Showing 69001 words to 72000 words out of 150281 words

Chapter 24 - MARTABARMU HAUSA NOVELS LUBNA SUFYAN .txt

23 Nov 2025

3974

tasan yana azumi takan kai mishi abinci har gida. Sau biyu yana hanata zama, tana ajiye kwandon da ta jera kuloli Rayyan yake mikewa alamar su tafi. Shisa ta daina sallamar mai napep ko mashin din daya kawota, tana ajiyewa itama take tafiya ba saiya koreta ba.

Ranar da taji kamar zata mutu idan batayi magana da shi bane ta dauki waya ta kira shi, yana dagawa wani irin kukane ya kwace mata da yasa Rayyan din lumshe idanuwan shi, yanajin wani abu na budewa a zuciyar shi

"Layla..."

Ya kira da wani irin yanayi daya kara tunzura kukan da takeyi

"Ban san ya zanyi ba... Ban sani ba wallahi"

Ya fadi yana sauraren sautin kukanta da yake kara mishi hayaniya a cikin kan shi. Kamar katinta ne ya kare wayar ta yanke, kira ya kai biyar yayi bata dauka ba, yaso ya share, har kwanciya yayi, sai ya kasa. Idan kuka yake so tayi zai bata dalili, bayason wannan kukan nata. Mikewa ya tsinci kan shi dayi yana saka takalma, gani yake idan ya taka ba zai isa inda take da wuri ba shisa ya hau mashin. Sanda ya karasa bakin hostel din, ya mata kira yafi goma kafin ta daga tana fadin

"Hello..."

Muryarta na fitowa daga can kasan makoshi

"Layla..."

Rayyan ya furta yana lumshe idanuwan shi, abinda yake ji yaso yayi kokawa da shi ya kasa

"Ki fito... Ki fito in ganki"

Ya karasa hadi da sauke wayar daga kunnen shi. Sanda ta fito hula ce kawai a kanta, bai san ya zai kira abayar jikinta ba, ta dai mishi kyau saboda farar hular da ta saka. Baya son hada ido da ita bai gama karewa fuskarta kallo ba, ji yake kamar ya dade bai ganta ba, wata irin kewarta ke danne shi

"Hamma..."

Layla ta kira sunan shi daga kasan zuciyar ta, hannu Rayyan din ya mika mata, da sauri take takawa ta karasa tana kama hannun na shi, ta sa kafa ya hankade kashedin Mami da rokonta da yake shirin yi mata katanga da Rayyan din. Shi kam babu abinda yake ganewa, babu abinda yake gani a duk fadin wajen banda ita, babu abinda yake ji banda son hada jikin shi da nata, a hankali yake jan hannun nata da yake rike da shi harya hadata da kirjin shi inda yake jin kamar ya jima a cikin dokar daji, yanzun daya riketa ne ya iso gida.

Bai taba furtawa kan shi yanda ko ina bako bane a rayuwar shi banda wannan yanayin, har Bilal wani lokacin yakan ji kamar bakone a wajen shi, amman banda Layla, tun ranar farko daya fara hada idanuwa da ita suka firgita shi yasan ita din ba bakuwa bace a yar karamar duniyar shi da take cike da tarin hargitsi, ta jima a tare da shi, tun kafin ya santa kaddara ta hada hanyar su, tun kafin ya ganta yaga halitta mai kalar idanuwanta.

"Hamma"

Layla tayi maganar da alamar kuka da wani shauki a muryarta tana kara shigewa jikin shi. Ita kanta abinda take ji ba zai misaltu ba, kalar duk soyayyar da take gani daban take da wadda takewa Rayyan. A jikin shi kawai taji ta yanzun, amman launin duniyar gabaki daya ya sauya mata. Idanuwanta a lumshe take, bata taba ganin kyawun duhun da yakan baibaye kwayar idanuwanta bayan ta rufe shi ba sai yanzun, saboda a cikin duhu take yawo harta isa wani waje da ya haska mata Rayyan a tsaye, tana kallon shi da zuciyarta da take cike taf da soyayyar shi

"Shhh..."

