Showing 177001 words to 180000 words out of 219669 words

Chapter 60 - So Makamin Cuta Complete Hausa Novels Compelet By Surayyams.txt

14 Mar 2026

4105

yaudariya,ta ci amana na..ta cigaba da kuka,
Sai ya budi baki in xtreme suprise yace subhalllah zahida me kike cewa haka? Fada kukayi da ita,

Ya san komai amma sai ya fita nuna damuwan ta gaya masa meya faru a lokacin ,

Nan ta zuba masa labari komai da komai har maganan shiga koto abu daya da ash bai ji ba shine hidiman ta saminu
Sosai ta boye sai ta nuna masa yanzun ta rasa yadda zatayi ta kwaco hakkin ta ne .bata san ya zatayi ba

Cikin yanayin damuwan da bai kai zuciyan sa ba ya shiga salati yana sallamewa
Ya nuna mata abun ya dame sa matuka har da cewa baisan haka mum take ba,
Sai ya shiga bata baki yana ce mata komai ya kare insha Allahu shi zai taimake ta kuma ya bata assurance zata karbi hakkin ta ..

Ta dago tace but how ? Bani da shaida a kanta mai karfi

Yace, kince ance miki harda wil din plantatiom din ku ko?

Ta ce eh har da shi,
Yace to bari na baki shawara sai ki duba ki gani

Ta nitsu ta share hawaye tana jinshi

Yace tunda arzikin rodriquez duk na yayan sane ,kinga ko za'ace will din wanda suka mutu ne, ba ma ita za'a tranfering ba, ya kamata ma yayan rod ne wanda suke raye am i right?

Ta gyada kai,,

Yace good kinga kenan tunda kina ganin ure not eligible enougth ki tsaya akan dukiyan maman ki kuma kiyi fighing akan na baban ki.

Ni zan iya taimaka miki mu fitar da brothers dinki a prison

Kinga Ranar sharia sai kawai sai ku taru kuyo defending hakkin ku,

I think yanzu ai kun girma da zaku rike arzikin ku da kanku
Sai aba kowa gadon sa na tun asali
Kefa kaso biyu kenan, sai ki karbi na mahaifiyar ki ki karbi kason ki na mahaifin ki kuma.

And i trust my baby nasan zaki iya handling dukiyar ki ba tare da taimakon wani wanda zai cuce ki ba..

Tayi shirruuuuu tana saka maganan tana hadawa tana jerawa a brain din ta
Tace tabbas wannan zaifi mata ciwo in mukayi haka,
Kaga ko a haka na rama abunda ta min
Shikenan A garin neman hadamar ta sai mu karbe komai kowa ya rike nashi a kyale ta da halin ta .

Ai nagani a asalin will din mahaifin mu bata da komai, ashe duk karya take yi baita ba
Sai ta sa aka yi fake duk nagani..

Ash ya jinjina kai yace,
Kar kiyi gaggawa kuma ni shawara kawai na baki
Atleast kinga kema kinyi adalci ko?

Tayi murmushi ta taho zata rungume sa ta hada masa kiss sai yayi saurin kaucewa gefe:

Tace baby,haba dan Allah ni kenan kullum haka?
Kamar zatayi kuka ta kuma cewa I tot yanzu mun zama daya ni da kai tamkar jini daya ne,
Kasan sirri na baby meyasa bazaka bari naji dumin jikin ka ba? dont u think we need some sexual connections, baby aure fa zamuyi

Sai ya sauya mood ya mata shiru tana ta magana ita kadai, sai tace yawwa ya kamata ma kace wani abu akan weding din, like yaushe zamu soma shirye shirye
Don nifa ena karban hakki na wajen wancan shegiyar sai muyi auren ko?

