Showing 99001 words to 102000 words out of 253142 words

Chapter 34 - ABOKIN RAYUWA Hausa Novels by Khadeeja Candy.doc

23 Nov 2025

18420

waya a kunnensa domin fitar da yayi ta dazun da gaggauwa be bar shi ya fita da Bluetooth dinsa ba.

"Shikenan Daddy na gode sai mun yi magana"

Ya fada sannan yayi ma mahaifinsa sallama ya aje wayar a cinyarsa ya cigaba da tukin har ya isa gida ya faka ya kashe motar sannan ya dauki wayarsa ya bude motar ya fita ya dauki kwando. Taku goma sha daya ya kai shi entrance din shiga cikin gidan, ya tura kofar falon ya shiga da sallama kamar yadda ya saba duk kuwa da ya san ba lallai yau a tarbe shi a yadda aka saba ba domin yau ya bata ran uwargidan ba kadan ba ko da yake bata nuna masa ba.

"Sannu da zuwa"

Ta fada a yanayin da ba na fushi ba kuma ba far'a sosai ba, sai dai kuma ba ta tarbe shi kamar yadda ta saba ba. Hakan be hana shi isa inda take zaune ya sumbance ta ba sannan ya aje basket din a gurin.

"Sannu da gida Gimbiya wannan ado haka?"

"Duk na ka ne kai kadai, je ka yi wanka ka zo ka ci abinci"

"Okay"

Ya haura sama ya shiga dakinsa, tufafinsa ya fara cirewa ya aje wayarsa ya shiga bandakin yayi wanka ya fito ya saka tufafi marasa nauyi ya fito falon domin bawa cikinsa abun da yake wajibun, yunwa yake ji sosai saboda be yi karin safe ba, dan haka ya zauna a seating room din ya nade kafafuwansa Kameela ta zera masa tuwon da miyar taushe ta kawo masa ruwan wanke hannu da kuma na sha da lemun kwakwa, sannan ta zauna gabansa tana game da wayarta.
Da ya kalli yanayinta sai ya ji babu dadi, saboda ya san akwai damuwa a tare da ita, amman ta nuna masa kamar babu komai, sai ya ji kamar be kyauta ba.

"Kameela da zaki fahimce ni ki yi min uzuri, da rayuwa bata wahalar da ke ba, na san kina jin babu dadi a zuciyar kuma kin biye ko kin aje a ido kuma kina min kallon rashin fahimta, Wallahi Wallahi Wallahi babu soyayya tsakanin da Emily, abun da zuciyarta ta raya miki ko zata raya miki ko idonki ya gani Wallahi ba soyayya ba ce, kuma na miki rantsuwa na fada miki ne a yanzu ba dan ina tsoronki ba sai dan ina son farincikinki, kuma ina sonki, tsabani ko kadan bana son yana shiga tsakaninmu, farko cikinki a koda yaushe shi ne burina, idan kin yarda da ni shikenan idan kuma baki yarda da abun da na fada miki ba a yanzu shi ma duk daya"

Ya karasa tare da bude Warmers din zai fara zuba abinci, sai Kameela ta yi karaf ta dauke miyar fuskarta dauke da damuwa.

"Karki ci wannan bari na zuba maka wata"

A matukar kidime Aliyu ya kalleta ya samu kansa cikin wani kalar firgice da be taba samun kansa a zamansa da Kameela, ta nufi kitchen da sauri sai yayi hanzari tashi ya bi bayanta ko da ya shiga ya samu tana juye miyar a sink.


_______________________

Sannu  yan uwa mata! Kin gaji da kayan da ba su da salo, ba su da inganci? To yanzu lokaci ya yi da za ki sabunta wardrobe Winki da kaya masu kyau, masu ?ima daga Khadeeja Candy Store

Muna da abaya masu kyau irin na zamani, masu sau?in sakawa da jituwa da dukkanin lokaci whether ki je wurin biki, ko casual outing.

