Showing 183001 words to 186000 words out of 219669 words

Chapter 62 - So Makamin Cuta Complete Hausa Novels Compelet By Surayyams.txt

14 Mar 2026

4142

zame maka darasi ko gyara .

Kuma a gani na ba su bane cursed din ku,arnt justice served to you?

Enaga sanadiyar files din su fa aka soma tono naki matsalar har kika san gaskiyar rayuwar ki,haba zahida.

Ta dan tabe baki, tayi shiru tace ,haka ne
Amma kawai bana son su ne
En ma lateef din na raye na san yana chan ya zama almajiri ko barawo.

Ash yayi wani munafukin dariya yace what if Allah ya sa yana rayen kuma yayi kudi ya wanku sosai
Sannan ya dawo rayuwar ki
Zaki nemi gafarar sa?


Ta juya tare da dan ja da baya ta masa kallon ai hakan ma bazai taba yiwuwa ba
Yace answer me pls
Sai tace baby, i think zan saurara masa amma not realy don nasan wallhy wannan mummunan hallita bazai kai wannan matsayi ba, is impossible

Ash ya dada kwashewa da dariya mai ban mamaki sai da ta tsaya kallon sa
Yace ure funny zahrod,
Amma ba komai,

Muje ki huta ni zan sha iska anan daga nan zan koma gida.
Idan kika yanke hukunci zaki tafi hutun pls tell me.

Ta dan shagwabe ta ce wannan ai ba sai nayi tunani ba next tomorow kawai zan tafi hutu na kaima sai ka huta ena dawo wa by then ka warke sai muyi aure ko?

Yayi smiles yace good idea baby na,
Oya jeki ciki .. I will c u tomrrow


Ba musu ta tafi nan ta barshi gaban tomb din
Tsawon lokaci yana tsaye shiru yana kallon kabarin lailan sa

Har ya tsuguna nan yayi mata addu'a, hawaye taf taf a idanun sa daga nan ya juya ya tafi.




Yau dai abun son kai ne😛
Surayyahms fans page and grop gudnite ppl ilsm awajen🌹❤




*Maman khyr i think yanzu ena partyn ki fa zahida bata da imani ashe,?dama my meems kullum tana mata baki jeki zaki gani😅hmm ena saffah one""....mom khad yau naji ki shiru ko dan baba ne😪,Allah sarki rashida abubukar zuban cikin jas din ne ko dai bata nan ne?*
🙆🏽‍♀🙆🏽‍♀🙆🏽‍♀





🤝🏼💯.






*Surriem*
[23/08, 05:43] ‪+234 806 071 2446‬: *⚜BRILLIANT WRITERS ASSO🖊*



💔

*SO MAKAMIN CUTA*
_'the sword of evil love'_


_Story and written by_
*SURAYYAHMS*🔥



*DEDICATED TO-*@UMMERHERNY NERSALLAH.



*Page▶79*





Bayan kwana biyun ashween har airpot ya raka zahida..
daga nan shima ya bar garin abuja ya shigaba da harkokin sa har kusan 2 months bai leko ba Har Sai dai ya tabbata ya dan sassauta makan sa yawan tashin hankalin da yake shiga akan tunanin jasmine, kafin sai ya sa ranar zuwa abujan.


Kafin nan rayuwa yanzu ta kasance ma jasmine kullum tana kullawa tana warwarewa ita kadai

Don Cikin watannin sosai ta kuma haskawa ,tayi kyau ta yi fresh tasha gyara kam barakallh,sai ramar da ta dan yi ya dada fidda shape din hips da boobs dinta suka bada shape mai mugun kyau ma jikin ta bisa kan tsari.

Ko ashraf ma saida maitan sa yayi mummann tashi amma jasmine ta sauya hali na kamar da chan ba,
Dan Yanzu da kyar abu ke bata mata rai bare tayi hawaye.