Ash ya saukar da kai kasa kamar wanda yaci kudin aika still yana shiru

Nan ta sha jinin jikin ta ta dago sa a hankali ta ga fuskan sa a murde,kamar mai shirin yin kuka sai alaman damuwa sosai ya bayyana,

Tace meya faru Ashween yanzun nan muna magana lpya lpya,sai ka kuma sauya fuska ?
Ko na nafadi wani abu ne
Marar dadi.pls tell me

Ya marairaice kalar tausayi ya rike hannun ta yace,tsoro nake ji zahida im scared baby, ina son na fada miki wani abu amma ena tsoron rasa ki a rayuwa ta, i want to be with u ,bana son ki rabu dani

Tuni tom and jerry suka soma mata zanen flower so a brain din ta, tsaban dadin words din nashi da ta ji har wani iska mai dadi ne ta zuka ta hanci cikin kula sai tace tell me mana dan Allah ,meye matsalar
Kaima kasan A duniya banga mai rabani da kai ba,dan Allah ka fada min ..

Yace uhm uhm zahida, gaskiya ena tsoro musamman ma yanzu da muka sa maganan aure agaban mu,i dont want to loose u,ena ganin maybe kice bazaki aure ni ba.

Nan hankalin ta ya soma tashi sosai don ta dauka ko zaice mata ance daga gida ya auri jasmine ne tunda tana da cikin Sa sai su zauna tare.
Tayi shiru Batace komai ba
Sai ya dago ya nuna mata shatin canula dake hannun sa alaman Yayo kwanciyar asibiti sai da bandages din Kansa daya ki cirewa.

Yace baby na miki karya tun ranar, accident nayi bana ma abuja ena lagos

Pls Kar kiga laifin kamal ni nace ya gaya miki hakan

Cikin terifyn mood Tace o my god, haba baby shine nake tambayar ka bandages din meye ne kaki fada min?

Sai ya dakatar da ita ya dada sauya fuska yace
Ba haka bane zAhida, bana so na daga miki hankali ne,

doc ne yace ,.ya..ce

Sai tace yace me..sai ya dukar da kai kasa.

A sanyaye yace i lost my potency sanadiyar hatsarin danayi,zahida bazan iya komai da mace ba.


A hargitse ta mike tsaye tana kallon sa tace what?me kace?

Sai yayi saurin riko hannun ta yace "Amma Kuma yace zan warke sai dai ba da wuri ba sai nan da 6-9mont,ya marairace yace
Kuma kina son auren da wuri ko?.kinga ba amfanin mijin da bazai iya biyan hakkin wife dinsa ba
Im sure u wont like it..


Ta dan ja da baya ta kalle sa taga duk ya nuna damuwar sa ,ta dauki mint 3 tana shiru
Chan tayi ajiyan zuciya ta dawo ta zauna ta dan ja karan hancin sa tace har ka tsorata ni wallhy,

Na dauka zakace an aura maka wata ne ba ni ba, don gaskiya kishiya ne kawai bazan iya zama da ita ba.
Dum da ma still bazan bar mata kai din ba.

ya dada sunkuyar da jai abun sa ,kalar tausayi

Sai tace hey baby, ka gani
Kar ka damu da wannan maganan, ko shekara ne zakayi baka warke ba ni zan jira ka ,kar ka manta i love you alot damuwar ka ai nawa ne.
So stop worying urself am ok with it kaji?

Yayi takaitaccen murmushi yace ,nagode zahida har kinsa naji sanyi a raina"

A ranta tace wow ashe haka Ash yake so na?im so stupid da na kasa fahimtar sa tun da chan,

Yace na yarda yau,kuna nagani baby na tana so na.and i promise u zan tayaki figthing akan koma waye a duniya da zai takura rayuwar ki, im here for u.


Tsaban dadin kalaman san bata iya bude baki ba ..sai murmushi kawai takeyi, irin yau ni ashween ki zuba ma wannan kalamai?..its a dream come true to me.

Tace to sai muje muci abinci ko naga 6 ya wuce

Yace ah a sallah zamuyi baby,

Tayi saurin cewa toh shikenan, sai ta haura sama don ma kar yace taje ita ma tayi sallah

Don bata son hakan ko kadan,ta tsana. gani take alwala takuri ne bare kuma rufe jiki da sa goshi akasa yin wani sallah.


