Showing 93001 words to 96000 words out of 219669 words

Chapter 32 - So Makamin Cuta Complete Hausa Novels Compelet By Surayyams.txt

14 Mar 2026

4101

KARA MANA LPYA,WANDA BASU DASHI ALLAH YA BASU.*





*Page▶43*






Nan mrs rod tayi ma jasmine hannu alaman tazo daf da ita ta zauna ,
Ba musu ta zo jikin a sanyaye dom sam a dar dar zuciyan ta yake.

Nan mrs rod ta soma jan ta da hira don sosai take so taja ta ajiki ko dan ashween Ya dada aminta da plan din ta

Zahida kuwa ko ta juya ta kalli jasmine din bare ya dame ta, don tunda suka gaisa sama sama ta dauke kai hakan ma don ashween na wajen ne

Sai ta zauna shiru tayi da fuskan ta kamar abunda duniya ne kawai ya mata yawa,
tunda yanzu sun dawo laughing stock a media 68% na hanyar arzikin su yay droping a cikin kwana biyu kacal, ..

Madam hidayt da kadan kadan take jan jasmine da hira su biyun su har ta soma sake wa kadan

Nan Wayar sa yayi kara
Yace xcuse me ya tashi ya bar su awajen su uku,
Duk son maida hankali suna kallon yadda jasmine ta juya tana binsa da kallo har ya kule Ba tare da tasan tayi hakan ba,

Murmushin keta suka sakar tsakanin su ,
A hankali mrs hidayat ta dafa ta tace my daughter,
A dan daburce jasmine ta juya tace yes maam
Uhm ...uhm... ta girgiza mata kai tace kar kina cemin maamm
Im also your mummy daga yanzu, ko dan kinji ashween son yana fada ne,? Oh c'mon Ai shima don baya ji ne don't be like him ok,?tafada cikin sigar wasa,

Murmushi kawai jasmine tayi tace ok mum,

Tace good ko kefa,
Ai dama nasan kinada kirki sosai tunda ganki nasan kinada hankali,

Ta sunkuyar da kai kasa batace komai ba
Nan mrs rod ta cigaba, tace
Uhm My daugher ena fatan kinsan nan gidan tamkar gida ne ma ashween, kema zanso ace kin sake jikin ki da kowa don tamkar jini muke

Ta nuna zahida tace ga sis din ki nan,
I hope kunyi setling difrncess din ku,? Jasmine Tayi shiru tavrasa me zata ce.

Mrs rod tace c'mon preety jasmine,pls ki zama mai tausayi da yafiya mana, kinga yar uwan naki tana cikin tashin hankali she needs u.
All of us as a family har dake ya kamata mu yafe ma juna ko?

Nan zahida ta ari bakin maganan tace mum, pls..tana kifi kifi da ido alaman taji kunyar karya.

Jasmine bata lura ba kawai tace bakomai mum, ai na yafe mata komai ya wuce.

Nan mrs rod Ta sake wani sarkakken murmushi tace Am so proud of u.Allah ya miki albarka ,as beautifl as ur hrt..
Ta juya ta kalli zahrod "
Oya ke me ki kace mata zahida
Nan ta dube ta badon ranta ya so ba tace " im sorry hun?
Jasmine Ta gyada kai ta danyi murmushin yake.

Gefen su ashween kuwa ba irin lallabi da kamal bai masa ba sam ,ashween yace shi gaskiya sai dai acanza plan don ba zai amince da komawar zahida gidan sa ba har abada, cewar sa " im tired i want to be with my wife kamal.


Kamal yace haba ash , ai dama nasan duk dan jasmine ne kake cewa haka
amma kasan plan din nan zai wargaje da wuri muddin zahida tana zaune da mrs hidayat ko?me akayi kenan.
Shes already poisoning her mind ita take bata duk wani master plan data ke amfani da shi wajen cutar da mutum

Kar garin kare matar namu fa mu jefa ta cikin mummunan hatsari.