Rayyan ya fadi yana kara riketa a jikin shi, su duka kamar sun gaji da yawon neman juna har sun fitar da rai kafin su hadu haka suke ji. Dakyar ya iya dagota daga jikin shi yana kallon fuskarta batare da ya hada idanuwa da ita ba, duk da yau tana son ganin kwayar idabuwan na shi, ko dan taga idan yanajin wannan yanayin da take ji, a karo na farko ya sumbaci goshin ta

"Nayi duk kokarin da zan iya. Ban san ya zanyi nisa da ke ba"

Rayyan yayi maganar batare da yasan ko ta fahimce shi ko itama tana jinta cikin kalar rudanin da yake ji ba

"Kar kayi mun nisa, dan Allah Hamma ka daina kokarin yi mun nisa"

Numfashi Rayyan yaja yana fitarwa. Tare suka taka rike da hannun juna, har suka samu inda suka zauna. Sun fi awa a haka, hannunta yana cikin na shi, har sai da yaga dare na karayi tukunna. Daya rakata kuwa dakyar ya bar wajen, kamar ta bashi hannun ya tafi da shi, bai karasa gida ba ranar natsuwar daya dan samu a tare da ita na kwacewa komai yana dawo mishi sabo. Daga ranar ya sake budewa kan shi kofar da ya sha matukar wahala kafin ya kulleta. Bayan nan Bilal yayi mishi magana, yayi da lallami, yayi da fada, yayi da tashin hankali kamar zai cinye shi akan rike Layla ya rasa yanda zai ya bari.

Itama Layla a nata bangaren hakane, in da tasan yanda zata daina tabashi da tayi, ko dan yanda taga hankalin Mami ya tashi, amman bata sani ba, Mami take roko da ta yafe mata, ta fahimci ba laifinta bane, soyayya ce take rinjaye akanta a kowanne lokaci, zuciyarta take riritawa fiye da martabar ta da Mami take yawan kira mata a duk wayar da zasuyi. Ta dai ji tsoro na fitar hankali randa Bilal ya sameta har hostel bayan ya kirata yana fada mata magana yake so suyi, bata kawo komai a ranta ba sai bayan sun sami wajen zama ya fara da cewa

"Ban san ta ina zan fara ba, na dai san tuntuni ya kamata in miki magana, in muku magana, sai na zabi in yiwa Hamma duk da nayi a kurarren lokaci, nayi kokarin gyara kuskuren yaki..."

Sai lokacin zuciyarta ta fara bugawa sosai da sosai, musamman da Bilal yaci gaba da fadin

"Abbu ya bani amanar ki, Abbu yace in kula da ke, na kuma mishi wannan alkawarin. Gashi na kasa cikawa, ranar farko da na ga kin rike Rayyan ya kamata in tsawatar miki, banyi ba. Kin san illar hakan, kin san rashin kyautuwar hakan Layla...ban san ya zan miki fada ba, amman zan rokeki, idan ina da wata daraja a idanuwan ki zaki bari, zaki jini tunda shi yaki jina"

Lokacin idanuwanta sun cika taf da hawaye, sai da ta saka su cikin na Bilal kafin hawayen nata su zubo

"Ina son shi.. Hamma Bilal ina son shi"

Ta fadi da dukkan gaskiyarta, a karo na farko tana furtawa wani soyayyar da takeyiwa Rayyan din. Cikin sonyin amfani da ita dan ta zame mata hujjar da zata isa ta bata damar rike shi, tana kallon yanda Bilal din yake fitar da numfashi a hankali kamar yana cikin tashin hankali, sai dai itama a cikin shi take

"Shi sa zaki daina, saboda kina son shi. Ba zaki so yaci gaba da tarawa kan shi zunubi ba"

Bilal ya fadi cike da son ta fahimce shi, kai t girgiza tana mikewa kawai tabar mishi wajen. Kuka tayi sosai ranar, da wayarta tayi kara ko bata kira ba sai gabanta ya fadi, sai tayi tunanin ko Bilal din ya kai karar su gida ne. Bata san me kuma zata cewa Mami bayan karyar da ta shirga mata na cewa Rayyan din baya kulata ba. Kuma da alama Mami ta yadda, bata dai fasa jaddada mata muhimmanci kare martabar ta ba. Kamar yanda itama bata gaji da amsa ta da