Tun daga ranar komai ke tafiya mata dai dai
Don ashween yana kula ta ya kuma sa mata hannu sosai akan hidiman fitar da su jamal

Abune mai wahala kwarai amma sai ya nemi taimako daga chan sama aka sa baki Aka sake musu brothers dinsu ana washe garin shiga kotu da mrs hidyat.


Ranar da su jamal da jabir suka fito Sunyi murna kwarai suka gode ma ash,

Nan zahida ta gaya musu komai abunda ake ciki,
Duk da ma ba suji mamaki ba

Jin an dago maganan lateef da lailah yasa jamal ya sake shiga wani hali,yace yayi nadaman yadda suka salwantar da rayuwan su yana daya daga cikin abunda ya ke damun sa sosai a ran sa yanzu.

Ash yayi shiru yana kallon sa don har ransa yaji dadin jin haka, sai jabir ne ya rarrashe sa shima cikin nadaman rayuwa,

Jamal din yace dama baida niyyar komawa ma familyn rodriquez rayuwar sa kawai zaije yayi sabo,
amma kodan ya hana a sake aiwata wani zaluncin da hakkin su lateef zai amince ya bada hadin kai aje da shi kotu a tarwatsa mum din su.

Jabir yace kayi gaskiya, nima ya zama min dole saboda ni kaina bansan eya adadin yayan ciki na da aka kai ophanage homes ba.samun saukin kawai yana da tabbacin duk na garin nan ne ba a fitar da su ba , sai ya yanke hukuncin in ya karbi kudin gadon sa zai raba biyu ya kai gidan marayu,

sannan yace yana so ya auri jummai tunda ance yanzu tana dauke da cikin sa kuma ta kusa haihuwa,

Ashween kamar zaiyi kuka jin wayannan kalmomni a bakin su.
Yace ko bai gaya musu shi waye bane a wajen su lallai nadaman su ya biya shi.

Zahida kam murmushi take binsu da shi, tana kaunar su sosai kuma taji dadin sauyawar sun amma ita kam yanzu take jin zata fara cin duniyar ta don haka zuciyan ta bata nan yake ba ,

Bata furta ba kam amma ko kadan cikin ranta ba damuwar ta wani hakkin lateef ko lailah bane,
Damuwar ta sabon rayuwan arziki da zata shiga ciki, ga masoyin ta Ash ,sannan ga shi ta na jin zata dau fansa ma mahaifiyar ta ta hanyar wulakanta mrs rod bayan sun karbe dukiya a hannun ta gobe..


Da safer rod ta riga kowa hallara ,taci kyau iya kyau sai hotuna media suke daukawa

Tsaban farin cikin dake balbale a ranta har dan takaitaccen hira tayi da media ana dauka

Anan tace musu tayi aiki tsawon lokaci cikin sirri da jajircewa wajen rikon amana kudin marayun yayan ta, sannan yau zata nuna ma duniya ita kanta mai ta mallaka, kuma duk abunda ake zargin familyn ta dashi yau zata wanke.


anan a wajen su jamal kaf An gama shiri, zahida ta karbo komai a hannun saminu, sannan suka shiga mota su ukun suka kama hanya..


Ashween bai samu damar halarta ba saboda anyi masa kiran gaggawa daga lagos cewa dattijo mr fadhul na cikin wani hali, kuma yayi umarnin ace masa ya zo akwai muhimmiyar magana da zai gaya masa.





*Good morning people, ni dai nace im a woman and i lost my potency irin na Ash🤣😸😂 amma nasan kawayen zahida ne kawai zasu yarda*









*surriem*
*⚜BRILLIANT WRITERS ASSO🖊*



💔

*SO MAKAMIN CUTA*
_'the sword of evil love'_


_Story and written by_
*SURAYYAHMS*🔥



*DEDICATED TO-*@UMMERHERNY NERSALLAH.





*Pageâ–¶77*





Gefen Jasmine kuwa duk da abubuwan dake damun ta dan dolen ta
tayi hakuri tana cin abinci normal
kuma ta soma dan sakewa har su dan yi hira sama sama da mamy "inda take fada mata za a soma gyara mata jikin ta tunda ta samu miscarriage,mamy tace ita da kanta zata kaita a dada kimtsa ta sosai ko dan taji dadin jikin ta.

