Showing 72001 words to 75000 words out of 253142 words

Chapter 25 - ABOKIN RAYUWA Hausa Novels by Khadeeja Candy.doc

23 Nov 2025

18406

kawo Emily ta mika mata hannu domin jin take kamar zata fadi, Tasmia ta karaso da sauri ta rikata, ta kalli Aliyu.

"Me ya same ta? Wani abun ka yi mata"

"Eh fyade na yi mata"

Ta amsa mata da gatse, sannan ya rufe gefen da Emily take tsaye ya zagaya ya shiga motarsa yayi reverse. Tasmia ta bishi da kallo mamaki domin ta gane waye shi. Emily ta dafata suka shiga cikin gidan ta zaunar da ita falonta.

"Emily kin san wannan mutumen da ya kawo ki ne?"

Emily ta kalleta hawaye na sauko mata.

"Dan Allah karki tambaye ni komai a yanzu, ki tafi gida ki bari sai gobe zamu yi magana"

"Shikenan amman ki yi ma maigadinki magana domin yanzu da na zo hana ni shiga yayi wai babu kowa a gidan alhalin na san a nan na taba sauke ki"

Emily ta daga mata kai domin shi ne kawai abun da take iya yi. Tasmia ta tashi ta fice har lokacin mamakin mijin kawarta take tana jinjina halin maza duk kuwa da kasancewar bata san me yake faruwa ba. Bayan Tasmia ta fice Emily ta rumgume kanta ta fashe da wani irin kuka mai karfi sosai daker ta iya rarrashi kanta ta mike tsaye ta haura staircase din ta doshi dakin da London yake a hankali ta tura ta shiga ciki, bashi a dakin ta nufi bandaki slowly ta bude nan ma be ciki, ta fito ta janyo kofar dakin ta shiga dakinta ta zauna kan tool tana kallon kanta. Ji tana bukatar ganin danta ya saka ta nufi gurin da dayar wayarta take ta dauka ta kira Chidimma a zatonta London yana tare da ita ne.

"Kina ina"

Ta tambaya bayan Chidimma ta dauka.

"Ina gurin kawata"

"Ina London?"

"Ba da shi na fita ba, na bar shi a gurin Sir Vito kamin na fita"

Emily ta kashe wayar ta kira wayar Vito ringing daya ya daga.

"Ina London?"

"Na bar shi a dakinsa yana bachi, Ina kika je?"

Bata amsa tambayarsa ba ta kashe wayar ta fito ta sake komawa dakin London din ta duba ko'ina har kasan gado bata ganshi ba, ta fito falo tana dubawa nan ma baya nan, ta fara duba lungu da sako na falon wai ko ya boya domin dabi'arsa boya a wani gurin musamman idan yana fushi, a nan ma bata ganshi ba.
[5/8, 8:18/ PM] 5???5???5???5???5???5???5???5??? 5???5???5???5???5??: https://chat.whatsapp.com/GATlsEHRyd2HW1OjrdF5AL



*

*? Khadeeja Candy*


SARAC STARS. C - Pen...
'?



FOLLOW ME ON =?G?
FACEBOOK
https://www.facebook.com/profile.php?id=100008156177914

TIKTOK
https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1

INSTAGRAM
https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0

CHANNEL
https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01

KHADEEJA CANDY STORE
https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08



Page 2?? 3??



Ta dauki wayarta da sauri ta kira Vito.

"Ban ga London ba ko'ina na duba baya nan, kuma na yi waya da Chidimma tace ta bar shi gurinka ta fita"

"Ina Lisa?"

Fatima yake nufi domin haka yake kiranta wani sa'in saboda ya tsani sunan hausawa da aka saka mata.

"Tana.... Fatima tana...."

Ta juya ta kalli agogon falonta lokacin dawowarta daga makaranta har ya gota.

"Ina kika je? Jiya ma kin fita ina kika je?"

Ta kashe wayar ba tare da ta ba shi amsa ba. Vito ya kalli wayar har ya aje sai kuma ya dauka ya kira Chidimma.

