Showing 177001 words to 180000 words out of 253142 words

Chapter 60 - ABOKIN RAYUWA Hausa Novels by Khadeeja Candy.doc

23 Nov 2025

18430

kusa da shi, sai kuma na fahimci daga nesa ya fi kyaun kallo, duk yakin da nake na samun kwanciyar hankali ne"

"Kar idonki ya rufe ki aikata abun da za ki sake dawowa kina nadama, ni dai bana nufin komai a gareki sai alheri, ina son na same miki wani tsanin hawa ne a duk lokacin da kasar da kike taku ta yi miki zafi, ina son na zama wata igiya da zaki rika ki cimma burikanki, na so na zama kamar uba ko dan'uwa a gareki a duk lokacin da ruwan sama ya sauka akanki, na so in kasance wanda zai kawo miki laima, a duk Lokacin da hawaye suka zubo daga idonki, na so in kasance wanda zai share su, a duk Lokacin da kika ji kadaici na so in kasance wanda zai rarrashe ranki kuma ya kwantar da zuciyarki..."

"Na gode amman ni a yanzu bana da bukatar ABOKIN RAYUWA, ko wane iri ne na nesa ko na kusa, zan nisanci kowa zan rayu kamar yadda aka bar ni, har zuwa lokacin da da rayuwar ita ma zata gaji da ni ta bar ni.. Sai wata rana Aliyu..."

Aliyu ya lumshe idonsa yana jin kamar ya sauka kan gadon, ina ma ace tana kusa da shi a yanzu ya kwantar mata da hankali...

"Wata ranar da bata da rana..."

Ta sake maimaitawa sannan ta katse kiran ta cire dankunnenta ta juya wayar ta cire layin ta saka a bakinta ta tauna har ta raba shi biyu ta jefar a gurin, sannan ta mike tsaye ta fara tafiya sai da ta fita kwararon sannan ta jefar da wayar.





ALIYU POV.

"Emily..."

Ya furta a hankali idonsa a lumshe, kamin ya bude idon ya sake gwada number wayarta sai ya jita a kashe. Tun da yake a rayuwarsa be taba jin tausayin wani yadda ya ji tausayin Emily a yanzu ba, duk halin da take shiga be taba jin tausayinta irin tausayin da ya rasa ma'aunin dora shi balle ya auna ba irin yau. Emily ta wahala har a yanzu bata samu gatan daya dace ta samu ba, gashi kuma abu ta dade tana nema ya zo mata a Saragurbi, da wanne zata ji? Be samu amsar tambayarsa ba, daya daga cikin masu tsoronsa ya kwankwasa ya leko kofar dakin ya sanar masa wai wani Turhan yana son ganinsa.

"Ce ya shigo"

Aliyu ya fada ba tare da ya kalli kofar ba ma balle kuma mutumen dake tsaye yana sanar masa isowar Turhan. After 3 min Turhan ya turo kofar dakin ya shigo cikin takun sarauta da da martaba. Sai da ya karewa dakin kallo kaf sannan ya kalli Aliyu.

"Na biyo sawun Aisha, sai Ummi ta fada min ta bata, wai nemanta suke... Na yi kyautata zaton tana nan ko kusa da nan, zuwan kuma ba na iya nemanta ne kawai ba har da na gargadi"

"Da nine kai, ba zan taba bibiyar matar da na nake ganin ba ajina ba ce, ba zan taba bibiyar matar da na rusa mata ragowar farinciki ba, ban ga dalilin da zai saka na yi amai kuma na bibiyi aman na lasa ba, kazanta ai ta kazanta"

Aliyu ya fada ba tare da ya kalleshi ba.

"Toh ai ba ni ne kai ba Aliyu, ban iya cin amana ba"

"Har abada, Turhan ba sai taba zama kamar Aliyu ba, namiji yana cika namiji ne da karfin tunana da hakuri da adalci da kyautata, ba da izza ko nuna isa ba, da kai wani mai wayo ne tun a lokacin da mahaifiyarka ta yi maka kyauta da ka riketa da hakuri wata kila da duk ba mu kawo a wannan ba"

"Turhan ya fi karfin Aliyu, shiyasa Aliyu ba zai taba zama kamar Turhan ba, ta ko'ina na damaka na shanye Aliyu"

Aliyu ya juya ya kalleshi.