Kuma fa, ba abaya kawai ba muna da bedsheet masu launin kwantar da hankali, masu kyau a gani da taSawa. Idan kina son daki ya zama kamar hotel, to bedsheet Winmu sun dace da ke

Kayanmu masu kyau ne, farashinsu? Ai sai kiyi mamaki sau?i ne sosai. Muna nan a Kano State, kuma muna delivery zuwa ko ina!


Ki danna follow yanzu, ki biyo mu a TikTok https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1

da Instagram https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0


Ki ga sabbin kaya masu kyau da rangwame.

Zaki sami kayan Kitchen masu inganci, kayan sakawa na zamani, da electronics masu ?ayatarwa duk a farashi mai sau?i.

Za ki iya saka tufafinmu ki fita lafiya, kitchen dinki kuma ki kawata shi da kayan Kitchen dinmu, da bedsheet dinmu kuma za ki yi barci cikin annashuwa komai daga shagonmu!

Baki da lokaci? Muna da sau?in oda ta waya ko WhatsApp - 08036126660 muna aika kaya zuwa ko ina!

To me kike jira? Biyo mu yanzu a WhatsApp https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08


Ba kawai kaya ba ne salo ne, ?ima ce. A Khadeeja Candy Store.
Ki zo yau, ki WanWani bambanci, Khadeeja Candy Store inda kyau da salo ke haWuwa.
[5/28, 9:27/ AM] 5???5???5???5???5???5???5???5??? 5???5???5???5???5??: https://chat.whatsapp.com/HQSJMqxBuI985hZVzy0S03




*? Khadeeja Candy*

SARAC STARS. C - Pen...
'?


Page 3?? 1??



"Me kika saka a miyar Kameela?"

Ta juyo a firgice tana kokarin dakewa domin bata yi zaton ya biyo bayanta ba.

"Me zan saka a miyar Aliyu?"

"Miyasa kika zubar?"

"Saboda ta yi sanyi"

"Wannan cooler ba yau na fara cin abinci da ita ba, kuma yanayin miyar be nuna yayi sanyi ba, kuma tun da nake dake ai baki taba sauya min miya ba, dan haka ki amsa min tambaya ne kika saka a ciki Kameela?"

Ya daka mata tsawa yana hade fuska kamar be taba dariya ba.

"Me zan saka a ciki? Ni ban saka komai ba"

"Guba kika saka a ciki? so kika yi na ci na mutu? Da kika ga na miki rantsuwa ina baki hakuri sai tunaninki ya sauya ko?"

Ta dafe kirjinta ta zaro ido.

"Guba kuma? Me zai saka na saka maka guba a cikin abincinka Aliyu?"

"Saboda rashin hankalinki da bakin kishinki, shiyasa na yi mamaki da baki yi hauka kin nuna halinki a lokacin da kika ga Emily ba, saboda kin san abun da kika shirya?"

Ta fara hawaye jikinta na rawa

"Ka zarge ni da kowane irin abu saboda kishina Aliyu amman ban da kisan kai, kuma a kisan ma na rasa wa zan kashe sai kai da nake kauna?"

"Abun da kike yi bana masu hankali ba ne, kwakwalwarki ta samu matsala ki shirya gobe zaki koma Kaduna idan kin je can zan samu likitan kwakwalwa ya duba ki"

Yana kaiwa nan ya juya ya fice daga Kitchen din, ta bishi da kallo kamin ta jefar da kular hannunta kasa da karfi ta fara bin kayan Kitchen din tana watsewa tana kuka, sai kuma ta bi bayansa tana kuka ta shiga dakinsa.

"Ni babu inda zanje, lafiyata kalau ba ni da hauka Aliyu, idan ma wani abun kake zargin na aikata saboda wa na aikata ba kai ba? Yaushe muka yi aure da zaka fara barin wata ta shiga rayuwarka? Idan kuma na yi fada ka buga min warning ko ka dauke kafa kana nuna wata banza ta fi ni?"

Ya katse wayar da yake ya matsa kusa da tsinka mata mari.