Ashween yace kamar ya fa, tana tare da ni wani hatsari kake nufi kamal,tab ashe ko da duniya zai tashi

Kamal Yace look, to kafa fara cin brain , wai ka na tunanin zahida da mrs hidayat baza su gane jasmine matar ka bace in suna tare ku kuna chan?kaifa ka fada min bala"in kishin da suke tafkwa tsakanin su,

mrs rod ai mahaifiyar ku ce, tafi ku nisan tunani duka, in har zaka iya wasa da hankalin zahrod akan jasmine kasa ni u cant fool mrs hidayat.
Nan ma Ya kalle sa yace
And I dont think zaka so abunda zasu ma jazmine
In suka fahimta matar ka ce. Hiding it is the beat way to protect her now


Ash kwata kwata Baiso hakan ba,Amma sai yayi saurin dake wa yace cewa "ya isa haka toh
C'mon why are u scaring me kamal, ba abunda zai taba min ita.. Sannan ya sauke numfashi yace
Toh dai Naji hakan zamuyi bawani changi, lets just go na barta ma tare da su,

Kamal yyi murmushi yace ko kaifa..c'mon just relax,
In don jasmine ne nasan ba matsala cos she loves u alots zata fahimce ka, kuma kaifa kafi kowa sanin yadda zaka shawo kan matar ka su zauna har komai ya kare.

Yace haka ne,ure right, nan suka dunguma suka shige daga ciki

zahida na zaune tare da jasmine a dayan falo suna kallo kamr shiru kamr ba su ba..

Nan su ash Suka kalli juna da kamal alaman hmm yau kuma

Duk da ma ba magana suke yi ba sai yayi kamr babu komai tsakanin su ,
Kamal yayi gyran murya duka suka juyo suka kalle shi,
Yace yan mata ne haka,
Jasmine ne ya soma maganan tace yay kamal, ena wuni
Yace fine yar kwai, kin kyauta da kika zo ai..
Tayi murmushi

baby, haw far?, yace ma zahida da ta dan daure fuska tana masa hararar wasa,nan ya zauna cikin su
Kadan kadan suka taba hira ,

Idon Ashween kuwa nakan matar sa don har ya lura kamsr ta dan sake kadan,
Shidai Baice komai ba sai daga baya yace ma zahida,
Ena maam take,
Ta wani karairaya murya ta dago tace tana sama dama kai take jira,
Bai amsa ta ba
Ya dawo gefen jasmine a hankali yace ena zuwa tare da dan shafa gefen face dinta a dabarance
itakam sai kallon sa kawai take bata amsa ba

Dakin sama suka tafi da kamal enda madam hidyat ke kwance,
Nan suka gaisa da kamal,
Ta zaunar da su

Surutun ta take wanda ta shirya su tsaf cikin hikima da fasaha da daukar hankalin duk maijin ta,
Ta ce ashween bansan ya zan nuna maka yadda anke jinka araina ba, amma bani da wanda nake jin zan jingina kafada ta akansa yanzu in bakai ba,
Son Ka taimake ni ,ka ji kaina tamkar yadda zaka ji kan mahaifiyar ka

Take zahida with you ka koya mata harkokin gona ko zamu samu mu daga 68% na harkokin mu .da suka zube tsakanin jiya da yau.

I know i have no rights, Kayi hakuri gadara da kai ne ya sa na ce kamin hakan ,kuma naga ure one of the best managers na ranch da plantations A kasar nan.i will be honoured en ka taimaka min son pls.
Ta goge hawayen ta cigaba... tace I lost my children kuma kasan duk maza ne suka tafi, badon haka ba da sai mu bi ta wani wajen,to nayi tunani eya tunani bani da lpyar da zan iya harkan papers a yanzu.
Yanzu Gonan ne kawai zai sake dawo damu kan kafarmu akan lokaci ,dama chan shi ya dago mu tun marigayi alhj abdul fatah rod yana nan
Basu ce komai ba suna binta da ido

Kafin su hankara gani su kayi tayi kasa ta tsuguna gaban sa tace pls ,pleasse
Help me son, help me. Ta rike gwiwan sa tana jimami kalar tausayi.

Kamal ne ya kalle sa alaman me kake jira ne wai... mahaifiyar ka ce fa?