Ashraf Tun yana ganin zata biye masa har dizgin da ta ke masa ya sa ya hakura Ya shareta shima

Cikin kwanakin Da tunanin ash ya ishe ta sai ta soma fita da kanta tana neman sa a gurare daban daban ko zasu hadu wata rana amma babu shi ba mai kaman sa,

Tasha zuwa gidan ammy amma ko ena a kulle ne gashi in banda spare key din dakin ta babu wani abu kuma a hannun ta.

Gashi salma ma ba ta kulata ba,
Ta samu dai sun yi magana ta tex a cikin watanni biyun don sau biyu ta amsa mata sakon ta daganan har yau kuma basuyi waya ba.

Duk ta damu musamman da tayi ta duban hanya ko zata ga ashween din ya sake zuwa amma shiru.
Taje ukraine ma har sau biyu makaranta nan ma tayi tsammanin ko zai biyo ta amma shiru


Tun tana danne abun har ya soma bata haushi,ga shi kullum ta tuno zahida kishi sai yayi kamar zai kashe ta ,sosai tayi fushi da shi duk dama bata san takamammen me zatace ya mata na laifi ba.

A cikin detention office kuwa mrs rod ta gama hayagagan haukar ta..
Tace sam makiyan ta ne suka hada ta da yaran ta.

Mrs rod Ta shiga wani mummunan hali a zuciyan ta na musamman ba don ma kudin ba kadai

,rasa yayan cikin ta ma yayi mugun taba zuciyan ta,
Tace tasan dai zahida bata da wayo ba zata taba iya tona mata asiiri haka kawai ba sai dai in zuga ta akayi.
To waye? Kullum sai tayi ma kanta wannan tambaya

Gashi cikin wata biyun gaba daya media sunyi facali da ragowar mutuncin ta a waje,
Dama bata da komai cikin kaso don haka wani karamin flat din ta ne ke jiran ta da motar guda daya tall ,

Bata damu da wannan ba saboda akwai kudin rodriquez wanda ta sace a bank achan switzland.
Amma tasan inta kuskura ta taba za a iya sake karbewa a danka ma yayan ta.

Yanzun dai ta qudiri niyyar muddin ta fito sai ta nemi munafikin daya hada ta da familyn ta ya tarwatsa mata rayuwa.

tace kisa Kawai ta yanke a ranta zata yi ma duk wanda yake da hannu a cikin tonawar asirin ta


Tun Ranar jumu'ah ashween ya shigo abuja,.
Da shike salma tana cikin watan ta na bakwai har a ana neman shiga na takwas
Wajen su ya wuni ,suna ta shagalin shirye shiryen sabon babyn da salma zata haifa nan ba da dadewa ba,

Gaba daya in ashween yana wani abun sai salma tana tuno da abunda ya faru,domin kuwa har yau tana jin haushin rasa na shi babyn da yayi...

Ba yadda kamal baiyi da ita ta kira jasmine ba amma ita ma taki sam ,tace bata jin yin hakan ne duk da ma she is no longer holding her,


'Ita kuwa jasmine ganin kowa ya ja baya da ita ya sa haka kawai yau take kawo tunanin iyayen na ta, sai ta soma jin zafi a ranta dama dannewa take bata so ta yarda cewa she lost all the important people in her life.

Amma kuma sai yana mata kaman hakan ne, babu mijin ta ash, babu ammy babu salman ta.

Tana zaune tayi zugum ta so ta danne kukan amma sai ta kasa sosai tayi ta kuma rarrashi kanta,
Sai ta yi sanyi kamar wacce bata jin dadi


Wani zuciyan yace mata ta tashi taje gidan ammy
In har tana so ta cire damuwar iyayen ta da mummanan background dinta aranta ,atleast koma yaya ne tasan ammyn ta bata taba rabuwa da ita ba


Da haka ta soma shiri kamar wanda aka ce mata in taje gidan ammyn zata ganta

Bayan asr Tayi wanka, tayi kwalliya mai kyau mai tsafta..sai ta ta feshe kanta da turare


Yadda taga ta fito tayi kyau cikin pink ankaran ta ya sa taji dama hakan ta keyi kullum..atleast ko damuwa ya dena nunawa akan fuskan ta a duk lokacin da ta tuno wani abun.



shi kuma sai kusan yamma ana neman 4 pm ya dawo gidan da shike baida niyyan sake fita sai bai bar motan sa a fili ba.