"In shaa Allah"

Ba, bata san ya suke so tayi ba, daga Bilal din har Mami, da alama basu san yanda soyayya take ba, basu san yanda duk lokacin da wanda kake so yake a kusa da kai baka muradin komai banda kaji ka rike shi koyaya ne, ka kara hada kusancin da kake ji. Musamman idan wanda kake so din Rayyan ne, Hammanta da emotions sukewa wahalar nunawa, Hammanta da bata da tabbacin zai furta mata wasu kalamai da suka danganci soyayya. Amman idan yana jinta a jikin shi sai take ganin a hankali zata raunana zuciyar shi, zata saka kalaman da take son ji su kubce mishi.

Balle takan karanta girman tasirin mace a wajen namiji, ko sarki ne akan ce a gaban mace shi din bakomai bane. Zuwa yanzun kuma tasan kalar halittar jiki da Allah yayi mata, maza da yawa a makarantar idanuwan su a kanta suke. Bata da wani makami akan Rayyan banda jikin da shima duk baudadden halin shi taga yana so, ko hannun shi ta rike tana kallon yanda yake sauri ya dumtse shi cikin na shi kamar yana tsoron karta subuce mishi. Bilal da Mami ba zasu gane wannan bace kawai hanya daya da zata iya mallaka mata Rayyan.

Tana ganin yanda Bilal ya kalleta bayan kwana biyu da rokon shi, yanda ta hada ido da shi cikin ban hakuri kafin ta rike Rayyan din. Sai mikewa yayi yana bar musu wajen

"Hamma Bilal zai fadinma Abbu bamu daina ba"

Layla ta furta muryarta na rawa tana dorawa da

"Ya mun magana, yace in daina rike ka, Hamma ban san ya zan fada mishi ya gane ba. Dan Allah kayi mishi magana karya fada a gida. Saboda Mami"

Sake riketa Rayyan yayi a jikin shi, shima din baisan ya zai fadawa Bilal ya fahimta ba, shisa bai taba amsa shi ba. In da zai iya daina rike Layla din daya bari ko dan yanda Bilal yake mishi tashin hankali a kai. Amman bai sani ba, sam baisan yanda zai fara bari ba. Hakan zaiyi dai-dai da nisa da yar natsuwar da ya samu. Yana bukatar wannan natsuwar, tana daya daga cikin katangar da take tsakanin shi da tabin hankalin da yakan ji a kurkusa wasu lokuttan. Haka suka rarrafa sukayi watanni shiddan daya kawo su inda suke tsaye yanzun.

Dan Layla tafi awa biyu a tsaye gaban ajin su tana jiran Rayyan din ya rubuta jarabawar shi ta karshe a ranar ya fito. Kuma da alama bai tsammace ta ba, tana rike da shi din tace

"Congratulations..."

Dan murmushi yaji yana shirin kwace mishi, lokacin daya kama hannunta yana zagayo da ita, kewar shi take ji tana tunanin yanda makarantar zatayi mata fadi idan baya ciki, amman zata danne komai yau ta taya shi murnar kammala makarantar shi lafiya. Wani dan ajin su ta gani yazo wucewa da rigar da daliban da suka kammala karatun su kan saka dan a dauke su hoto, kuma ya kalleta har da dan murmushin shi

"Ko zan iya aron rigar hannun ka na yan mintina dan Allah?"

Murmushin shi ya fadada, yana mikawa Layla da take mishi kallo cike da godiya, tana saka Rayyan kama dayan hannunta ya rike yana ma saurayin wani irin kallo

"Na san yarinyar ka ce"

Saurayin ya fadi yana wuce su. Duk wanda yake a ajin su Rayyan din, koma department din yasan shi da Layla, wanda suke burgewa da yawa, wanda kuma suke zagin su ma haka. Wasu na musu kallon masu dace a soyayya, wasu na musu kallon tantiran marassa kunya. Duk da haka rayuwa take tafiya, mutane basa taba rasa abinda zasu fada a kanka. Balle kuma Rayyan da Layla da suka basu abin magana a kai, a gaban kowa suke rike juna kamar su ka daine a filin wajen, kamar ba yaran hausawa tarbiyyar musulunci ba.

