Showing 81001 words to 84000 words out of 253142 words

Chapter 28 - ABOKIN RAYUWA Hausa Novels by Khadeeja Candy.doc

23 Nov 2025

18415

tsaye tana kallon Vito.

"Kajinta ko?"

Vito ya kalli Emily calmly yace

"Je ki jirani gurin mota, Chidimma zata hado kayanku yanzu zan kaiki gida"

Emily ta kama hannun Fatima suka fice daga falon, Chidimma ta sauke numfashi ta nufi Kitchen ta zuba cups din hannunta a shara sannan ta fito ta haura sama inda dakin Fatima da Emily yake.

"Kana ji tana fadar abun da yarta take so shi take so? Daman ina tunanin bata lokacinka kake yi a kan yarinyar nan baka yarda ba"

"Bana bukatar Emily ta so ni, tun da ni ina sonta hakan ya wadatar, na sani tuntuni ban gama shiga zuciyarta ba, amman da sannu zata gane kuma zata gode min ta kaunace ni, zuwa lokacin da ta rasa Lisa (Fatima) za ta gane bata da kowa sai ni"

"Idan kuma hakan bata faru ba fa?"

"Abun da yake nawa nawa ne har abada ke kin sani, dole zan yi ma Emily uzuri saboda ta sha wahalar rayuwa, kuma ta tashi bata da kowa bata yan 'uwan bata san kowa a jininta ba sai yaran da ta haifa, daya ya mutu sauran daya to me zai saka ba zata ki abun da yarta take ki ba?"

"Wai miye a wannan yarinyar da lekewa haka ne? Kana da kudi zaka iya samun kowace mace kake so a duniyar nan, idan ma fari ne akwai fararen mata, idan kana ganin kamar ita baturiya ce zaka iya tsallakawa ka auro wanda kake so wanda ta fita kyau da komai, ita wannan fa har ta haihu kana ta wahala da yaran da ba naka ba"

Ta nufi windows din falon ya daga curtains din yana kallon Emily dake tsaye jikin motarsa tana cizon hannunta.

"Abun ba daga kyau ba ne kawai, wani abu ne ya hada zuciyata da kaunarta ya daure, kamin ita ai na ga mata da yawa ban so kowa ba sai ita, bayan ita ban ga wata wanda zan iya so ba, yarinyar da dukiyata bata dame ta, sanin tana da damar da zata iya sakawa na wulakanta kowa akanta be taba burgeta ba, ita kadai ce macen da ta saka na ji ina sha'awar tara iyali, mutuwar danta nan tana da damar ta tuhume ni saboda ni na barshi na fita alhalin ba a barinsa shi kadai, amman bata tana ce min komai akan haka ba bata taba nuna min bacin ranta ba, a yanzu zuciyarta a bushe take, nakasassun mazan da suka rayu da ita basu gwada mata komai ba sai azaba shiyasa har yanzu bata san yadda zata so kowa ba"

Ya juyo ya kalli Mahaifiyarta.

"Akwai mata da yawa, amman masu irin halinta kadan ne, a idona kuma ita kadai ce, kuma baki fahimce ta, karki sake fadin wata magana marar dadi akan Emily indai kina so, ki so Emily...!"

Yana kawai nan ya nufi kofar falon ya bude ya fita, Emily na hango shi yana saukowa ta nufo shi da sauri tana hawaye.

"Vito I'm sorry kasan be kamata na yi magana da mahaifiyarka haka ba, raina ne ya bace kuma..."

Be bari ta karasa ba ya rumgume.

"Na fahimta"

"Zaka iya bata hakuri?"

"Eh, shiga mota muje"

Ya sake ta sai ta zagaya ta shiga motar Fatima daman ta dade a ciki zaune sai cika take tana batsewa kamar wata babba. Be jira Chidimma ta zo ba yayi ma motar key.