Da ya shiga dakin bayan yayi refreshing kansa sai ya nemi waje ya kwanta kawai a dakin ammyn nasa yayi shiru shi kadai.


Jasmine ta shigo dakiin mamy ta ce mata zata je super market ta duba text book din anatomy and phisiology vol 3,

Mamy ta dube ta da kyau tace A,ah ki bari ashraf inya zo zaije ya duba miki

Amma sam jasmine ta ki ta turje sai da mamyn dai ta hakura ta barta.


Mota ta dauka sai wajen 4 :55pm ta isa kofar gidan ammy ,
Nan Ta buga horn a hankali mai gadi ya bude ta shigo
Sai da tayi parking kafin suka gaisa ta shige ciki kai tsaye.

Ko ena shiru ne sai ta haura site din ta,
tayi zaman kusan 30 minut tana murmushin karfin hali tana kallon dakin nata,
cikin ranta tace i missed the old jasmine ,don yanzun kwata kwata ba ita bace, duk damuwa ya cinye wannan..
Sai Ta sa hannu ta bude drawer ta ta dauki diaryn ta tana karantawa
anan hawaye da murmushi ya soma sauko mata lokaci guda

don kuwa tsantsar soyayyan da take ma yaya ash din ta ne aciki tun ma lokacin baisan da hakan ba.

Har Ta ajiye diaryn tana dan dariyar farin ciki tare da goge tears din ta "wani sabon miiikin son shi ne ya dada tsatsafowa a zuciyan ta lokaci guda taji ena ma ace zata gansa.

sai ta tashi ta yi kofar dakin sa ta dan murda taji gam gam a kulle ,cikin dan karamin numfashi ta maida bayan ta jikin kofar ta jingina tare da lumshe ido,a hankali
Tace ,yaya na ya kyale ni.

Bayan kamar 5 min da haka sai ta kama hanya domin ta je itama tayi feeling ammyn ta
A ganin ta ammy ne kawai bata taba barin rayuwar ta ba har sai da ta mutu,

Nan ta haura a sanyaye ta sa hannu a handle din kofar da niyyan ji ko a kulle ne shima.

Da mamakin ta tana tabawa ya budu a hankali
Ba tare da yayi wani kara ba alaman ba wani kullewa akayi ba dama

Sanye yake da light and cool orange riga armless
Da wando baki wanda shi ba three gtr ba shi ba boxers ba.

Duk da idon sa ba abude bane
sai ta kure sa da nata idon tana murmushi mai dauke da hawaye.

Yana jin komai sarai amma jira yake yaji kamal yayi magana don shi kadai ne yake zuwa masa hakan

Jin shiru ya sa shi ma juya mata baya,

Nan Ta sake kofar ta soma tahowa a hankali daf da shi ta zo ta zauna tana bin bayan sa da ido.

Qamshin turare na daban da karin bugu a zuciyan sa ya sashi cikin rudani da mamaki, bai hankara ba yaji soft hand din ta cikin suman kanshi tana shafawa kadan kamar bazata yi ba

Sai ya lumshe ido sosai yace ya Allah, kar kabari wannan ya zame min wani mafarkin ,

Jin hakan yasa Ta dada yin murmushi mai sauti sai ya juyo da sauri a dan firgice

Suna hada ido da shi sai ta fada kan kirjin sa ta fashe da wani fitinnanen kuka..

ya kankame ta dam kamar ance mai za'a kwace masa ita ,

Sun kai 15 mint ,hankalin sa na dada tashi don jin sautin kukan nata

da kyar ya dago ta cikin kulawa da kallon so yace" jasmine ?
What happen, waya taba min ke ne?
wani abun aka miki gaya min mana koma waye ne ni zan rama miiki.
.
Ta dan ja fuskan ta daga rikon da yayi masa ta kai masa duka cikin fushi a kirjin sa,
Cikin kukan da yafi kama da shagwaba tayi nuni da shi fuskan a kwabe da hawayen masifa tace ba kai bane ka shareni,

sai ta cigaba tana yi tana jan zuciya tace, wai ko ka gaji da so na ne?
u left me all alone kwana nawa baka zo ba wannan adalci ne,? ta sake kai hannu zata maka masa sai ya riko hannun bata fasa ba ta cigaba tana cewa' ena ka shiga ka barni , u better explain to me don ni nagaji.