"Da ko wace dakika idan na yi maganarka Emily rokon take na boye maka sirrin saninta, saboda tana jin zaka rusa ragowar farincikinta, da ko wane numfashi idan na tuna na boye maka sai na ji cewar ban kyauta ba, daga lokacin da ka gane gaskiya sai na gagara samun salama na abun da nake zaton cin amana ce na aikata, amman a yau na gane abun da na aikata daidaine, na fahimci karatun da Emily take karanta min a yanzu biye da lokacin da take min bitarsa, yanzu a haka sai ka kira kanka namiji? Ka cutar da yarinyar iyakar cutarwa ta raini yarta da dadi babu dadi har ta yi wayo, rana daya ja dira a rayuwarta ka raba ta da yarinyar da ita kadaice ta rage farincikinta? A haka kuma kake neman yafiyarta? Wallahi....! Da ace zan iya sake rubuta farkon faruwar wasu abubuwa da na goge shafinku a tarihin rayuwar Emily...! Zaka gane kana sonta kawai idan ka rasa ta, kuma ka rasata...!"

"Ka iya bakinka, karka sake ka sake aikata kuskuren tsoma kanka ko bakinka a tsakanina da Aisha, balle kuma ka sako zancen yata, kuma babu kai babu Aisha babu Fatima daga yau, kallon matata ma karka sake yi, na san inda ka dosa ai, shiyasa kake zugata kake hore mata kunne kuma ka boye gaskiyar komai har sai da matarka ta gaji ta bayyana, ba kai babu Aisha daga yau, kaga dai kamar mutumen kirki mai tarbiya ashe dai kura ce lullube da fatar akuya, tirrr da kai... "

Turhan ya juya, sai Aliyu ya gyara zamansa.

"La la lala Aliyu. Bari na fada maka wani abun da baka sani ba, a lokacin da Emily zata haifi Fatima ni na dauke ta da hannuna na saka ta a mota na kaita asibiti, gurin aikinmu daya da ita, Fatima ta shaku da ni fiye da kai, na san ciki da wajen na halin Emily fiye da kai, babu abun da bata fada min ba na zamantakewarku, a Part hartcour muke zaune dukanmu, a duk lokacin da na so ganinta ziyara kawai nake kai mata. Yanzu ina son ka je ka mutu..."

Turhan ya ji zuciyarsa kamar zata fado tsabar bakin ciki da kishi numfashinsa har daukewa yayi ya dawo. Turhan ya juyo

"Kana magana kamar wanda yayi nasara, Jarumi ne kai haka kake son na kira ka? Ko kuma na taba ma? Ka taba ganin wanda yayi cin amana yayi nasara? Ko yanzu kasuwa ta watse dan kwalli ya ci riba, Fatima bata da wani Uba sai Turhan, bata da wasu family sai nawa, har abada kuma alaka ba zata yanke tsakanina da Aisha ba, kuma zaka ga sakamakonka... Ko da yake kq fara gani ai, tun a gurin matarka, yanzu kuma gaka kwance a asibiti waya san mi zai biyo baya kuma..."

Ya dauke kai ya juya ya fice yana jin wani irin bakinciki da be taba ji ba irin yau, ba a taba fada masa magana mai daci kamar ta yau ba.



KAMEELA POV.

"Au baki ci abincin ba?"