"Hello ranka ya dade"

Ta amsa da nishadi da girmamawa.

"London yana gurinki?"

"Aa ai tare na barku da shi da zan fita"

"Baki koma gidan ba? An duba ba a ganshi ba"

"Wata kila ko yaji muryar mahaifiyarsa ne ya boya, dan yanzu rashin kulawar da take ba shi ya saka baya son zama kusa da ita, madam bata kula da shi yadda ya kamata"

"Chidimma ki yi hankali da bakinki, ki daina fada min laifin Emily, idan ma wani abu take marar kyau ki bari na gani da kaina, karki sake fada min tana gida ko bata nan sai idan na tambaye ki, madadin na ga laifinta ke zan tsane ki ne"

Yana kaiwa nan ya kashe wayar ya dauki rigarsa dake aje kan gadon ya saka ya fito dakinsa sai ya samu mahaifiyarsa a falo tana hira da mai dafa masa abinci.

"Fita zaka yi"

"Eh"

Ya amsa a takaice sannan ya dauki daya daga cikin keys din da suke lake a kofar fita falon ya fice. Ta dayam bangaren kuma Emily na aje wayar ta nufi harabar gidan tana tambayar mai gadi ko Fatima ta dawo? Sai ya fada mata bata dawo ba amman direban dake daukota daga school ya fita da mota tun dazun.

"Amman ka ga London ya fita?"

"Aa be fita ba indai ba Oga ne ya fita da shi ba a mota a kafa kam be fita ba wani kuma be fita da shi ba"

"Ya bata ban ganshi ba"

"Kin duba ko'ina?"

"Eh"

Ta amsa masa sai ta nufi kofar gate din ta bude ta sauri ta fita tana ta kalle kalle bata yarda yana cikin gidan ba domin ta duba ko'ina bata ganshi ba, haka ta fi hanya ko talkami babu a kafarta tana tafiya tana kalle kalle idan ta ga mutane sai ta tambaya ko sun ga wani yaro, kowa yace mata a'a.

"Yaro ne sosai fari yana ihu idan ya ga mutane wani lokacin yana da jin tsoro kuma yana yin abu kamar marar hankali amman ba mahaukaci ba ne Autism ne, yana da matsalar data shafi kwakwalwa"

"Ba mu ganshi ba"

Gungun mashayan sun fada suna kallon cinyoyinta dake waje. Ta dora hannu akai har zata fasa kuka sai kuma ta karfafawa kanta guiwa ta kara gaba tana nemansa. Sai da ta kusa kai karshen unguwar tana duba kwararo ko lungu bata ganshi ba kuma kowa ta tambaya sai yace be ganshi ba. Can wata zuciyar ta raya mata ko ya bi direban da zai dauko Fatima makaranta gashi bata fito da waya ba balle ta kira, ta juya ta koma da sauri duk nisan hanyar bata gani ba cikin mintuna ta dawo gidan ta buga gate din da karfi mai gadin ya bude yana kallonta sai dai be ce komai ba ita ma bata bi ta kansa ba ta nufi cikin gidan da gudu sai ta samu kofar falon a bude Fatima na zaune rike da jakarta ta makaranta tana kallon mahaifiyarta a tsorace.
Da sauri ta nufeta ta dafa ta.

"Fatima kin dawo? Da direba zai je daukarki a school tare da London aka je? Ya bata ban ganshi ba"

"Be bata ba, ruwa ya fada Vito ya zo nan ya tsamo London a swimming pool ya tafi ya kai shi asibiti"

Emily ta fadi zaune idonta na cika da hawaye wata sabuwar fargaba na tunkarota, tunaninta be bata zai tafi can ba even though ta leka bata ganshi ba amman bata saka ran zai fada ruwa ba. Ta saki Fatima ta nufi staircase ta haura sama zuwa dakinta ta dauko wani makullin motar domin wacan motar data fita da ita da safe tana can gurin aikin su Aliyu ta baro.
Ta sauko da sauri tana jin numfashi na sama kamar zai dauke gudu take amman kamar ana daure mata kafafuwa haka take ji, rashin kuzarin nan da ya same ta a office din Aliyu a dazun bayan ta gama gutsura masa labarinta ya dawo mata a yanzu.