"Karamin yaro kika dauka ko marar wayo? Yaushe zan zauna na miki rantsuwa na miki alkawari kuma ki rika dawo da magana baya? Okay saboda ina fada sai kika zabi ki yi poising dina? A tunaninki idan na mutu ke zaki huta ne? Hakki rai ai ba zai barki ki samu salama ba"

Ta zube a kasa gabansa dafe da kunci tana kuka.

"Wannan ba kishi ba ne Kameela, hauka ne kina bukatar likita ya duba kwakwalwarki, wato ki kashe ni kije ki auri wani?"

"Ko mutuwa ka yi Aliyu ba zan iya auren wani ba, ina sonka ka sani ko wata mace ka kalla Aliyu jin nake kamar zuciyata zata fito, idan har ba son yarinyar nan kake ba me yasa baka hadata da Turhan din ba? Me kake jira?"

"Yanzu duk wannan ya wuce na fada miki ki shirya gobe zaki koma Kaduna"

"Ni babu inda zan je, na koma na cewa Hajiya Me?"

"Ki fada musu guba kika zuba min a abinci, kina kokarin kashe ni, dan haka ni kuma yanzu ba zan yarda dake ba, ba zan iya kwana gado daya dake ba, ba zan iya sake cin abincinki ba, zamanki a gidan nan ba zai taba bani kwanciyar hankali ba, tafiyarki gida shi zai fi a gareki da kuma ni"

"Ni ban saka maka guba ba, sai idan daman kana neman dalilin rabuwa da ni ne kawai saboda ka kawo wata, Wallahi Aliyu ba zan taba kyaleka ba, Wallahi ko mutuwa na yi ba zan barka ba, sai fatalwata ta addabi rayuwarka, saboda kai ka daukar min alkawarin da ba zaka iya cikawa ba, Aliyu ko rabuwa ka yi da ni ba zan iya kallon ka yi rayuwa da wata macen ba"

Aliyu ya saki baki yana kallonta.

"Ah lallai baki da hankali, ashe abun na ki ma ba kis???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?hi ba ne, hauka ce, ilminki be miki amfanin ba tun da har kika iya bari zuciya da shedan suka rinjayeki, abun da kike yi a yanzu Kameela yana nuna min zaki iya kauce hanya kam kishi, zaki iya komai ido rufe"

Ta lumshe ido tana sassauta kukanta ita kadai take iya fahimtar kanta ita kadai tasan halin da take ciki, wata kila ita kam tata jarabawar kenan so da kuma kishin Aliyu.

"Ka yi hakuri Aliyu"

"Ba abu ne da za'ayi hakuri ba, maganar rai da mutuwa ake, kin san idan Ummi ta san da maganar nan aurena da ke ya kare? Kuma ko rantsuwa na yi ba zan yi kaffara ba sai ta kai ki kotu"

"So kake na tafi Aliyu? Haihuwa daya ka fara juya min baya? So kake na tafi na barka da wata banza mushirika karuwa macen da akanta babu kalar fadan da baka min ba? Idan na kome me zan fadawa Abbana? Miye ma'anar na koma gida? Ka sake ki ne kenan?"

Ya nufi closet dinsa ya canja tufafi jikinsa ya dawo ya dauki keys dinsa da wallet sannan ya ce.

"Bana son na dawo na tararda ke a gidan nan gobe da safe"

Ya nufi kofa yayi ficewarsa tana kallonsa har ya rufe kofar dakin. Wani bakinciki ta ji ya ratsa zuciyarta, ta raba kafafuwanta tana kuka mai taba zuciya, iyakar karatun data iya na son mijinta ne da kishinta, irin kishin da hankali yake rumgumar tunani su gudu a kwakwalwarta ta aikata abun da bata san inda inda illarsa zai kaita ba, da ace Aliyu be bata hakuri ba a yau da ya ci abunda zai yi sanadin ajalinsa, saboda tana ganin kamar hakan ne mafita a gareta da kuma shi, duk kuwa da ta san ba lallai hakkin rai ya barta ta huta ba.