"Ni fa ba zan saka ba"

Rayyan ya fadi yana kallon rigar hannun Layla din

"Dan Allah Hamma... Dan Allah"

Take furtawa tana jan hannun shi da nata yake ciki, bai musa ba yake binta, basu kai da barin wajen ba Bilal ya karaso, hannun Layla da yake cikin na Rayyan din yabi da kallo, shima a watanni shiddan nan duk yayi zuru-zuru. Abinda wasu zasu alakanta da karatu, kusan harda karatu, amman baifi kaso ashirin ba, tamanin da doriya Layla da Rayyan ne. In da zai iya bude bakin shi ya fadawa Abbu a tsawatar musu zaiyi, amman wata murya na fada mishi kishine yake saka shi wannan tunanin ba girman amanar da Abbu ya bashi ba.

Sanda duk zai ga Rayyan da Layla a tare, tana mishi murmushin nan kamar zata iya tsayar da duniyar kacokan domin Rayyan idan tana da damar haka sai wani abu ya bude a kirjin shi. Amman ranar da yaji kamar kirjin nashi ya rabe gida biyu shine ranar fa ta saka idanuwan ta cikin nashi tana fada mishi yanda take son Rayyan, tana maganar kamar shine dalilinta na rike shi, dalilinta na komai. Har jiri yakeji sanda ya karasa gida, daren ranar salloli ya kusan kwana yanayi, bai san da gaske soyayyar Layla a zuciyar shi mai girma bace sai da yaga digar hawaye a cikin sujjadar shi yana neman sauki a wajen wanda ya halitta mishi zuciyar har ya darsa bugunta da soyayyar Layla.

Banda wajen Aisha babu inda yake samun sauki, kamar kaddara ta san zai shiga wani halin da zai bukaci taimakon Aisha a cikin shi shiyasa ta hada hanyar su.

"Hamma kace ya saka rigar nan ayi mishi hoto dan Allah"

Layla ta cewa Bilal din tana katse mishi tunanin da yakeyi

"Ka saka ko dan tarihi, kayi abu daya yau da zai nuna da gaske kayi makarantar nan ba siyen takardun kayi ba"

Bilal ya karashe cike da tsokanar da yaso ta dan washe mishi kishin daya taso mishi, amman hakan bai faru ba. Rayyan din dai ya yarda ya saka rigar. Sun danyi hotuna, kafin suka tafi gida dan Rayyan na kiran kan shi na ciwo. Layla hostel suka rakata tukunna. Bilal na kula da kalar kallon da take yiwa Rayyan, kamar tana son daukar iya hotunan shi da zata iya a cikin makarantar kafin ya tafi, sai yaji kamar ya sama mata sauki ta hanyar fada mata plan din Rayyan din.

"Ni in dai zan samu bautar kasar da zanyi anan Zaria ko Kaduna nake so"

Ya fadi kamar daga sama kwanaki yana saka shi tambayar

"Saboda me?"

Kafadu Rayyan din ya dan daga mishi, duk da a idanuwan shi yake ganin Layla ce bayason yayi nisa da ita. Addu'a yake da dukkan zuciyar shi kar Rayyan din ya sami abinda yake so, ya kamata yayi nisa da Layla, ya taimaka mishi yayi nisa da ita ko zai saukaka mishi jin amanar Abbu da bai rike ba, ko zai daina ganin yanda yake raba zunubin duk wani abu da zasuyi shi da Layla din.

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 7, 2020

17

A Zaria yai zaman shi, babu yanda Bilal baiyi da shi ba

"Ka zo mu tafi gida. Idan mukayi sati daya sai mu dawo. Ko dan Ayya..."