Ko ya ji ajikin sa saima kau daknsa gefe dayayi ma dan lokaci
Nan Ya sa hannu ya dago ta yace
Ai Nayi fushi dake maam,
Ashe har sai kin roke ni na taimaka miki?
C'mon wannan ai ba wani abu bane.
Dont worry ok?take yasa fuskan tausaya mata shima kamar ba shi ba yana fooling dinta da calming words
Wanda yasa kamal jinjina masa aransa yace hmmmm

Nan Tayi murmushin jin dadi tana goge hawayen ta tace Allah ya maka albarka har karshen rayuwar ka son,
I truly love you son,ni dama tun dana fara ganin ka nake jiN ka har ajini na ..ta riko hannun sa dam tace
Kaje duk enda da kaje a duniya ba abunda zai sameka sai alkhairi,

Nan Duka suka amsa da ameen..
Haka shima kamal ta dinga praising din sa da kyar dai sukaa rabu,
AKan zata gaya musu komai da komai game da aikin da duk abunda suke bukata kafin a soma aiki akan gidan gonar na su


Dama Allah Allah jasmine take taga fitowar su don tagaji da zaman kurmayen da suke yi da zahida
Yana zuwa kuwa ya sakar mata murmushi a dabarnce itama ta turo mai baki cikin sigar shagwaba

Me yace ma zahidan ne sai Allah dan a hankali sukayi magana tsawon minti 5 kafin ya ce ma jasmine lets go,
Kishin nan nan aranta amma sai ta dan ji saukin sa yau don sosai ta dan tausaya ma yanayin su zahidan musamman mrs rod..
don Bakaramin wasa da tunanin ta sukayi ba dazu a dakin
Don har maganan zahida zatayi aiki a yola sai da sukadan tsakura mata duk da ma basu ce a gidan ashween zata sake dawowa ba.

Cikin motar suna tafiya Kamal ne kawai ya ishe su da surutu don sai da yasata dan dole ta sa baki a hirar tasu ,
ashween kuma yana jan motar yanata dariya kasa kasa don yawanci hirar tsokana ne da shirme,

Nan Har suka ci abinci tare su ukun a wani bukataria,
Kafin sukayi sallama enda kamal ya dada jaddada mata zai samo mata salma nan ba dada dadewa ba.

Da hakan su ma suka tafi gida
Bayan anyi isha'i, sai 8 ya shigo ya same ta alaman ta gama komai tana shirya musu kayan su na tafiyan goben.

Zama yayi gefe tana nadewa yana sa mata a bags
Yana tsokanan ta tana shaqwabewa
Har aka zo kan tsarabar mamy,
Yace bani naga meye ne aciki wato ke kadai aka sani banda ni ko

Ta damke abun ta tace ah' a , yaya me zakayi da shi
Naga dai duk abun Mata ne aciki yaushe kadawo baby girl?

Abun ya bashi dariya yace nidai abani naga abun matan ,ai in ni ba bby girl bace ena da baby girl,

Hararar sa tayi don inya fadi hakan saita rasa da ita yake yi ko da zahida

Haka ta ki fir ta damke abunta ,yace to bakomi, zan rama

Tace eh ,kawai ka rama ai turare ne anan din ba wani abu ba,

Yace ohhhh kin gwammaci na rama akan naga turaren

A dan tsorace tace ehh,
Ai ko rufe baki batayi ba taga yayi wuf ya kashe wutan dakin guri ya lume dum yayi baki, sai karan Ac
Ai sikinini ta ajiye ledan agefe tayi tsit zuciyan ta na neman fara bugu

Shi kuma saiyayi shiru ya dauke numfashin sa yana gefe yana hangen ta .
Tayi lalume tayi laume ba taji kowa ba

Chan Tace yaya ka tafi ne? Taji shiru.
.ta sake cewa, yaya ena kake ne? Still shiru....na ukun ta karkace murya kalar kuka tace wayyo Allah yaya na..wallhy tsoro nake ji

Shiko Yana shiru yana jin
Ta dariya ya riga ya cika masa ciki
Haka ta cigaba da bare baki tana lalume tana kiran sa cikin kukan shagwaba,

Amma shiru,.jin kukan ya soma yin Tsanani ya tashi ya lallaaba ya janyo ta jikin sa a hakan ma saida ta tsorata tana fizgewa
Ba don taji qamshin jikin nasa ba tayi niyyan kurma ihu ne don tsoro.