Sai dai sanin bata da wata mafita sai wannan ya saka ta cire batirin agogo falonta ta daka ta saka masa a miya, saboda ta gane hargowa bata canja komai, domin da ta yi haukanta na farko bata samu abun da take so ba. Yau kuma zuciya taso ta kai ta baro, saboda ta biyan mijinta kuma ta tararda abun da take zargi, idan tace bata yarda da shi ba a yanzu bata yi ma kanta adalci ba, amman sanin a guri daya suke aiki da Emily ya fi komai daga mata hankali ko ba komai zai ganta kullum kuma za su yi magana, daga haka bata san iya inda abun zai tsaya ba, musamman data lura kamar Emily tana da muhimmanci a gareshi ko kuma shi din yana da wata manufa akanta, idan ba haka ba miyasa ya sama mata aiki a kusa da shi? Meyasa ba zai hadata da mai nemanta ba? A wane dalili yayi mata tsawa yayi fada da ita saboda kawai ta kira Emily a waya.

"Zan iya rayuwa ko babu kai Aliyu, gidanmu kuma ba gidan yari ba ne da zaka ce na tafi na kasa tafiya"

Ta fadawa kanta sannan ta mike tsaye ta fice daga dakinsa zuwa nata, tana shiga dakin sai kuma ta nemi courage din ta rasa, kawai sai ta rushe da sabon kuka, tana matukar son mijinta tana matukar kishinsa wannan abu ne da ya ke rubuce a cikin littafin kaddararta, rashin aiki da lissafi zai saka ta kashe aurenta da kanta yan'uwa kuma za su mata dariya su ce daman sun fada, ta tashi ta fita dakin da sauri ta dawo seating room gurin da wayarta take ta dauka ta aikawa Aliyu sakon ban hakuri da rokon kar ya saketa.

"Ba zan iya rayuwa babu kai ba Aliyu, ko sakina ka yi ba zan iya rabuwa da kai ba, idan ma har kana tunanin ina kokarin kashe ka ne ka yi hakuri ka yafe min dan Allah"

Ta jira be bata amsa ba, hakan ya saka ta kira shi be daga ba kuma be kira ba, ta san halinsa ta san idan yayi fushi yana da wahalar saukowa, ita ma dai jin ta yi bata bukatar zaman gidan dan haka ta sauya tufafin jikinta ta fice duk kuwa da kasancewar ba kowa ta sani a garin PH sai Tasmia.



ALIYU POV.

Hotel ya kama domin ba zai iya kwana a gidan ba matukar Kameela na ciki hankalinsa be taba tashi ba irin yau, ba dan komai ba sai dan ta fi kowa kusanci da shi ta san lagunsa ta kowane gefe idan har zata iya saka masa guba a abinci to zata iya masa komai ma.
A hotel din ya karasa dan yammancin da ya rage masa, kansa a kulle tunanin idan yayi baya tsayawa shi dai gaba daya ya gagara fahimtar kalar kishin Kameela shi ko a tarihi be taba jin irin nata ba, ko da yake a yanzu yana dora abun ne a babin matsalar kwakwalwa. Ya ga kiranta ya kasa amsawa haka ma sakonta be amsa rokonta ba. Ya sani idan be daukar mata mummunan mataki ba abun da zata aikata sai ya fi wannan.

Sosai yayi ma matarsa addu'a a sallarsa da Isha'i ya roki Allah ya sassauta mata wannan mugun kishin ya saka mata natsuwa da kwanciyar hankali a zaman aurensu, ya son matarsa kusan son ne dalilin da ya saka yake mata komai kuma yake daga mata kafa har take kokarin wuce gona da iri. Sai da ya hau gadon dake dakin na Hotel ya kwanta sannan ya kira Family Friend dinsa Nura da suka kwana biyu ba su yi waya ba tun bayan da ya kira yayi masa gaisuwa da barkar haihuwar da aka yi masa. Nura ya amsa wayar yana zolayarsa.

"Manya masu kasa baku nema sai dai a neme ku"

"To yanzu kai ka nemi ki ni na nemeka?"

Nura yayi murmushi mai sauki.

