar da kanta daga hannun sa

Mamy ta dada sunkuyar da kanta ta cigaba da kuka

Yau ana neman kusan sati biyu kenan ga media sunyi rububin labarin cewa famous dan kwalisan nan Ashraf musaddik yayi atempting raping din mace har ta cire masa ido daya.

Yawancin yan matan da ya tayyara rayuwan su su suka dada azzala abun a shafukan su na media
Su Suka dada bada shaidan ashraf zaiyi abunda yafi haka

A hakan nan mamy ta kasa samun nitsuwa tsaban bakin ciki, jasmine ce ta kasance kullum tare da ita tana sanyaya mata rai

Shi kuma ashween yana tsaye akan case din ashraf ana nema masa saukin jikin sa
gaba daya ashraf sai ya dawo shiru shiru baisan yin magana tsaban takaici,wayar sa ma ya kasa budewa sabida sakonnin mutane wanda mafi yawancin su na gwale ne.


A haka asibiti Sai kusan bayan sati biyu aka soma yunkurin sallamar sa lokacin akayi sa'a wutar fitanan yana neman ragowa kadan kadan.

Duk hankalin sa bai jikin sa musamman da ya lura cewa albarkacin roko da magiyan da ashween yake yi yasa abban sa yake kula da shi

Doc ya tabbatar musu da cewa aahraf ya rasa karfin ido daya dole sai dai yayi amfani da ido daya

Ga raunaukan da yar senator ta ji masa 'a kullum in ya tuno yadda yarinyar ta masa sai yaji ya tsani kansa.

Musamman daya tabbata karya take yi bai ce zaiyi raping din ta drugs kawai ta debo ta tsula masa rashin mutunci amma sai gashi
Ta juya magaman a media,girman shi da mutuncin shi gaban iyayen sa da mutane ya girgiza..

Yace hmmm duniya budurwan wawa yanzu ni ribar me naci?
Ni ban aikata ba amma ya shafe ni gashi narasa komai har da kyaun halittar da nake rigima da shi.

Sosai abubuwan ke damun sa, ga mamy bata ko amsa gaisuwan sa
A takaice Ashween ne kadai ke sake masa fuska yana tare da shi

Amma kuma yana mugun jin kunyar sa
Ta ena zan fara ? Tambayar kenan da ke hanasa tabuka komai gaban Ash don shi kansa ya san gaban da yake yi da Ash tun suna kanana ne.

Shikuwa ash ba ruwan sa tausayin sa ma kawai yake ji
Shiyasa ma yake nace masu mamy suna kula dashi kar ya shiga wani hali duk da fushi suke yi har yanzu

Haka rayuwa ta cigaba ma ashraf ba aikin yi gaba daya abba ya kwace ya rike abun sa

Sai ya zamo in ya zauna ba abunda yake tunawa sai kazamar rayuwan sa
Ga ido dayan nan shi yake asalin damun sa gani yake ba wacce zata aure shi a hakan kullum sai yayi kuka yana neman mafita wajen uban giji .

Da kyar ya soma samun sauki ya rusuna sosaii wajen neman yafiyar iyayen sa.

Kafin wata daya ya sake zagowa har ya dan sake ya soma fita sai dai yawon ba ya wuce gidan su jasmine anan ma Ash ne kawai yake kula sa.


Jabeer shi yayi sanadiyar zaman su jazmine na dan lokaci a abuja akan Ash zai taimake sa ya tada plantation din daya bar musu kyauta.

Anan su kanje asibiti a duba lpyar cikin jasmine sai dai kullun akaje sai ta turje masa akan lallai aje aduba zahida..

Duk da yanzu kam ta bude ido amma sam bata san ena take ba.
Gashi jamal da jabir sun gama shirye shirye akan za'a akaita chan babylon a cikin kasar iraq ayi mata special body surgery
Wata kila hala ayi dace ta dawo asalin siffar mutum

A asibitin nan duk sunyi signing din files dinta amma
Ashween ko ajikin sa hakan ya matukar damun jasmine

Ranar din ma da kuka aka koma gida yana driving baice komai ba don abun na mugun bata masa rai yadda take neman daga masa hankali akan zahida

Shi baisan meyasa jasmine ta damu da zahida ba shikuma gani yake zaman ta achan yafi tunda bazata taba barin komai ya wuce ba.

Ga ba daya ranar haka taki kula shi, ko magana bata son amsa masa
tun yana kau da kai har ya sauko ya fara yar lallabi amma sai abunda ma ya karu.

Chan dare Tana kwance a kan bed da katon cikin ta a gefen sa ' yayi lumui yana kallon ta
Sai chan yace, jasmine ki fada min ya kike so nayi miki ? Ni kenan bazan yi abunda zai kawo min kwanciyar hankali a rayuwa ta ba
Nan ma ta shiga matso ido tace yaya ba haka bane
Ni dai nafiso ace kana kula da ita kaima ai yar uwar ka ce,
Ka duba fa kaga yaya jamal da yay jabir thy are doing alots kaifa? In don nine wallhy na yafe maka
Kasan ba wanda ya isa ya kare ni sai Allah,.. ko da yau ta warke bata shiryu ba in Allah bai qaddara zata min wani abu ba bazata yi ba

Yayi shiru abunsa bai kula ba ta cigaba da jero masa bayani har dai ya hakura yace ,to shikenan in aka kammala surgrey zasu je su ganta tare

Duk da ma jasmine ta dan ji dadi amma ta so ace yanzu ne yaje don surgery zai iya daukar wani 4-5month kafin ta tashi gar gar kamar kowa.

Amma da shike tasan halin ogan nata sai ta amince kawai magana da ya kare tunda yace zai je.

Wata uku aka dauka ana ma zahida komai da komai har ansa ta a layin observation ana so aga wani irin kalar depigmentation jikin ta zai sake bayar wa

Ko ena bandages ne a lullube a jikin nata amma tana magana warau da muryan ta, tana kuma cin abinci sama sama

Sannnan ana koya mata yadda zatayi amfani da wasu gabobin jikin nata da yadda zata na motsawa

Zahida Yadda take jin ta garau ta ciki gani take tamkar in aka bude bandages din nan zata dawo normal kamannin ta.

Ana saura wata na karshe lokacin ashween
Yayi rakiyar jasmine makaranta don da kyar take motsawa ciki na watan shi na takwas.

Haka yayi jigila da ita ta kammala classes dinta sannan ta sa shi agaba sukazo babylon city don ganin zahida kamar yadda yayi alkawari

Already jamal da jabir sun iso kowa ya taru a asibiti tana zaune akan gado za'ayi unveiling bandages din agaa sabon kaman da zahida ta koma

Kowa na tsaye aciki yana jiran agama banda jasmine data manne masa ta rike hannun sa dam tana lafewa jikin sa don tasan sa sarai aiki kadan ne wajen sa ya zame ya bar musu wajen

Jamal ne ke dan amsa maganan zahidam kadan kadan ga dai muryan ta real kowa naji

Ana kaiwa karshe kowa yayi shiruuuuu awajen ganin yadda gaba daya ta dawo ba ita ba ce.

Wani halitta ce daban ,bakar fata mai madaidaicin hanci da baki sannan da kananan idanu

Ba yabo ba fallasa ba za ace mummuniya bace amma ko kadan baza a jera ta a layin kyawawan mata ba.

Hawaye ne suka sauko kam

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login