Gurin shiga motar ma sai da ta yi da gaske sannan ta iya bude motar ta shiga, cikin karfin hali ta yi ma Motar key ta yi reverse, a hanya ma tana jan motar motar na janta sai ta taka burki ta tafi sai kuma ta tsaya ko ta yi baya kamar wanda ta sha wani abu haka ta samu kanta duk wanda ya ganta sai yayi zaton ko ta sha wani abu ne, fakawa ta yi gefen hanya ta dora kanta a sitiyarin motar tana ta sauke ajiyar zuciya ta rufe ido tana maida numfashi, ta yi hakan ya fi a kirga sannan ta samu kuzari ya dan zo mata, ta sake tuka motar ta nufi asibitin da aka saba kai shi a duk lokacin da bashi da lafiya.

Ta faka motarta a emergency ta fito ta rufe motar, ta nufi entrance din Emergency din tana kokarin daga kafarta ta taka gurin gabanta ya fada ras ras ras dudududummmm har sau uku, kamar wadda ta tuna wani abu sai ta fasa bata dora kafar, ta ja baya ta tsaya tana kallon Kofar Emergency din dake can ciki wato second door da mutane suke fitowa, ta kasa shiga ta gagara komawa ta tsaya a gurin har na tsawon minti 5. Tana tsaye a gurin sai ga Vito ya fito tare da wani yana hangota sai ya tsaya da sauri kamar mai jin tsoro, sai kuma ya taka ya karasa inda take tsaye.

"Mu tafi gida"

"Dana ya mutu ko? London ya mutu?"

Vito ya dafata kamin ya sake cewa komai ta ce

"Na jiya a jikina, an sanar min saboda ni ma uwace, ban taba samu kaina a irin yanayin da na samu kaina a yau ba, ban taba jin abu makamancin wannan ba, saboda ban taba rasa makusanci na jini ba sai yau, na ji abun da ake ji, na ragu yau na koma daga ni sai Fatima"

Tana maganar wasu masu tsananin zafi suna sauko mata.

"I'm sorry, zan kasance a tare da ke a cikin kowane irin hali Emily"

Ta fasa wani irin ihu kamar mahaukaciya Vito ya rike kamin ta kai kasa, wani irin kuka take daya saka hankalin kowa dawowa gareta, bata san yadda ake ji idan an rasa wani ba sai a ranar domin bata taba rasa kowa ba sai yau.
Shi ya saka ta mota ya tuko zuwa gida wanda suke tare kuma ya taho da gawar London, ta shiga falonta tana kuka Fatima ta tarbeta ita ma tana Kukan domin tun a dazun jikin yayi sanyi saboda yanayin yadda ta ga an ciro dan'uwanta a ruwan kamar tsumma.

"Ya mutu Momi"

Emily ta kasa magana ta rumgumeta tana ta kuka. Vito ya nemi guri ya zauna ya dafe kansa ya runfe ido, domin ba kadan yake son London ba, dama Fatima ce wata kila ba zai ji damuwa da bakinciki kamar haka ba, amman London yana son yaron yaron ma yana sonsa, shi ya canja masa suna Ibraheem zuwa London ya canja masa addinin kuma ya yarda, ba kamar Fatima ba dake nuna masa kiyaya da rashin kunya, kuma ta ki yarda da sunan Lisa da ya saka mata, haka kuma har gobe idan ibadar ta tsikareta sai ta yi sallah ko taje Islamiyar da mahaifiyarta ta sakata.
Chidimma na shigowa falon ita ma ta fashe da kuka, kusan idan aka cire Vito London ya fi sabo da ita fiye da mahaifiyarsa musamman a yan kwanakin nan da baya yarda da Emily.




KAMEELA POV.

"Hhmmm sai yau kika tuna da ni?"

"Ke tunawa kike, ke da ba kira kike ba sai dai a kira ki?"

"Baki san na haihu ba halam?"