"Chidimma bata zo ba"

Be ce mata komai ba yaja motar suka fita daga gidan. Har suka isa gidan da ya tanadar ma be ce mata komai ba ita ma bata ce masa ba, amman hannunsa na rike da nata yana tuki da dayan hannun. Be gama farkin ba Fatima ta bude motar ta fita ta bar masa gambun a bude, fita yayi ya zagaya ya rufe motar ya budewa Emily ta fito tana kallonsa, ta kai hannu ta taba fuskarsa sai ya matsa baya ya bata hanya ta ratsa shi ta nufi cikin gidan shi kuma ya koma motar yaja ya fice gidan.
Ta samu gidan yayi kura yayi gummm irin na gidan da aka dade ba a shiga ba, guri ta samu kusa da Fatima ta zauna tana jin kewar danta London yana dawo mata.

"Kin ce zaki nemi kudi zaki yi gida mu bar karkashin Vito amman har yanzu ba ki yi ba"

Emily ta dube ta.

"Zan yi Fatima zan nema har ma dace zan zama miki irin rayuwar da kike so, ba ni da wani nauyi da ya rataya a wuyana yanzu sai na ki, amman ki daina abun da kike yi, ba haka yara suke ba, meyasa ke kika fita dabam?"

Ta yi shiru tana turo baki, Emily ta ja jikinta ta rumgume tana jin rashindadin fadan da ta yi mata a yanzu.

"Momy, yanzu tun da London ya mutu zan iya amfani da sunan mahaifinta a makaranta? So that yan ajinmu su daina min dariya?"

Ta tambaya murya kasa kasa, Emily ta hade wani abu daya tsaya mata a makoshi ta lumshe ido.

"I miss him"

Cewar Fatima cikin sautin kuka. Emily ma kukan take.

"I miss him too"

Ta kara kankame yarta hawaye masu zafi na sauko mata. A haka Chidimma ta zo ta same su bayan direban dake gidan Vito ya kawo ta.

"Zan yi kokari na baki rayuwa mai kyau Fatima, ni kam ba zan miki abun da iyayena suka min ba, ba zan taba bari ki ji cewar baki da kowa ba, ba zan taba wulakanta ki kamar yadda mahaifin London da naki suka yi ba, ina son jini ko yaya yake"

"Momy waye babana? Baki san bani da baba ba? To waye kuma baba na?"

Fatima ta tambaya tana lafe a jikinta. Emily ta share hawayenta da sauri.

"Idan kina son uba to ki rike Vito a matsayin Ubanki"

"Bana son shi"

Emily ta dago ta.

"Baki da hujjar tsanarsa, kalli gidan da kike zaune, makaranta mai kyau ya saka ki, ya dauki mai girka muku abinci, tufafi sai wanda kika zaba kike sakawa, a ciki wadanda na aura akwai wanda ya bani rabin rayuwar da kike ciki yanzu?"

Ta dauke da mari tana daka mata tsawa.

"Karki sake min maganar abun da ya shafi ubanki"

Fatima ta saka wani irin ihu ta dafe kunci, Emily ta tashi ta bar mata falon. Sai dai bata iya fushi ba dan haka ta dawo ta rarrashi yarta saboda tana jin babu mai rarrashinta sai ita ta rumgumeta, a tare suka kwana kamar yadda ta saba mata a yanzu tun bayan mutuwar London kullum a gado daya take kwana da Fatima.
Washe garin ranar bayan Fatima ta tafi makaranta Chidimma tana ta aikin gyara gida Emily ta shirya ta fita saboda tana jin gidan ya mata babu dadi. Taxi ta shiga ta tafi gurin sabuwar kawarta Tasmia daman bayan can ai bata da wani gurin zuwa. Bata same a apartment din nata ba dan haka ta zauna a gurin har sai da Tasmia ta dawo. Da gangan ta yi kamar bata gane Emily ba.

"Malama lafiya?"

"Lafiya kalau"

"Toh na ga kin zauna a nan ne"

"Ina jiranki ne"

"Kina jirana? Kin san ni ne? Wani abun zan miki ne?"

"Haba Tasmia"

"Malama ni fa ban san ki ba ban taba ganinki ba"

Emily ta mike tsaye.

"Karki fara wannan wasa"

"Fine na gane ki, amman fa gaskiya ba zaki zo ki janyo min matsala ba"

"Bana fatan janyowa kowa matsala, kin tsorata ne?"

"Yanzu dai ba wannan ba me kika zo yi nan"

Ta yi shiru na mintuna.