Haushi ne ya kamata musamman data ga yana mata dariya,tace shine zaka tafi ka barni kalan wani abu ya kamani ko?

Yace me zai kama ki?.naga abunda kike tsoron Ma ya mutu saura me kuma

Ta murguda baki,ta dada lafewa jikin Sa,
Nan ya dago ta suka haura gado
Shiru Sai safiya kuma,


Agogo na buga 7.05 am alaman har sun kammla ibadun su sun koma bed "suna jone Kissing in minti 15 yake mata Yaki ya sake mata lips bare tayi numfashi

Sai da ya kammala ya ji dai dai sannan yace,to nagama nima ki rama min, ta gwalo ido cikin ranta tace kaji fitina, ni dai na gaji wallhy a
Shikenan ayi ta abu daya tun jiya,?
Kamar wanda yake karantar taYace bazaki min ba ko,

Ta marairaice tace yaya bakace gida zamu tafi ba naga ranar da sassafe muka zo nan garin ai sai muje gidan mu ma da sassafen ko?

Yace um.. um..ba zamu je ba don bacci nake ji jiya kin hanani bacci

yau anan zamu zauna
Har Sai na rama baccin, that is in kin iya sani , in kuma baki iya ba kissing dina kawai zaki nayi har sai na koshi nace stop.

Ta dago tana kallon sa ta takune fuska, yace yes
Me kike ce,?wanne zakiyi daya

Nan ma ta dada tashi da niyyar langwame mai wuya ko zata samu ta lallabasa ya hakura ta huta
Sai akayi rashin sa'a,garin tashi bargon ya yaye rabin gefen kirjin nata awaje wanda ya dada dauke hankalin sa,

Bata fasa ba Ta takune fuska shima nan ya bita ya takune nashi fuskar kamr baby
Yace ok toh wannan nake so,nafasa sauran.. ya nuna mata boobs dinta da hannun sa,

Anan suka soma hayaniya amma sai dai Duk kaucewar ta saida ta hakura ta sakar masa yana wasa da su yadda yake so har baccin ya dauke sa da gaske

kansa ya lafe kan kirjin nata wanda sai zugi suke mata sama sama,gashi ya dau lokaci yana bacci har kusan rabin awa bai tashi ba

Itako tana nan bata runtsa ba hankali kwance take kallon kyakkwan fuskan sa tana jin kwanciyar hankali da nishadi a zuciyan ta.

Sosai ta kara jin son sa na yawo a cikin jinin ta
Nan ta Dan dukar da kai ta manna masa kiss a bakin sa dayake daf da kan nipples dinta

Ji tayi ya sake damke hannun ta acikin baccin,
Ta dawo tana kallon sa a hankali ya bude ido shima
Kallon kallo Kawai suka aika ma juna na sakon so, chan tayi murmushi tace
Yanzu kam zamu iya komawa gidan ko ai ka rama bacci

Yace of cous, amma badan kinyi kokari ba dai don kawai na hakura ne.
Nan duka suka danyi dariya
Ba bata lokaci suka kimtsa tsaf
Amma duk da haka sai bayan azahar jirgin su ya tashi zuwa yola.




🤒




*surriem*
[23/08, 05:42] ‪+234 806 071 2446‬: *⚜BRILLIANT WRITERS ASSO🖊*



💔

*SO MAKAMIN CUTA*
_'the sword of evil love'_


_Story and written by_
*SURAYYAHMS*🔥



*DEDICATED TO-*@UMMERHERNY NERSALLAH.



👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻👏🏻





*Page▶44*





Tun da suka kama hanya Wani sabon nishadi jasmine take ji Tun da har suka isa yola
Sabida gaba daya sai ya sauya mata tun ajirgi yake ta sata nishadi har suka iso bai dena ba.