"Tohm yaushe?"

"Yau kwana takwas, amman abun da na haifa be zo da rai ba, ina gida"

"Allah sarki Allah ya bada rayayye"

"Ameen kina PH har yanzu"

"Eh mana kin san sai na yi shekara a nan ai"

"Okay Allah ya taimaka"

"Ameen, shi mijinki yana nan kenan?"

"Tasmia ina ruwanki da mijina da har zaki tambayi mijina bana fa son haka"

Tasmia ta kalkale da dariya

"Kameela kina bani mamaki, wai ke lafiya kike kar kishi ya haukata ki fa"

"Ke ya haukata ni din ina ruwanki? Toh miye na tambayar mijina"

"To ai na ga yadda kike da kishi ne na yi zaton ko ba zaki iya barinsa a can ba tare kuka zo wanka gidan"

"Mtssschesssss"

Ta yanke kiran. Tasmia ta kyalkyale da dariyar mugunta.

"Yau da kin san abun da mijinki yayi da sai kin kusa kashe kanki dan kishi, gashi nan daga tafiyarki ya tsallaka gurin wata da ba addinmu daya ba"

Ta sake fashewa da dariya.

"Ko da yake gayen ya hadu dole ki yi kishi ki yi taka tsantsan ai"

Ta fada tana murmushi kamin ta tashi daga kwancen da take ruf da ciki ta yango Food flask dinta mai two set da ya siya gurin Khadeeja Candy ta bude ta zubawa kanta tsemo da miyar agutsi. Ta sake daukar wayarta ta kira layin Emily sau biyu tana maka miss calls sai a uku aka daga.

"Hello..."

"Wacece wannan"

"Kawar tace"

Dip ta ji an kashe wayar ta duba wayar tana mamakin waya daga? Ta sake jira sai ta ji wayar kashe. Ta tabe baki ta aje wayar kusa da ita ta cigaba da cin abincinta.



ALIYU POV.

Ya kalli harabar gidan da iska mai dadi ke kadawa sannan ya amsa.

"Ina gida"

"Gida a ina?"

"Compound"

"Me kake yi a nan toh?"

Yayi murmushi.

"Wai ke me kika dauke ni ne? A harabar gida gidan dai ba aljannu ne za su tsallako su shigo nan ba ina zan ga mata?"

"Baka kallon mata amman ai akwai social media kuma wasu ma za su iya samun numberka su kiraka"

"Saboda ni kadai ne namiji a duniyar nan? Kameela wai wane irin kishi ne yake damunki? Ke har alkawarin da na yi miki ba ki yarda da ni ba"

Ta yi shiru.

"Na san kowa da yadda Allah ya halicce shi, amman ya kamata ace muna damuwa da wasu abubuwan ba wai kishi ba a koda yaushe, already kin aure ni, ina sonki kina sona kina da kishi wannan abu ne da na sani tun kamin na aure ki kuma na aureki na miki alkawari ba zan miki kishiya ba, toh miye kuma abun daga hankali da bin diddigina?"

" Mata shedanu ne wata zata iya sakawa ka karya alkawarin da ka yi min"

"Akwai abubuwan da ya kamata ace mun damu da su, wata ma kokarin ganin ta samu kwanciyar hankali take, wata bata da iyaye bata da yan'uwa bata da kowa, damuwarta na samun canjin rayuwa ne, bata ta kishi take ba, be kamata muna damuwa da wasu abubuwan Kameela"

"Damuwar wasu ba tamu bace, kowa ai da kalar kaddararsa, ni tawa kaddarar kishi ne da kaunarka yaushe zaka zo?"

"Sai idan zaki koma zan zo na tafi da ke"

"Saboda me? Yanzu baka yi marmari na ba?"