Hajiya ta tambaya sannan ta zauna bakin gadon da Kameela take kwance jiki ba kwari domin ta kwaracewa komai tun a ranar da Aliyu ya sake ta, bata fahimci girman laifin data aikata ba sai sakin ya shiga tsakaninsu, sai dai kuma sakin ya kara tabbatar mata Aliyu yana son Emily domin ko a lokacin da ta saka masa guba be sake ta ba sai a yanzu dan kawai ta dauki yarta ta kai gurin ubanta, hakan ya kara karantar da ita cewar Aliyu yana son ya auri Emily ne ko kuma shedan ya ci karfinsa yana son ya shirya zaman banza da ita. A duk lokacin da ta yi yunkurin daukar waya ta kira Aliyu da nufin ba shi hakuri sai zuciyar ta ta tuna mata ya fifita wata banza ne akanta fa, bayan marinta da yayi har da saki a cikin gidan iyayenta, gashi kuma ita ma nata iyayen sun dauki zafi sosai kuma sun goyi bayan abun da ta aikata, har suna farincikin mutuwar auren, sai dai ita ta san abu ne mai wahala ta iya cigaba da rayuwa babu Aliyu a tare da ita.

Ta yi ta sauraren ko zai gane kuskuren abun da ya kamata mata ya dawo ya bata hakuri kuma ya gyara aurensu, sam a rayuwarta bata taba tunanin Aliyu zai iya furta kalmar saki a gareta ba, kuma abun abun bakincikin ma saboda wata karuwar banza. Bata gane rabuwa da wanda kake kauna bata da dadi ba sai a yanzu da igiyar aure daya ta warware tsakaninta da Aliyu, a yanzu ne ta fahimci ashe duk son da take masa a baya karya ce yanzu ne take ainahin kaunarsa, washe garin ranar da ya sake ta ma sai da ta yi kamar zata yi karamar hauka, kamar wata mai aljannu haka ta zame musu a gidan, ta hanyar ihunta ne Mama Barakat ta san abubuwan da suke faruwa...

"Ke kan dai Allah ya wadaran wannan hali na ki, wai anya Aliyun nan ba magani yayi miki ba kamin ya zo neman ki ma? Akanki aka fara saki ne? Ina ce ga yar uwarki nan damuwa kika ga ta yi? Sai ke? Sai kace Aliyu ne autan maza, toh bari kiji na fada miki ko ma dawowa yayi ba zaki taba komawa ba, aure tsakaninki da shi ya kare har abada, da ma ya sani saki uku yayi miki ba daya ba, sai mu san shi dan iska ne"

Kameela ta tashi zaune ta sauka daga kan gadon tana share hawayenta ta fice daga dakin kasa ta sauka ta fice daga bangaren na su gaba daya, ta nufi bangaren Mama Barakat domin acan ta san ta saba jin sanyi idan wani abu ya faru tsakaninta da Aliyu, ko ba komai Mama Barakat tana bata shawarar yadda zata bullowa lamarin, ba kamar mahaifiyarta da yar;uwanta dake kara bata abun ba. A lokacin da ta shiga falon Mama Barakat ta samu ita ma shigowarta kenan daga cikin gari idonta ya kumbura yayi ja kamar zai fashe. Mama Barakat na ganinta ta katsi hanzarinta.

"Dan Allah indai kin san kin zo ne saboda Aliyu to ki tashi ki koma bangarenku, ni ma ina da nawa tarin matsalolin a gabana, Emily ce kin riga kin yi nasara akanta to me ya rage kuma?"

"Wallahi har yanzu ban yi, amman dai zan yi, sai na ga bayan yarinyar nan, kuma na zan sake zuwa neman shawara a gurinki ba"

"Karki sake ki sake zagin Emily"

Kameela har ta juya ta juyo tabe da baki jin abun da Mama Barakat ta fada.

"Tohmmmm ko dai ta miki maganin ne ke ma?"

"Emily ?ata ce...!"

Kameela ta yi dariyar da bata shirya ba, ta rike kumkuru ta kara matsawa kusa da Mama Barakat.

"Eeehhhh? God Forbid Wallahi karya ne, to ta ina? A zaren ma ba kalar yadin ba ne, sai idan dai Lake lake dangin nepa, ko lake laken ne ma Wallahi babu kama, Mama Barakat ki ma daina alakanta kanki da watsan yar iskar yarinyar kafirar ba..."