"Bana da gurin zuwa ne kawai na zabi na zo nan, kuma na ji anje nemana gida na yi zaton ko kece ko Aliyu"

"Ba ni ba ce, ni ba zan tafi gidanki ba yanzu kam, Aliyu ma ba shi ba ne domin be taba zuwa nemanki ba"

"Okay zan tafi, duk lokacin da kika ji zuciyarki ta natsu da ni, kin san gidana kuma kina da number da wayata, sai anjima"

Emily ta tafi ta barta tsaye a gurinta tana binta da kallo. A taxi ta dawo kamar yadda ta tafi a taxi ta shigo gidanta tana share hawaye. A falo ta samu Vito zaune Chidimma na zuba masa ruwa a cups.

"Do you take my phone?"

Ta tambayi abun da yafi zame mata wajibi a yanzu, domin jiya ta duba ko'ina bata ga wayarta ba. Vito ya k??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????alli Chidimma yayi mata alama da kai sai ta tafi dakinta ta dauko wayar ta mikawa Vito da hannu biyu be karba ya aje cups din dake da sauran ruwa ya kalli Emily, sai ta juya da wayar bangaren Emily da hannu daya ta mika mata.

"Akwai wata number data turo miki sako har sau hudu wai ki kirashi ya damu da ke"

Emily ta karbi wayar da hannu daya sannan ta ware dayan hannunta ta wanke fuskar Chidimma da mari.

"How dare you take my phone? Har ki karanta min sako?"

"Ta saman screen na karanta sakon ni ban san password din ba ma, shi ma na kunna wayar ne kawai saboda na tabbatar tana yi saboda faduwar da ta yi a hannuna, bayan haka kuma na kashe ta kamar yadda take"

Cewar Chidimma cikin kuka.

"Waya aikeki daukar min waya? Tsawon kwanakin nan da na yi ban damu da wayata ba ashe tana gurinki?"

"Ba ita ta dauki wayar ba, ni na bata ta aje, amman me zai saka wani ya turo miki sako? Miyasa zai damu da ke?"

Vito ya bata amsa sannan ya dora mata da tambaya, Chidimma kuma ta fashe da kuka har da zubewa kasa.

"Burinka kai ka raba ni da kowa, so kake ka ga ina rayuwa cikin kunci, matar da na samu mai kyakkyawar zuciya ta rike ni a matsayin kawa yau naje ta nuna bata san ni ba, saboda ka lalata tsakaninmu ka firgitata"

Ta dauki ragowar ruwan da ya sha ta watsa masa a fuska.

"Ni na saka ya damu, zo ka kashe ni ka huta"

Ta wuce fuuuu ta haura sama, binta yayi da kallo sai kuma yayi murmushi ya kalli Chidimma dake ba shi hakurin ruwan da Emily ta watsa masa, ya rikota ya mikar da ita tsaye.

"Karki damu"

Ya fice ya bar falon. Emily ta shiga dakinta ta zauna tana ta haki kamar wanda ta yi ya?i, ta kunna wayar ta cire Password ta shiga messages box dinta na sms sakon Aliyu ne kadai sakon da ya banbanta da sauran sakwanin dake wayarta na Mtn. Ta karanta duka sakwanin sannan ta gwada kiran numbersa.






ALIYU POV.


"Wato baki ma wani damu da ni ba kalli yadda kika yi kiba kika yi fari"

Yana maganar yana kai mata abincin da ta shirya masa a karamin falon mahaifinsu. Ita kuma tana rike da wayarsa tana abun da ta saba yi masa a waya, wato bincike amman har ta yi ta gama bata ga wani abun da zata zarge shi da shi ba.

"In ji wa? Wannan kibar fa ta haihuwa ce kowace mace tana yi da muke Video call baka gani ba"

"Aa waya ai rage miki kyau take rabin raina"

Ya sake kai mata wani spoon din.

"Kina nan kina cinyewa Alhaji abinci ko?"

Ta yi dariya tana kallon wayar da kira ke shigowa da number da babu suna a jiki, a take ta amsa kiran ta kara a kunne.

"Hello... Aliyu..."

Ta ji muryar mace tana ambaton sunan mijinta.

"Wacece wannan?"

"Emily ce"

Mai kiran ta amsa mata kai tsaye.

"Emily....?"

