Showing 36001 words to 39000 words out of 219669 words

Chapter 13 - So Makamin Cuta Complete Hausa Novels Compelet By Surayyams.txt

14 Mar 2026

4135

a sanyaye yace
Ammy?
Kinyi fushi dani ko? Nasan na bata miki rai jiya am so sorry
Dan Allah ki yafe min,kawai rai na ne ya baci.i don't mean to talk to yhu like dat ya dukar da kansa kasa qwanin tausayi

Wani sanyi taji aranta don hakan na daya daga cikin halayen sa data ke so ,baida girman kai musamman wajen bada hakuri inyayi kuskure,take ta sake karamin murmushi tace
No my prince u have everyright kayi fushi,
Dama ena son magana da ku duka amma sai kadawo daga office

Ba tantama yace" Tohm ammy ..sai na dawo yakarasa tare da mikewa
Kallo kawai ta bishi da shi har ya bace ,sannan ta cigaba da abunda takeyi

Wajajen karfe sha biyu saura, bakin da suka zo mata suka soma kama hanyar tafiya ..

Gefen jasmine kuwa tun safe ta kasa tsaye ta kasa tsugune burinta ta samu ta ba ammy hakuri,
Amma bata samu dama ba har yanzu
Koda ta je gaisheta already likitan ta ta tarar don haka bata iya bada hakuri ba sai kawai ta gaishe su ta fice,

Ganin fitar ammyn da bakin nata kawai tayi
Amma bata lura da dawowar ta ba

Kusan minti 15 tana lekawa chan ta yanke hukuncin saukowa kawai ta jira ta..
Tana kaiwa hannun step na kusa da karshe daga oart din ta taci karo da kyakkywar fuskan da yamata kamar bata taba gani ba,jikin ta dai ya bata ba yau ta soma ganin ta ba amma sai ta rakube gefe tana lekowa

' ji kawai tayi matar tace
Sunana zahidah,
Nazo wajen Ashween ne"yana ciki kuwa?

Wani Dum taji a zuciyar ta
A hankali ta dada ja gefe ta labe
Tanajin su da kyau,

Lpya lpya ammy ta karbe ta da fara'ah, har suka danyi hira kadan

Budar bakin zahida tace" dama na sha cewa ya kawo ni na gaishe ki amma yaki,
I hope zaki bani dama nazo wata rana ?ammy tace
Bakomai yata , yanzun ma im gratefl, tace atakaice
Murmushi zahida tayi tace
Toh ni zan wuce tunda baiya nan
Dama kwana biyu muna yawan sabani ne shine nace bari na duba sa a gida,

Ayyah ,na gode zan gaya masa sako,.ki gaida gida

Sukayi sallama zahida ta wuce abunta,

Da gudu ta haura chan sama donta kare mata kallo da kyau ko xata ga wani abun aibu ajikin ta amma sam bata gani ba

Sai ma wata mikakkiyar motar dataga ta bude ta lume ciki'hmm zahida taji kudi ba karya

Wajen ta sulale kasa zuciyan ta kamr zai fashe ,amma ta kasa gane na meye ne guda daya
Tuno fuskan zahida kawai yasa ta jin wani mummuman haushin kanta,

Yo meye zaiyi dani in wayayann matan na binsa .ai dole ya dubi tsaban idona yace ma yaya ashraf wawa marar taste don yace yana so na"
Hmmm wato wanda ya ke nema na kenan baida taste...hmmm.tafada a fusace

Koda ta fito ganin lumewar ammyn tayo
Nan ta kama hanya zata bi bayanta amma jitayi an damke hannun ta gam
Saida ta tsorata

A gagauwce ta fauce tare da cewa meye haka yaya ashraf
Ya zaka shigo mana ba sallama and what are yhu doing here?