Komai tsaf gidan tamkar basu je ko ena ba
komai ma'aikata sun gama hatta abincin ya zama ready,

Nan ma tana kan kammala ajiye tsarabn ta da mamyn ya leko ,
Yace mata tafito su ci abinci,
Toh ta amsa masa da shi sannan tayi saurin kimtsa kanta, ta fito.
Suna ci yau kowa da nashi har aka watse ba wani hayaniya.

Ashween Gaba daya ranar baije ko ena ba,ko ya fita ma bai kaiwa minti kadan sai ya dawo
Abum na mata dadi don bata saba ganin sa arha a gida har haka ba.

Wajen bayan isha nan tasha make up din ta
ta sa fitted gowm rigar atmpa pitch wanda yaji style din zamani mai kyau tana zaune gaban mirror tana admiring beautyn ta.

ganin gidan yana neman yi mata boring bai dawo daga masallaci ba, ya sa ta dauko wayar ta ta soma scrolling tana kallon hotunan data masa ranar a abuja,.

Sosai murmushi ya bayyana kan fuskan ta sai zuba zance take a zuciyan ta ita kadai,tayi zurfi ta shagala wajen kallon bata hankara ba taji kyat an kashe wutar dakin

A firgice ta dago zatayi magana sai kyat ya kunna ,
Ganin yadda tayi tsuru tsuru tayi setin kuka ya sa shi yin dan dariya yace mutum sai shegen tsoro kawai, kika sake kika min kuka anan ko tam.

Bata fasa ba don gaba daya zuciyan ta bai daina bugun ba... , nan ma ta marairaice fuska sai ganin hasken flash tayi ya mata pics bazata.

Tayi saurin rufe ido,alamn jin kunya .
...yace u look great da normal face dinsa still yana tsaye daga bakin kofa,

Murya kasa kasa tace thanks,you too
A kunyace tace Kaima kawo na maka toh

Yace ni? Noo.sai dai in zaki biya ni, haka kawai ki dauka min fuska kyauta.?

Tace ok fine. nawa ne?

Bai amsa ba Daga enda yake ya ware hannayen sa duka alaman ta taho ta rungume sa
Duk da taji kunya amma hakan ta daure ta je ta lume cikin kirjin nasa ya rungume ta,
Dukan su murmushi suke yi, itako sai dada boye face take wai tana jin kunyar sa,

Nan yace toh dago na nuna miki photon ki, tana dagowa kuwa ya dauka musu selfie mai shegen kyau dukan su suna murmushi,

Rigima ne ya tashi awajen don sam ya hanata ganin pics din, sai bori take karshe haka ya dinga jan ta har suka sauko tsakar gida tana binsa har ya fice gaban motar sa tana tafiya tana bubbuga kafa tana kiriniya.

bai kula ta ba Sai da ya bude mota ya shiga kafin yace to zan baki ki gani amma sai kin koma kin dauko mayafin ki tukunna
Tace tab, lallai yaya wayo ko... kawai kace na tafi gida zaka gudu ne kabar ni, ta cigaba da juyi kamar xatayi kuka,

Yace ni dai nafada miki
In kika bata lokaci natafi kuma shikenan sai nadawo ki gani
kuma in nadawo bana bayar wa sai an biya ni,
Choose now or later, ya kdan kashe mata ido yace your time starts now.

Ai da a gurguje ta juya ta koma cikin gida sai dariyan sa yake yi a gaban motar har ta lume ciki,
Dawo wan ta keda wuya taga baya wajen dayayi parking

A kasa tayi jefa da mayafin ta fara numfashi mai dauke da fushi zata soma aikin kuka
Bata hankara ba Hannu taji ya sa ya dauke mayafin akasa ya hada harda ita ya dauke ya cigaba da tafiyan sa yana mata murmushi

chak ta yanke kukan ganin wani uban murmushin tsokana dake fuskan na sa,
Ashe dagan gan ya juya kan motar don yaga drama,

Nan ya sata a ciki suka tafi holewar su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login