Ta furta da mamaki, Aliyu ya aje Spoon din hannunsa ya mika mata hannu.

"Ba ni wayar"

Ta mika masa kamar ba ita ba.

Aliyu ya dora wayar a kunnensa.

"Emily kina lafiya?"

"Ina lafiya"

"Babu abun da ya same ki?"

Kameela ta zaro ido tana sakin baki.

"Aa na kira ne saboda na riski sakonka a wayata"

"Okay, ina tare da Matata yanzu"

Gudun kar zuciyar Kameela ta sosu ko ta yi zargin wani abu ya saka be ce mata zai kirata ba sai kawai ya kashe wayar. Tsabar mamaki Kameela bata san lokacin da ta mike tsaye tana kallon Aliyu ba.


_______________________

Sannu  yan uwa mata! Kin gaji da kayan da ba su da salo, ba su da inganci? To yanzu lokaci ya yi da za ki sabunta wardrobe Winki da kaya masu kyau, masu ?ima daga Khadeeja Candy Store

Muna da abaya masu kyau irin na zamani, masu sau?in sakawa da jituwa da dukkanin lokaci whether ki je wurin biki, ko casual outing.

Kuma fa, ba abaya kawai ba muna da bedsheet masu launin kwantar da hankali, masu kyau a gani da taSawa. Idan kina son daki ya zama kamar hotel, to bedsheet Winmu sun dace da ke

Kayanmu masu kyau ne, farashinsu? Ai sai kiyi mamaki sau?i ne sosai. Muna nan a Kano State, kuma muna delivery zuwa ko ina!


Ki danna follow yanzu, ki biyo mu a TikTok https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1

da Instagram https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0


Ki ga sabbin kaya masu kyau da rangwame.

Zaki sami kayan Kitchen masu inganci, kayan sakawa na zamani, da electronics masu ?ayatarwa duk a farashi mai sau?i.

Za ki iya saka tufafinmu ki fita lafiya, kitchen dinki kuma ki kawata shi da kayan Kitchen dinmu, da bedsheet dinmu kuma za ki yi barci cikin annashuwa komai daga shagonmu!

Baki da lokaci? Muna da sau?in oda ta waya ko WhatsApp - 08036126660 muna aika kaya zuwa ko ina!

To me kike jira? Biyo mu yanzu a WhatsApp https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08


Ba kawai kaya ba ne salo ne, ?ima ce. A Khadeeja Candy Store.
Ki zo yau, ki WanWani bambanci, Khadeeja Candy Store inda kyau da salo ke haWuwa.
[5/18, 7:55/ PM] 5???5???5???5???5???5???5???5??? 5???5???5???5???5??: *

*? Khadeeja Candy*


SARAC STARS. C - Pen...
'?



FOLLOW ME ON =?G?
FACEBOOK
https://www.facebook.com/profile.php?id=100008156177914

TIKTOK
https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1

INSTAGRAM
https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0

CHANNEL
https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01

KHADEEJA CANDY STORE
https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08



Page 2?? 6??


Ya daga kansa kadan ya kalleta irin duban na lafiya?

"a gaban idona Aliyu?"

"Zauna"

Ya mata umarni.

"Wacece wannan miye tsakaninka da ita?"

"Zauna"

Ya sake fada peaceful.

"Na ban zauna ba, wacece wannan matar?"

"Emily ce, tsohuwar matar Turhan ina tunanin min mun taba magana da ke akanta"

"Toh ya aka yi kake Communicating da ita? Taya number wayarka ta shiga hannunta? Har ta kiraka har ka damu da lafiyarta? Na shiga uku kirjina"

Ta dafe kirjin tana numfashi da karfi daman tuni ta fara daga masa murya irin dagawar da kowa zai iya ji.

Kansa ya sauke kasa be sake ce mata komai ba, domin ya san halin matarsa da kishi karamin abu ne ya fita hayyacinta a yanzu nan ta fara masa hauka.

"Ni ban ma yarda ba, mu ga wayar mu gani waya sani ko soyayya kuke ka boye wani guri da ba zan gani ba"

Ya mika mata wayar ta karba ta sake shiga chat dinsa ta duba ta fito ta sake duba inbox dinsa, kamin ta shiga longcalls dinsa ta yi forwarding number Emily zuwa number ta.