Ko ajikin sa sai kallon lips dinta yake yadda take motsasu fuskan ta dauke da tsoro
Ga Idonta sun fififto gwanin sha'awa
' hannu ya sake kaiwa ya damko ta da karfi
Yace nagaya miki wani abu jasmine?wallhy kinfi kyuw a haka
Next time in zanzo haka zAki na fitowa baby na

" wani haushi ne ya tokare ta a wuya Iya karfin ta ta sa tana kokarin zare hannun ta amma dam ya rike so
Shi dai damuwar sa yadda boobs dinta ke motsawa cikin rigan ta inta yi yunkuri.
Ka sakeni nace me haka ne wai yaya ashraf tafada a tsawace alaman ranta ya mugun baci

Amma ko ajinkin sa sai wani annoying smile daya sa kan fuskan sa
' cikin muryan kirsa yace
Why are you not picking my calls yana dada janta kamar zAi hade bakin su waje daya.. . Haba jasmine kinsan bana iya baci banji ki ba
Kinga kuwa dole nazo uhnm" oya kiss me tunda naga lpyar ki"
In bahaka ba bazan sake ki ba

Kafin tace zata budi baki tayi magana
Ji tayi muryan ammy tace' jasmine? Me nake gani haka

Da sauri ya sake ta ya dukar da kai kasa yana sosa keyan sa cikin jin kunya

Wuce ki bar nan..bana son shashanci
Ba musu ta wuce sum sum ta haura sama
Wani takaici ne ya rufeta har bata ganin Gabanta tsaban bacin rai

" fada sosai ammy ta masa sannan tace masa kar ya sake zuwa kofar gidan nan sai ta neme sa
Da kanta ,

Jin an bude kofar dakin ta ya sa ta jin wani dum a ranta don a tsorace take
Koda ba ce ba tasan ammyn Ne ta shigo
'
Sauri tayi ta sulale kasa tana mutsu mutsu takasa magana
Da mamakin ta ,jitayi ammyn tace toh
Ni zan fita,
Saura naji kema kinsa kafa kin bar gidan nan jasmine.
Kaiwa nan ta fuce bata jira wani amsa ba,

Nan ta wuni tana juye juye aranta
Ga salma bata daga waya tun jiya itama ta share ta,
Karshe ma ' kashe wayarta tayi don yaya ashraf baiko ji gizau da abunda ya faru ba
Damuwar sa ma ta bashi dama ya kara zuwa hira ko a sace ne.
'
Haka ta zauna jiki ba kwari har kusan tara na dare talatu ta shigo ta ce mata ammy na son ganin ta,

Ba musu ta mike ta janyo hijabi,ta nufi dakin
Isarta bakin kofa keda wuya
Taji lokacin da ammmy. Take cewa nifa ka gaya min gaskiya ashween indai hankalin ka ya daidaita da yarinyar nan ayi ayi kowa ya huta,

" ammy nifa bance miki aure nake so ba fa
Kuma ni ai bani nace miki akwai wani abu tsakanina da ita ba

To sai me?ai ita tafada min
Kaga banson wani shahshanci idan na bincika na gano wallhy cikin satin nan zan daura maka aure like it or not
Ta fada fuskanta a damke

Dan shiruuu yayi daga baya yace
Toh kiyi hakuri ammy,.ure right am dating her amma dan Allah kar kice na aure ta yanzu wallhhy im not ready.....
Toh ya isa ,amma dai ene zaka auretan?
Da kyar ya amsa da cewa eh..
tace
Gud

Buuut jasmine ta shigo dakin fuskan ta ba alaman rahma,
Kallon da suka bita da shi ya sa ta shiga hankalin ta ta rusuna
Murya a sanyaye tace salam alaikum.

Kowa da yanayin Yadda ya amsa mata sannan
Ta nemi waje ta zauna

Batare da bata lokaci ba ammy tace
Dama na kira ku nan ne dan na riga na gama tunani na yanke hukunci
' ashween kayi kokari ka nitsar da kanka waje daya
Na riga nagama magana ta dakai kenan

Ke kuma tunda na lura auren kike so dan haka, zan yi magana da hadiza asan me ake ciki kowa ya zauna lpya.. Ta dube su tace wanda yake da magana ena jin sa

Wani tokarraren bakin ciki ne ya durmuye su duka amma kowa sai ya fiske'
" a dabaran ce ta sauke ajiyan zuciya
Tace" ammy
Kina nufin yaya ashraf zan aura?