"na yi idan na zo mi zan yi? Aiki nake a nan fa Kin sani, zan zo amman dole sai na dauki hutu"

"Toh ka dauki hutu mana"

"Okay, zan dauka shikenan"

"Eh i love you"

"I love you more, ki kula min da kanki"

"I will sai da safe"

"Okay"

Ya aje wayar yana daga kansa ya kalli sama, labarin Emily halin da ta shiga kawai yake hangowa, ya kan ji labari kala kala na ban tausayi amman be taba jin kalar nata ba, be taba arba ido da ido da wata mata da ta sha wahalar rayuwa kamar ita ba. Duk kuma labarin da ta bashi na rabin wahalar da ta sha ne na rayuwar da Khaleepa, be san wane irin zama suka yi da abokinsa ba, be san ya ya riketa ba, da alama shi ma bata sha da dadi ba shiyasa har take guje masa kuma ta biyowa yarsa cewar tana da uba a raye.

Ya sauka daga bayan boot din motar da yake zaune yana mamakin yadda zuciyar wasu mazan take bushewa su saka rashin tausayi a ciki har su cutar da abokiyar zamansu, ba su yarda ana hisabi ba ne ko kuma dai gani suke kamar matan ba su da hakki su kadai ne suke da hakki akan matansu? Abun takaici ne kuma abun haushi ace Khaleefa ya juya mata baya ya san wacece ita kuma ya amince ya aureta. A yadda taba shi labarinsa mutum mai addini amman ya take saninsa ya rufe ido ya zalinci wanda bata da kowa sai shi. Bata da uwa ba uba sai shi ko da yake har a yanzu a cikin wahala take a ganinsa saboda Vito ya mata duka a gabansa ranar da yaje gidan, shi ma yayi mata hakan ne saboda ya san bata da kowa. Ya tabbatar da ace tana da iyaye a raye wannan kangi da wahalar rayuwar da cin zafin ba za a yi mata shi ba.

"Rashin iyaye masifa ne"

Yana maganar yana danna kiran mahaifinsa bayan sun gaisa ya nemi ya ba shi Ummi ita ma suka gaisa sannan yayi musu sallama ya kashe wayar. Ya gwada kiran number Emily har sau biyu ya ji ta a kashe sai ya ji duk ya damu ya san halin da take ciki domin ya aje ta gidanta a dazu a wani yanayi marar dadi, yanzu kuma ya ji wayarta a kashe, waya sani ko mutumen dake nuna mata fin karfi ya ga lokacin da aja aje ta a dazun ko kuma wani ya fada masa, waya sani ko ma ya mata duka akan haka saboda kowa ya maida ita baiwa saboda bata da gata. Gashi ya tuna mata da baya ya san yanzu damuwar zata mata yawa, a yanzu ya gamsu da hujjarta na son gina rayuwarta ita kadai da take ba tare da neman taimakon kowa ba.

"Idan kin ga wannan sakon ki kira ni, ina son na san halin da kike ciki"

Ya aika mata sakon yana jin zafin yadda suka cutar da ita har cutarwa ta yi nasarar sauya tunaninta akan musulunci da musulmai. Ya dan jima a tsaye a waje, labarin da ta ba shi kawai yake ta hararowa yadda ta yi zaman. Sai kuma ya ji ya kagu ya ji irin zaman da ta yi da Turhan yadda ta hadu da Vito kuma taya halittar jikinta ta canja zuwa siririya bayan Turhan ya fada masa tana da jiki sosai a labarin da ta bashi a yanzu kuma ta fada masa ta yi rama sosai a gidan Khaleefa saboda wahalar data sha. Ya bude motarsa ya zauna a ciki yana kai dubansa gurin agogon da ta aje masa dazun a office. Ya kai hannu ya dauko agogon yana ta juya shi a hannunsa.

"Kai wasu mazan akwai bakar zuciya"

Ya fada yana mamakin yadda wani zai aikata abun da shi ba zai iya kusantar makamancinsa ba me balle ya aikata.

"Waya sani shi ma ko yana can yana nemanta"

Ya ayyana da nufin Khaleefa a ransa kuma yana jin haushin Turhan tun gabanin ya san wane irin zama suka yi.




EMILY POV.

Ya aje wayar a hankali kusa da ita bayan ya kashe wayar gaba daya. Ya zauna kusa da Emily da bata iya daga ido

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login