"Wai ke da na yi ma alkawarin ba zan miki kishiya ba, miye abun tashin hankali idan kin ga ina magana da wata? Har yanzu hankalinki be kwanta da ni ba? Kuma ko aure zan yi ta ina zan aure matar da abokina ya aura?"

"Aliyu ka ci amanata Wallahi da kake waya da matar nan, ashe ina nan ina wankan jego kana can kana soyayya da wata, jira kawai kake na daga kafa"

Ta fada cikin kuka da hargowa, sai ya mike tsaye ya karbi wayarsa.

"Idan kin huce kin sauko zan dawo mu yi magana"

Ya juya ya fice ya barta a gurin tana gurnanin kuka, wani irin ihu ta saka tana shure shure duk ta watse abincin da suka ci da wanda ya rage a warmers ta watse kayan gaba daya a kasa kamar mai aljannu, da sauri Anty Shafa da Farida suka shigo suna tambayar lafiya sai kuma ta kasa fadar komai saboda bata son su ji abun da Aliyu ya aikata kar su mata dariya ko su ce Allah ya kara.

"Ba komai"

Ta tashi tana cigaba da kukan ta fice daga falon suka bita da kallo.

"Ba komai take wannan kukan"

Farida ta fada sai Anty Shafa ta kyalkyale da dariya.

"Ya gumama ai kadan kika gani daga halin maza, yarinyar da kin yi auren kudi ma da kin more, amman yanzu ai sai bakincikin ya miki yawa ko rabuwa kuka yi ga kiyayyar aure ga ta siyasa"

"Ai dai tun da ta nace sai shi sai ta ga babu dadi kuwa"

Cewar Farida Anty Shafa ta fice domin labartawa Hajiya Asma'u wato Mahaifiyarsu abun da ke faruwa, Farida kuma ta fita kiran mai aikinsu domin gyara gurin da Kameela ta bata.
Kameela na shiga dakinta ta fada kan gado ta fashe da wani sabon kuka tana jin kamar ta shake wuyan Emilyn da bata taba gani ido da ido ba. Ta dago ta nufi wayarta ta dauka ta duba number Emily din ta kira number, sai kuma ta kashe gudun ajin abun da take fada ko halin da take ciki ya saka ta fito dakin ta sauka kasa ta fice daga bangarensu zuwa bangaren Mama Barakat, ta bangaren ma ba shiga ta yi ba waje ta samu inda babu wanda zai jita ta sake kiran number Emily ringing biyu Emily ta amsa kiran da tsoro domin bata tsammani shigowar kira daga bakuwar number.

"Hello"

"Sannu karuwa, yar iska marar aji mai bibiyar mazan mutane, me kokarin raba aure fasika yar titi, kafirar banza yar wuta, saboda ke baki tsaya kin yi zaman aure ba shiyasa kika kokarin ruguza nawa auren ko? Toh Allah ya fiki, Wallahi ki fita sabgar mijina ko na kashe ki, Aliyu ya fi karfinki ba zai taba sonki ba ba zai taba auren mace irinki ba, karki sake kiran mijina a waya karki sake magana da shi idan ba haka ba Wallahi sai na lahira ya fiki jindadi, akan mijina zan iya komai, shegiya marar tarbiya haihuwar hasara, ke je gurin mijinki mana, wato so kika ki kashe min aure kamar yadda ke naki yake kashe ko? Me yasa dole sai Aliyu? To mijina musulmi mai addini babu abun da zai yi da fasika irinki, wato so kike ki lalata masa tarbiyar ko? Ki shige jikinsa da sunan matar abokina ki gwada masa duniya"

Uffan Emily bata ce mata ba har ta yi maganganun da zata yi ta gama.

"kina jina dam ubanki ko na sake maimaitawa? Ko da yake ke ai baki da uba ma, baki san zafin hakan ba ko da an zage ki, shiyasa yanzu kike son ki rusa gida ko? Toh ki shiga hayyacinki ni bakar macijiya ce"

Ta kashe wayar tana huci, kamin kuma ta saka ihu ta fashe da kuka, ta dawo main door ta shiga bangare Mama Barakat ta zauna a falonta tana ta rusar kuka, Mama Barakat

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login