Eh ..shi din fa?

Amma ammy ..ammy...sai ta kasa cewa komai..
Ta sun kuyar da kai kasa..

Ko ajikin qmmy sai dagowa ma tayi ta dubeta
Naga dai shi kike so ko ba haka bane?

Wani kallon da ashween yamata na wulankanci da haushi ya sata furta

eh,ammy
Batare da tasani ba


.....ko jira baiyi an sake cewa komai ba, ya mike ya karaso daf jikin ammy ya mata light peg kamar ba abunda ke damun Sa ya ce gudnite ammy
Insha Allah zan miki duk abunda kike so...i promise

Fadan hakan yasa boyayayen hawayen ta suka zubo tayi saurin share su

Ammy kuwa tace Allah ya maka albarka son
Sai da sfe

Ya wuce ya tafu abunsa..

Shiru ne ya ratsa wajn dakyar ta da matso kusa da ammyn ta zuba gwiwarta akasa
Tace
Nasan kina fushi dani ammy na pls forgive me..ta karashee cikin kuka da tuntuni dama yinshi take a boye

Sosai ta ba ammyn tausayi don tagama lura da ita tuntuni abun na cin ta arai fiye da misali ta dube taa tace
' ba kiji ne jasmine
Bansan yaushe kika fara ba."

Wallhy na dena ,bazan sake ba ..,dan Allah ammy karki min aure ni makaranta nake so

Shiru ammyn ta mata kamr bataji ba ..nan ta cigaba da kukan ta tana kan bada baki
Ciki har da cewa ita bata son yaya ashraf kawai gwadawa takeyi..duk bata san ma ta furta su ba
Saida tayi ta gaji tayi shiru kafin ammyn ta mata nuni da bayi
Jeki wanke fuska kixo

Ba musu ta mike ta wanke fuskan ta
" gefe ta zauna
Ammy ta dago ta kalleta cikin nitsuwa tace
Jasmine Kunyi fada da yayan ki ne?
Da tayi niyyar boye wa saita tuna yanzun nan ta gama daukr alkwariin bazata na karya ma ammyn ba nan tace
' shi ne wai dan na masa happpy bufday ya ...ya...wulakanta ni.

Wulaknci?.uhm uhm jasmine akwai dai abunda kikayi ba wannan kadai ba

Dan shiru tayi daga baya tace
Cewa yayi na shiga masa daki
Da tarkacen saurayii na

Hm,Ok kin kai masa wani abu ne?
Uhmm tace a kunyace,

hmmm to shikenan,
Nan ta mata nasiha sosai akan abunda yafaru tsakanin ta ashraf din "sannan ta ce mata taje tayi tunani,.duk abunda ta zaba shi za'ayi mata
Da haka suka rabu jasmine ta nufi dakin ta


Tun daga ranar ya zama kamar an huro wutar fitina a zuciyar ashween haushi take basa tunda ta amsa tana son ashraf agaban ammy don haka ma ya yanke baya shiga damuwar ta
Yanzun Sosai ya sake yana harkan rayuwar sa da zahida baiya ko boyewa kamr da chan
Sau dayawa yakan ba ammy waya su gaisa
Wani lokaci har ya kawo ta gidan

Tun jasmine tana kishin abun har ta soma danne zuciyarta itama ta sake
Ta fara bada kulawa ma soyyayar su da yay ashraf
Sai dai basu haduwa don sam ammy ta masa katanga da zuwa hira wajen jasmine
"
Kwanaki na ja jasmine Sosai tayi rama cikin dan kwana biyun don aganin ta ashween ya riga ya kufce mata kenan har abada
" musamman inta tuno zahida ga kywu,ga kudi da aji,sai taji wani shaukin son ta cire duk wani digon son ashween aranta
Hakan yasa ko zahida ta zo gidan sau dari ne bata fita,haka ma cikin su ammy ba wanda ya kula ya ce ta fito
Don tuni ammy ta fahimce komai game dasu amma sai ta zuba musu ido kowa ta kyalesu ...