Duk ana yi ne Sai dai zuciyan ta fall yake da son jin dalilin da ya hana ashween bai zago ya duba ta ba yau har sati biyu kenan...

Gefen mrs rod kuma ana neman karfe 8am na safe ba taga an fara kiran sharia'r ta ba sai ya sa ta shiga wajen judge tace ' mr judge dan maliki, ya dai an barni ena ta jira meye ne haka?

Yace calm down mrs rod
Na gaya miki Akwai muhimman abunda nake jira akan case din nan naki ne
Ki bani minti 20 za'a kira

Tace ince dai lpya ko?
Meyasa baka sanar da ni akwai jira acikin harkan nan ba.

Yace mata kar dai kimanta aikina da tsari
Kotun ne ta sauya lawyer mu da mai bincike da tantance case, amma kinsan ai duk munyi maganan wannan dake ba matsala ko?

Tace of cous, yanzu shi ake jira kenan

Alkali yace eh,pls sit down and stay put, kar ace muna hada wani abun dake kinsan ansamin ido..

Ba tace komai ba ta juya ta zauna ta tare da harde kafa.

Ko minti 5 bata yiba da zama saiga shi comitten sharia sun soma shigowa

sai tana binsu da ido tana murmurshii tana Allah Allah minute of success dinta ya zo
Har wani lumshe ido take don farin ciki..

Ana kan shiga sai ga lawyer mai bincike da tantacewa ya dosu,shima ta bishi da ido tabbas wannan bata san shi ba,sannan fuskan sa ba wasa ko fara'a,

tana kau da kai kansa ganin wa zai sake shigowa
Sai Zama ya gagara ta mike tsaye cikin wani razanannen shocking tana bin zahida da kallo,
Ga jamal ,ga kuma jabeer tafe.

Take fuskan ta ya tsatssafo da zufa zuciyan ta yayi bugun tara tara , ta rufe ido gam tana dan bubbuga kai a hankali ko zata tashi a mummunan mafarkin da take

Su kuwa Haka suka zo suka wuce ta gaban ta ba wanda ya mata kallon arziki
Kowa ya zauna aka barta a tsaye durus tana kan waswasin abun

Jin anbuga akalar sharia za asoma ya sa ta dan razana Ta zauna tsuliya a zage .

Gaba daya sai taji gwiwan ta suna karkarwa hankalin ta yakai makura wajen tashi, jamal, jabir zahida ? Kai wannnan ba alheri bane.tace ma kanta.

Ba bata lokaci aka soma shari'a
Sai gashi Tun kafin sharia yayi nisa, notin kan mrs hidayat ya soma kuncewa ta fara hauka.
musamman da aka kawo shaidan cewa tunda lailah ta mutu ,akwai lateef sannan bata da shaidan cewa yana raye ko ya mutu don haka anyi invalidating case din su lateef har sai an samo gaskiyan lamari in aka tabbata ya mutu shima sai azo ayi magana,kotu ta buga wannan,


Nan ma Ta hadiye yawu da kyar tasan wannan ya kubce mata kenan har abada ,

Sai aka cigaba anan aka dago na hanan hrnandez
Nan ne fa lawyer mai tantacewa ya bada korafin Hrod tana da will a karanta a kotu aga arzikin ma waye ne ,


mrs rod bata so haka ba,
Amma kasancewar akwai original will din Hrod a hannun lawyer wanda zahida ta bayar sai ta dakata dan dolen ta aka karanta.

Hauka sai ya kunce ma mrs hidayat aka dawo rike ta ake yi tana kuka.

Nan alkali ya bada izini aka ba zahida dama itama tafadi abunda ta sani akan haka

Zahida ta tashi Ba mutunci,ba kawaici ko kunya tsaf zahida tagaya musu komai, tun daga yadda mrs hidayat ke hana su sanin komai akan hakkin su na mahaifun su, da yadda take sirri da mulki da su akan hakkin sun, da ranar da ta soma ganin key din hrod a offishin mrs hidayat kankat ma har da case din rasa contract din plantation sai da bada bayani gamsashu.