Bata kai karshe ba Mama Barakat ta dauke fuskarta da mari.

"Fita daga falon nan"

Kameela ta juya da sauri ta fice daga falon babu shiri, domin da take da Mama Barakat bata taba ganin bacin ranta irin yau ba, gashi har ya kai ga ta mareta.

"Ahhh Ahhh ni fa duk ban gane wannan ba, anya shekarar nan ba so ake na haukace ba? To ta ina ma zata zama... Oh.... Hadin kai aka yi da Aliyu ko Ummi wai ni ake son durawa bakinciki"

Ta shiga bangarensu rike da fuska tana ta mamaki sai tunani take.
[7/21, 9:49/ PM] 5???5???5???5???5???5???5???5??? 5???5???5???5???5??: https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08?mode=r_t


*

*? Khadeeja Candy*



Page 5?? 6??


Tana jefar da wayar ta cigaba da tafiya, a yanzu ta yi giving up akan rayuwarta da duk wani abun da ya shafe ta, ta sha wahala iya wahala, daga karshe kuma burinta da mafarkin da take da shi ya rushe. Jin tsayawar motar bayanta be saka ta juyo ba har sai da ta ji an fisgota an juyo da ita da karfi. Wani mutum ta gani wanda bata sani ba, ya rike ta gam sai ga wasu maza biyu sun fito daga motar wacce ta kasance ta jigila ma'ana motar haya, dukansu suna sanye da kayan gida ne.

"Ke ce Emily?"

Dayan dake rike da ita ya tambaya, sai ta daga kai ko kadan babu tsoro ko faduwar gaba a tare da ita, domin a yanzu ta shirya ko da mutuwarce tana ra'ayin a mutuwar.

"Kina tare da wani a nan ne?"

Ta girgiza kai. Sai ya ciro wayarsa ya kira.

"Mun same ta"

Yana fadar hakan ya amsa da

"Okay Sir"

Sai ya kashe wayar.

"Su waye ku?"

"Jami'an farin kaya ne"

"Me aka ce na yi?"

Yayi shiru be ce mata uffan ba kuma be sake ta ba duk kuwa da irin kokarin da take na kwatar kanta. Sai da wayarsa ta sake ringing ya daga yayi magana.

"Abunda muke gani dai babu wani rauni ko matsala a tare da ita"

Ya saka Hands-free ya mika mata.

"Emily ki shiga mota za su taho da ke"

"Waye wannan?"

"Sunana Adam Bello"

"Dr A-B, suwaye dan nan me aka ce ana yi?"

"Baki yi komai ba, na kira baki daga ba, sai na sake kira na ji kina waya bayan kin fada min kina neman taimakona, shiyasa ni kuma na nemi taimakon Babana aka yi tracing dinki"

"Na nemi taimakonka a dazun saboda ina tunanin kamar ?wa?walwata ta tabu, amman yanzu na samu lafiya, bana son taimakon kowa bana son kowa kusa da ni"

"Emily ko da tsiya ko da arziki za su zo da ke, dan haka ki bada hadin kai su zo da ke ta arzikin zai fi"

Ya katse wayar, mutumen dake rike da ita ya sake ta ya nuna mata motar da suka shigo, ta nufi motar ta dayan ya shiga ta shiga dayan ya shiga aka saka ta tsakiya sannan guda ya shiga front seat direba yaja motar suka yi gaba.
Headquartersu suka tafi da ita suka bata guri mai kyau da abinci, bayan sun dauki Information dinta, amman ruwa kawai ta iya sha, shi ma saboda makoshinta yana bushewa ne, daman bata ci komai ba ya tafi gidansu Turhan.