Shiru shiru salma ba labari yasa jasmine dada shiga damuwa,
Yau kusan wata biyu kenan
Komai ya lafa mata ,alhamdullhi yanzu wani abun bataji aranta game da shi
Gaba daya ta mika almarin ta ga ubangiji...sai ya zamo ma bata kaunar ganin sa duk iya kokari tanayi kar ma su hadu tagan sa

Ji takeyi ena ma ace son data ke masa ya koma kiyayyya.. Kullum tana gode ma Allah a ganin ta tunda baisan tana son shi bama komai ya zo da sauki

" Shiko ya kasa fahimtar ta musamman data biye masa itama tana boye kanta
Amma sai yayi tunanin yaranta ne kawai ke damunta
Hakan yasa sai yayi kamar bai masan ta nayi ba .

duk da abun na damun sa sosai amma ko sau daya bai taba nuna mata ba
Sai ma dada jan jikin sa yake yana dulmuyar da ita akan cewa eh da gaske ne baya yin ta ..
Tsawon wata uku kenan ba abunda ya zanca..




Exams over👅👯🏻‍♀



*surriem*
[23/08, 03:02] ‪+234 806 071 2446‬: *⚜BRILLIANT WRITERS ASSO🖊*



💔

*SO MAKAMIN CUTA*
_'the sword of evil love'_


_Story and written by_
*SURAYYAHMS*🔥



*DEDICATED TO-*@UMMERHERNY NERSALLAH.

*Allah ka kare mana yan uwa musulmai a duk enda suke,ka kuma bi kadin wayanda aka zalunta a hanyar jos,ya ubangiji ka saka mana😪😪😪*




*Page▶14*




Ashween ne Zaune a asibiti kamar da gaske
Kamal ya tinkaro sa
Yana dariya ciki ciki kamar munafiki ya sai yazo ya tsuguna daf

' daure fuska ashween yayi ya kau da kansa
Wanda ya dada sa kamal fashewa da dariya,

Da Allah ni ka kyale ni,banson iskanci fa
Ya fada a fusace

Ok calm down ..mr zahida rod
Wallhy dramar ce take bani dariya
Lallai yarinyar nan yar iska ce ji enda tayi lumui ta kwantaa asibiti ta hanaka motsi? Hmm

Mswwww kayi na kudin ka fa kamal,
Itama Ba barin ta nayi ba ta san hali na sarai,so nake ta sa hannu akan wancan abun dana fada maka shiyasa kaga ena bata lokaci na anan din im so tired..yafada sounding serious

Ka kara hakuri kamal ya dafa shi ..fuska ba yabo ba fallasa
Ya labarin ita madam hidayat din? Yaushe xata dawo daga china?

Ashween yace, In four weeks time,amma kafin nan insha Allahu na kammala komai sai dai next plan
Gyada kai kamal yayi yace " insha Allahu roh
Barinje na duba babyn namu ....ya mike ya shige cikin room din yana dariyar tsokana

Zahida dake kallon karasowar su ta glass din kofar Kifi kifi ta so mayi da ido ,tana nishin karya "shiko kamal sauya fiska yayi ya dube ya yace
Sannu zahida luv ,.hw r u feeling now?
Tace, Fine ,sai yanzu kake zuwa ko ai ka kywta

Dan tabe fuska yyi yanayin tsokana yace " so kike ki hada mu biyu ki nakasa..abokina fa har ya rame pls get well mana kar shima fa ya kwantaa
Dariya tayi cike da jin dadin maganan
Amma sai ta marairace fuska tana duban sa
" bayan sai nayita ihu anan kafin yazo kusa dani,.ash is so lazy kamal.. ta karashe a shagwabe...