Ya dada kure ta da ido hannun ta damke a cikin nashi baice komai ba yana dai kallon ta tana bare baki,,

sai ta sukuyar da kai murya a sanyaye cikin kukan tace
kayi hakuri mana yaya
Ko don nayi maka laifi ne ..nasan nayi kuskuren taba babyn mu but i dont mean to hurt u,..i love u.


Lokacin idon sa sun gama kawo ruwa Sai ya jawo ta jikin sa baki daya ,ya shiga rarrashin ta ahankali yana bin tears din ta da kiss har ta sassauta kukan nata

Duk idon sa sun ciko sosai amma sai ya cigaba da dauriya yayi yunkuri ya jawo ta kan gadon ya ajiye ta gefen hannun haggun sa suna fuskantar juna,

Yana kallon ta tana kallon sa suna maida numfashi ,ya kai hanu yana shafa fuskan ta in a cooling and soothing way,duk ta sakalce masa fuska

Sai ya riko hannun ta a hankali yayi whispering lightly yace, ure so beautiful wify.
Sai kamo hannun nasa dake yawo a fuskan ta dan yi kissing

Yace ,jasmine meyasa kika zo nan?akwai matsala ne

Tayi shiru sai da ta dawo daf kan kirjin sa ta shige ciki da kyau tukunna nan ta soma fada masa duk abubuwan da suke mata ciwo.

Tun Daga ranar da tayi abortion,fadar su da salma da dai duk abunda ya faru harta maganan iyayen ta da taji wajen mamy sai da ta gaya masa cikin kuka..

Shikan sa bai hana hawayen sa sauka ba sabida ya san she is too young to bear All dis pain..
"
Ya dada rungemeta yace kiyi shiru abun ki, duk ba laifin ki bane princess,
C'mon dont cry anymore baga ni nan ba?

Yace its tru,naji zafin rasa babyn mu kam amma bana fushi da ke,everything u did is justified dukkan mu bamu miki adalci ba..

Ya dago ta a hankali tana fuskan tar sa yace,jasmine wont you ask me?ko baki so kiji me zan fada mikin ne har yanzu,

ta sunkuyar da kai kasa ,ta dan murguda masa baki tace ba nayi ta neman ka ko ena kaki zuwa ba ai bazan jin ba,,ta karashe da kukkuni mai ban dariya

Sai yanzun ya tabbatar lallai tayi fushi rashin zuwan nasa kwana biyu, anan sai ya saukake muryan za yace kiyi hakuri ,u know that zubar hawayen ki na mugun min ciwo ,kinga kuma duk ranar da naje gidan mamy sai mun saki kuka gaskiya bana son haka,

Sannan bawai bana son nazo bane nafiso ne mamy ta dan sauko sai na zo sake rokon ta, nasan fushi kawai tayi dani kuma duk laifi na ne.


Nan tayi shiru ba tace komai ba daga baya ta dago kai tace , yaya, meyasa kace kana so na amma babyn mu ya dawo biggest mistake din ka, ?nifa bazan hanaka auren ka ba, but pls tell me why, abun yamin zafi sosai...sai Ta dada sauke masa hawaye masu zafi


Ganin haka Duk sai ya birkice ya rasa ta ena zai fara, karshe sai ya zaunar da ita kan gadon shima ya zauna a gaban ta sai ya shiga bata labarin rayuwar sa tun daga ranar da lailan sa ta mutu,sannan ya gaya wacece zahida a wajen sa'
Da duk abubuwan da ya fuskan ta har ya hadu da ammy,

Duk da ma ba komai da komai ya fada mata ba ,musamman shirin su da kamal don baya so ya sake sa rayuwan ta a wani hidima.