Kai Rayyan ya girgiza mishi

"Sai sun ganni zan musu laifi. Ka barni Bilal, ka cikani da surutu"

Shine amsar daya bashi, duk wata magana da Bilal din yayi bayan nan bai ko kalle shi ba ballantana ya amsa. Yana kokarin kare Layla ne iya yanda zai iya. Idanuwan Mami ko Abbu ba zasu hana shi riketa ba idan ya tashi. Ko dan Abbu ya nuna bayaso, akwai abinda zai tunzura shi ya rike Layla a gaban Abbu, abinda har yanzun ya kasa gane kan shi, yana fahimtar yanayin mutane tun kafin ya karanci fannin, shisa baya son su. Amman ya kasa fahimtar kan shi, ya kasa gane abinda yake damun shi.

Ya sha cin karo da abinda ake kira "Depression" a turance, yanzun haka yana kan magungunan shine da basayi mishi aikin komai banda kara mishi kuncin da yake ciki. Zuwa yanzun ya hakura, ya saduda da cewa akwai wani likita da zai mishi maganin matsalar shi, ko zaima fahimceta. Ya dai san katangar da take tsakanin shi da tabin hankali bata da kauri. Shisa ya zabi zama a Zaria, shi zai dauki duk wani surutu da za'ayi. Layla ba zata dauka ba, baya son kukanta, baya son ganin hawayen da bashi bane dalilin su a idanuwanta.

Sam ba zai iya zama a cikin gida daya da ita yayi mata nisa ba. Zaman shi a Zaria shine saukin su dukan su. Kuma ya ma tsaya ya karasa project din shi a satika shiddan da aka bayar ya tattara ya basu yasan ya gama. Su yake jira, ya tafi bautar kasa abin shi. Duk da Ayya ta kira shi a satin farko, sallamar da tayi ya amsa yana yin shiru

"Shine baka zo ba ko Rayyan? Yaushe rabon da in gan ka? Baka tunanin idan kai baka kewata ni zanyi taka?"

Akwai wani yanayi a muryarta a ranar da yasa shi fadin

"Ina abune haka Ayya..."

Yanda ta ce

"Hmm..."

Sai da yaji wani iri, kafin ta dora da

"Allah ya taimaka ya tsare"

Bai iya amsawa ba harta kashe wayar, daya sauke daga kunnen shi bin wayar yayi da kallo, lokutta da dama yakan nemi kusancin daya kamata ace ya kasance a tsakanin mahaifiya da danta a tsakanin shi da Ayya ya rasa. Sosai yake so yaji wannan kusancin, yakan ga Bilal na binta da kallo kamar babu macen da zata zamana da muhimmanci, kima da daraja a idanuwan shi kamarta, zai rantse murmushin da Bilal kan yiwa Ayya bai taba yi mishi irin shi ba. Akan fuskar shi zaka ga tsantsar kaunar da yake yi mata a shimfide. Ko a waya ta kira shi, kafin ya daga Rayyan ya san ita ce, saboda yanda fuskar shi take canzawa gabaki daya.

Ko ran Bilal a bace yake idan Ayya ta kira shi sai yayi murmushi, karshen bacin ran kenan a wasu ranakun. A tare da Bilal yake ganin kaunar daya kamata ta kasance a tsakanin shi da mahaifiyar shi. Zai karya idan yace abin baya mishi wani iri, sosai abin yake ci mishi rai, bambancin da yake tsakanin shi da sauran mutane mai girma ne. A tsayin satikan su kanyi magana da Layla, rannan ma tace mishi

"Dan Allah Hamma ka siya babbar waya"

Tun kafin ta karasa maganar ma yake girgiza kan shi

"Um um"

Ya furta

"Dan Allah, za muna chatting fa"

Numfashi ya sauke yana sakw furta

"Um um"

Jin ta fara cika mishi kunne yasa shi fadin

"Idan kika dameni zan kashe wannan in ajiye"

Sallama tayi mishi da sauri tana katse kiran, sai da yayi murmushin da bai bayyana akan labban shi ba, a cikin kan shi kawai ya tsaya

"Mayya... Mayya ta"

Ya tsinci kan shi da furtawa. Ranar da suka dawo kuwa bata yarda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login