Ashween Murmushi kawai yayi baice komai ba,
Don shi ya san me take nufi,. Amma ya riga yayi alkwari har ya mutu ba abunda zaisa wani abu mai kama da romance ya shiga tsakanin sa da ita...ko da kiss ne

Hmm karki damu kamal yace
Ki warke kawai..kinji?
Kamar baby haka ta gyada kai
Jefa jefa suna hira,har suka watse

Gefe guda bangeren asibitin
Ammy ne zaune a counseling room tare da doc
" zugum tayi
Bayan ta kammala karanta sakamakon gwajin ta
Kallon nitsuwa doc ta mata sannan ta ce
Kinada sauran lokaci hajiya shahida
Kar ki manta farincikin ki is important a wannan stage din
Kiyi kokari kibi kai'dojin maganin dana kara miki yanzu in akayo haka ba matsala insha Allahu

Murmushin karfin hali ammy tayi tace
Hakane doc,kullum kina fadan haka karki damu insha Allah zAn yi kokari

Dan shiru doc tayi...daga baya tace tun da nake bantaba ganin mace mai karfin zuciya kamr ki ba hajiya,
Sau dayawa mutane masu dauke da brain tumour ke qarar da rayuwar su ta hanyar damuwa da kunci tun kafin ciwon ya yi halinsa
Amma ke kam sabanin haka ne ,,na miki murna

Murmushi kawai tayi ta ce" nagode kwarai ..kema ai kina iya bakin kokarin ki Allah dai ya saka miki da alkahiri..

Bakomai hjy en akwai matsala a kirani anytime

Insha Allahu ..Sai anjima sukayyi sallam ta wuce gida


Tun daga ranar ammy ke kokarin danne zuciyar ta
Amma ena waNi bin damuwa da tunani na cin karfin ta tasan mutuwar ta yazo ba shakka
Kullum tunanin ta rayuwar ashween da jasmine
Musamman Da yanzu ta lura ko maganan ma ba sosai sukeyi ba.

Kwana na tafiya kullum tana dada kirga ranakun ta ne ,..don likita ya tabbatar mata tana mataki na karshe

Amma Haka take daurewa ta danne duk wani alama ,.tana cin abinci ta tana shan maganin ta amma duk a boye ba wanda ya lura da halin da take ciki

Bangaren su zahida kuma Yau kusan sati guda kenan media tana news akan familyn madam hidayat wanda mafi aka sari sun samu tallafawar kara bude ido ne ta wajen ashween, yanzu haka jabir ne zaiyi wani gagarumin concert na tallafawa yan mata wanda basu da galihu karkashin wani companyn kamal...

Daga gidan hajiya hadiza kuwa ashraf tsungune yayi kansa kasa yana kukkuni
"Mamy amma wannan ba adalci bane
Ni banga wani abun jira anan ba ,kawai dai ana neman a hanani yarinya

Yi min shiru da Allah'
Toh ai sai kayi tayi, sau nawa zan kira jasmine din baki da baki tace min ita bata muradin auren ka,ta nuna sa da dan yatsa tace ashraf
Kaine kake tilasta ta,


Wani cunkusashhen bacin rai ne ya durmuye sa amma sai ya danne zuciyan sa don hargowa take kamar zata fashe nana ya sake cewa" Mamy ai dama basai tana so ba ,ke fa yar uwan ammyn ta ne. kawai ni in za'a bani kawai a bani....

Wani mugun kallo ta bisa da shi ta ce
Lahhhhh ta dafe kirji
" zaka mata na dole ne ,? Toh bisimillhi

Amma dai Kar ka manta idan jasmine ba amince ba na tabbata hajiya shahida babu abunda zatayi akai..gwara ma ka saukaka rashin kunyar dake damun ka kaje chan in kun shirya da ita to sai kazo min da magana ni ba ruwana da iskanci
Bude baki yayi zaice wani abun ta dakatar da shi dacewa tashi,oya. .oya ..fice min naga wuri
Bai ce komai ba "Sum sum ya wuce waje rai a bace ai kuwa
Bai tsaya ko ena ba sai gidan su jazmine din

Sosai ta sha Mamakin ganin sa don kuwa ta san rabon sa da zuwa yakai 3 months kenan yau

Lpya kuwa ?
Ta fada tana dan tura sa waje kar wani ya hango su
Bankade hannun ta yayi yace" Ai dole zAki min wannan tambayar?jasmine Ashe ke munafuka ce

Cikin mamaki tace ni

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login