Amma sai yayi kokari wajen wayar mata da akai akan rodriquez sune asalin familyn sa, yace jasmine zahida is just fake a rayuwar mu babu ita a zuciya na ke kadai ce.
ko soyayan gaskiya babu a tsakani na da ita bare aure,
Muguwa ce, kuma gaskiya Tsoro kawai nake ji karta taba min ke da babyn mu kamar yadda tayi ma twin sis dina lailah.
I just can't lose u...na gwammaci na fada miki koma miye ne in har zata rabu dake fatan kin fahimce ni?

Tana shiru ta kafe sa da ido

Sai Ya gyara position dinsa ya sa gwiwan sa akan gadon a gaban ta ya rike kunne hannu bibbiyu,tare da marairacewa yace jasmine kiyi hakuri dan Allah walhy ena kaunar ki ,ke kadai nataba so a rayuwa ta,..

i know im the bad guy now, kuma nasan kinyi hakuri sosai wify, im sooo sory dana saki a matsala kala kala saboda matsala na da sister na ..ki yafe min kinji?

Ya dan matso guntun tears gaban ta yayi zugum kamar wanda yaci kudin aika

Har yanzu ta tsaya tana binsa da kallo cikin wani yanayin shock, she just cant believe her ears,

Cikin ranta tace yanzu dama zahida is all fake a rayuwan sa,?

Sai Ta kalle sa da kyau ta da kallon sa dan karamin hawayen ta ne suka dada sauka.
sai ta daure fuska ta juya masa baya ta ja jikin ta kadan daga enda yake.

Nan kirjin sa ta buga A hargitse ya kai hannu yana binta zai juyo ta yace na shiga uku jasmine kar kiyi fushi mana im sorry,baki da lpya ne amma naso na gaya miki tun tuni "kiyi hakuri

Cikin borin da gangan ta ma koma chan gefen gado ta sauke kafafun ta a kasa ta barshi a tsakiya bata ko tanka amsa ba.

Lokacin duk ya gama rudewa ya damu sai ya gama sawa aran sa zata ce bata yarda ba

sai Ya sauko shima a hujajan ta site din fa,, tana ji har ya iso ta gaban ta ya sake sa gwiwan sa a kasa
suna hada ido ta wani sa masa fuskan bori mai dauke da shagwaba,

Shiko ya kawo hannun sa again yana cewa wify ..sai ta kama hannun ta dan mutsine shi cikin yanayin masifa tace ka sake kawo wa i will pinch u again

Looking very seriuos kalar tausayi yace,no, kar kiyi pinchinh dina nasan bazai min zafi sosai ba,u can punch mebif u want'ya dada sakankance wa yace punch me baby, kimin mai zafi ma in kina so duk na yarda ...


Har cikin ranta yadda ya marairace ya sukurkuce mata akan tayi masa komai indai zata hucen Sai abun ya bata dariya ,


dama tun yana gama bata labarin taji kamar an yaye mata wani gundumemen dutse a kirjin ta,
she just still cant believe dat ita kadai ce a rayuwar sa har yanzu don taji dadi sosai marar misaltuwa

Yau Rana ne wanda bata taba tsammanin ko a mafarki zai zo mata ba.amma don son taga drama shine take bashi attitude shina ya taba yaji

Yana kan gwiwar sa duk hankalin sa ya gama tashi ,sai rawan jiki yake

Sai ta dawo Ta daure fuska sosai, yanayi yana satan kallon ta yan dukar da kai kamar muminin almajiri ya cigaba da cewa,say sumthing pls zanyi kuka fa.

Kan ya sake fadan wani ta dauko pilow ta maka masa "ganin ta danyi murmushi ya sa ya biye mata shima nan suka balle da wasa da pillows din kan gadon kaf sai da suka hargitsa dakin da dariya tana biyo sa tana jefa masa in ya kare sai ya soma mayar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login