Da dare yayi suka dauke ta daga nan suka sakata wata mota mai kyau da ac aka kaita gidan wani babban mutum, suka tarbe ta da hannu biyu a nan ma suka bata masauki mai kyau aka kawo mata abinci, shi ma ta kasa cin komai, bata raina kanta ba sai da dare yayi bachi yaki zuwa mata sai tunani gashi ta gagara kuka, gaba dayan rayuwarta sai da ta tuna shi a dare, yadda Khaleefa ya latsata ya yaudareta, zaman da ta yi gidansu, fitowarta haihuwar London, haduwarta da Ammy aurenta da Turhan zaman da ta yi a masarautarsu, dawowarta wahalar da ta sha da cikin Fatima, haduwarta da Vito yar rayuwar jindadin da ya bata mai hade da duka da kangin na zaba mata abokan mu'alama, haduwarta da Aliyu, mutuwar London, yadda ta rasa Fatima har zuwa yau da Fatima ta zabi ubanta sama da ita, wanda shi ya fi komai yi mata ciwo, da karya zuciyarta.

Ba'ayi wani dare da yafi kowane tsayi a idon Emily kamar wannan daren da bachi be rabi idonta ba, tunani be barta ba, kuma hawaye ba su ziyarce ta ba, kamin safe kanta ya cika yayi mata nauyi kamar wanda aka hurawa iska ciki, idonta ma sun yi nauyi sosai kana kallonta kasan bata samu runtsawa a daren ba. Misalin karfe takwas wata yarinya wacce ta fi kama da mai aiki ta shigo gidan ta ce mata ta shirya za a zo a dauke ta karfe 8:30, Emily ta daga mata kai kawai, babu jimawa yarinyar ta dawo ta kawo mata ruwan tea da kayan hada shayi sai bread.

"Na a gama hada abun karyawa ba, amman ki ci wannan saboda za ku tafi"

Nan ma Emily ta daga kai kawai, saboda bata son yawan magana ko musu, yarinyar ta fita Emily ta kalli kayan da aka kawo ta dauke kai har lokacin bata ji tana sha'awar cin wani abu ba, gaba daya bata jin yunwa cikin ya daure jikinta ne kawai take ji babu karfi sai kuma ciwon da kanta yake. Misalin karfe takwas da rabi yarinyar ta sake shigowa tace ance ta fito.
Emily ta mike tsaye ta bi bayan yarinyar suka fita tare, yarinyar ta rakata har harabar gida, har lokacin masu gidan masu farka ba, sai yan aiki ne suke ta kai da kawo.

Mutumen da ya kawo ta jiya ne ya dawo ya dauke ta a wata motar ta dabam ba wacan ba, sai da ta shiga cikin motar ta tarar da wani a mazaunin direba, dayan ya shiga front seat suka damka mata duk abun da ya kamata sannan suka nufi airport da ita, suna yin farkin a harabar airport din ta fashe da kuka tunawa da zata tafi ta bar yarta, idan akwai abun da take kauna a duniyar nan be wuce Fatima ba, saboda ita ce kadai sanyin idaniyarta, sai dai tunawa da ita kanta Fatimar bata bukatarta ya saka ta takaita kukanta ta share hawayenta ta duba ticket din hannunta. Da kanta ta bude motar ta fita mutanen suka mata rakiya har ciki, ba su bar gurin ba sai da jirginta ya daga zuwa Abuja, a jikin Window ta zauna ta jingina tana jin kamar jirgin ya juya ta koma ta dauko yarta ko da da karfi ne.





ALIYU POV.


Duk inda ake saka ran za a samu Emily kamar tasha ko unguwanin dake kusa da su, sai da Ummi ta aika aka bincika mata ana cigiya amman ba a samu ganinta ba, a nan hankalin Mama Barakat ya kara tashi ta sha kuka sosai kamin Ummi ta iya rarrashinta har ta samu karfin guiwar tafiya gidanta, daman yaranta tun gabanin ta yi magana da Ummi ta ce su tafi gida. Ummi bata samu tafiya Asibiti da safe ba sai aikawa ta yi aka kai masa abinci da tufafin da zai canja. Da dare ta dafa masa abun da ya fi so wato sinar da miyar kaza ta tafi masa da shi hadi da watermelon juice.
Ko da ta shiga ya same shi zaune yana karatun qur'ane a wayarsa. Direban da suke tare ya aje abincin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login