Aka kuma baza proofs gaban kotu aka ga komai hakan ne,
Ga shi yau mrs hidayat ta riga ta fada ma yan jarida a sirri take rike da kudin yayan ta Marayun,
Take sai aka juya wannan maganan nata aka ba zahida gaskiya na cewa eh duk tana hakan ne don ta musu yankan baya da hakkin su.

Mrs rod Tace Allah ya tsine miki zahida uwar ki tayi asarar haihuwa,

zahida tsaban munafurci sai ta sa kuka ma judges akan akarba mata hakkin ta ita tsoro take ji, cewa anyi depriving dinta right na samun wani access da late mahaifiyar,
tace ko a hoto mrs hidayat ta hana ta ganin mum dinta, ita ta an toye mata hakkin ta na dan adam..a taimaka mata

Ta cigaba da kuka sai da
Kowa hankalin sa ya tashii gashi sai dauka ake yi a cameras ba sauki,

Karshe jamal ne ya rungumota ya zaunar da ita yana rarashinta,

Alkali yayi rubuce rubucen sa ,ya ce akwai mai magana? sai jabir yayi saurin cewa eh,
Nan ya roki alfarman kiti da a raba musu gadon su yau kowa ya huta,.

Bisa ga dalilai masu karfi kotu ba bata lokaci ta shiga kasafi aka raba gado chas chas ,batare da antaba na ashween da sisters lailah ba akan sai an bincika anji ko yana raye ko ya mutu duk dama alkalin ya san gaskiya.

Kafin azo wannan matakin mrs hidayat ta suma sau sha takwas
Sai ya dawo rike ta akaye kamar tsohuwar lagwani bata iya tsayuwa da kafan ta.

Asalin will din rod data boye tasan bata da gadon shi kona ficcika gashi da shi akayi shariar ba da fake din ba

Don a fake an nuna tana da 30% alhalin dik ashe karya takeyi..

Kotu ta zo karshe enda aka maida ma zahida dukkan abunda mahaifiyar ta ta bar mata ,,
Sannan da kaso ta na gado

Aka kuma bayyana mrs hidayat a matsayin azzaluman uwa, barauniya,mai danne hakkin marayu,

Ranar Kowa wani shafin jarida da gidan talabijin da kalar sunan da ya kira ta labari ya dawo latest in town

Dadin karawa kotu ta tsare ta tsawon wata uku..
Da likita da hukuma aka zo aka fitar da ita,

A lokacin mrs rod ta zare har tayi kusa yin ma kanta tsirara garin yage yage da fincike fincike tana hauka tana kuka tana zage zage...

Bata tashi sake suma ba sai dai jamal ya gaya mata bakaken magana, jabir ya kara mata da mai zafi sannan zahida ta cinna mata wuta a kirji suka nuna mata ita kadai ce yanzu a duniya, ba su santa ba..kowa kuma yayi hanyar sa.

Daganan mrs rod a motar ambulance aka tafi da ita ga hukuma akan ta suna kula.


Rayuwa yayi ma zahida dadi, duk da ma can kasan ranta taji wani digon tausayin mum din nasu,

A ranar jamal ya bar nigeria yace musu zai tafi mexico ya tada rayuwar sa a fresh,

Shikam jabir da ma ya gama plan dinsa har yakan je ya duba lpyar jummai a gidan gwamnati da suka dauki nauyin ta.

Bangeren ash kuwa yana isa lagos aka masa jagora wajen mr fhadul,

Duk da yaki nunawa amma zuciyan sa ta dan tabu da jin labarin halin da yake cikin

Domin yasan rasa shi wani mummunan rashi ne a gare shi,
Ya zame masa tamkar guadian angel wajen lura da hidimomin sa da sa shin akan hanya wanda shi kansa bai san da su ba,

wata rana yakan yi alfahari da shi yace da bazar sa yake taka rawa,
Mr fadhul kwararre ne mai ilmi da basira nagani na fada,

Dan ko shi ashween mamakin sa yake sha musamman in yana koyaar da shi abubuwa da dama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login