"Malam har garin Abuja ka shigo fa baka neme ni ba, sai da na hadu da Ummi take fada min ka shigo"

"Tafiyar ta kwana biyu ce kuma ban shirya ba tafiyarce kawai ta zo a haka, ka san yanayin aiki ba ko da yaushe muke samun time ba"

"Haka ne, aikin ne kusan da yanke mana komai ai, zumuncin ma idan ba mu yi da gaske ba sai mu bar shi saboda neman duniya"

"Toh Allah dai ta shirya ka"

Nura yayi dariya.

"Ya shirya mu dai. Yanzu dai ya gidan ya kowa da kowa"

"Lafiya kalau, ya naka iyalin"

"Alhamdulillah"

"Nura kai ka fi kusa da ni cikin dukan mutanen da na sani masu aikin lafiya, dan Allah wane likita ne ka sani kwarare ta bangaren kwakwalwa da zai iya duba mutum kuma ya fadi gaskiyar komai"

"Me yasa kake neman Likitan kwakwalwa? Lafiya?"

"Lafiya amman ba kalau ba, Matata nake son a duba"

"Subhanallahi Kameela? Meya same ta?"

"Wani kalar azababben kishi take fama da shi da ya wuce hankali, shiyasa nake son a duba kwakwalwarta abincika ko akwai wani abu"

"Ban katsi hanzarinka ba, domin ni da kai musan duk mata suna da kishi sai dai na wata ya fi na wata, amman miyasa ka ce tana da azababben kishi? Wata kila abu ne da ba saka shi a muhallinsa ba sai ka yi masa fahimta baibai"

"Nura, tun da ka ji na ce maka tana da azababben kishi tana da shi ne, ya wuce hankali"

"Kamar me take yi"

"Kamai ma tana yi har abun da baka tunani, kawai so nake ka bincika min likitan kwakwalwa da zai iya dubata, da ace kai ba likitan kwakwalwa ne ba na yara ba da kai zan nemi ka dubata"

Nura yayi shiru na few seconds sannan ya ce.

"Aliyu, look idan akwai matsala ne za ka iya fada min, kasan sometimes mu bukatar abokan tattauna sirri, kuma akwai abun da iyaye ba zamu iya barin iyaye su sani ba, kuma da can ni da kai bama boyewa juna sirri sai dan girma da kai muna yanzu da aiki da kuma rashin zama a guri daya, ya saka dukanmu muka maida hankalinmu gurin wasu abubuwan, amman ni har gobe idan ina cikin wata babbar matsala Aliyu kai ne mutum na farko da zan kira na shaidawa, domin bana kallonka a matsayin aboki kawai ko abokin karatu ko abokin gari daya, ina kallonka ne a matsayin dan'uwa na jini, domin sanadinka na zama abun da na zama Aliyu sanadinka na samu komai da na samu a yanzu, idan kana cikin wata damuwa dan Allah ka fada min"

Aliyu ya sauki ajiyar zuciya.

"Nura ka san Turhan ai?"

"Eh na san Turhan"

"Amman kamin nan daman Kameela tana da kishi kai ka sani kuma...."

Ya fada masa abubuwan da suka faru tsakaninsa da Kameela da kuma Emily ciki har da alkawarin da yayi ma Kameela cewar ba zai mata kishiya ba.

"Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, a lallai Kameela bata da hankali, taya zaki yi kokarin kashe mijin da be bijiro miki da maganar aure ba ma? Gaskiya rayuwarka tana cikin hadari, kana iya yanzu?"

"Ina hotel na bar gidan"

"Ka yi tunani mai kyau, amman ka yi kuskure Aliyu, tun farko be kamata ka mata alkawarin cewar ba zaka mata kishiya ba, be kamata ka haramtawa kanka abun da Allah ya hallata maka ba, ita mace mai kishi daga lokacin da aka fahimci tana da kishi taka mata burki ake, tun tana haukan tana kishin har ta gaji ta hakura idan ta fahimci ba zaka fasa son wata ko auren wata saboda kishinta ba, bayan kuma kishi ka yi hakuri da abun da zan fada da alama Kameela bata da zuciya mai kyau"

"Na mata alkawarin ne saboda bana da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login