Showing 129001 words to 132000 words out of 150281 words

Chapter 44 - MARTABARMU HAUSA NOVELS LUBNA SUFYAN .txt

23 Nov 2025

4186

da ita. Bai taba tsintar kan shi a yanayin da yake ji ba yau, musamman da ya kasa tuna wanne kalar passport ne Bilal ya manna a jikin takardun su, ko kamannin su sun fito ko basu fito ba. Sauran semester daya Bilal ya kammala karatun shi, yana ji a jikin shi zai dawo, yana kuma fata da addu'ar dawowar ta zamana a kusa, ya iya kalar signature din Bilal, dan ya ko shi Bilal yakan yi mamaki

"Dan dai kana zane ne, shisa bai maka wahala ba"

Cewar Bilal wani lokaci can baya, bai sha wahalar tsayar ma da Bilal karatun ba, yayi amfani da uzurin rashin lafiya ne. Kusan rabin rana yana abu daya, dan akwai kudin da ake biya kafin a iya. Wajen uku saura ya samu ya kammala komai, saiya tsinci kan shi da samun wata natsuwa da baisan daga inda ta fito ba. Baisan kafafuwan shi na daukar shi zuwa gidan su ba sai da ya gan shi a kofar gida, akwai mukullin daki a jakar shi, dan haka bai sha wata wahala ba daya shiga, ya daiyi mamakin yanda jikin shi ya dinga bari wajen budewa.

Yaji dadi sosai da bai samu kowa daya sani ba harya shiga. Dakin zaka rantse anyi watanni ba'a shiga ba saboda kurar da yayi. Sai yaji zuciyar shi ta matse a kirjin shi, tsaye yayi a tsakar dakin yana ganin rayuwar da sukayi a cikin shi kamar an kunna film, yana ganin Bilal a ko ina na cikin daki, yana jin shi a ko ina na zuciyar shi da take wani irin ciwo da baiyi tsammani ba. Ba zaice ga lokacin daya dauka a tsaye a wajen ba, wayar shi da ta fara ihu a aljihun shi ce ta katse mishi tunanin da yayi zurfi a ciki, ko dubawa baiyi ba bayan ya dauka ya daga kiran, karawa yayi a kunnen shi

"Hello..."

Ya fadi muryar shi na fitowa daga can kasan makoshi

"Rayyan"

Yaji muryar Haris cikin kunnen shi da ta saka shi yin gyaran murya saboda yanayin da yake ji

"Hamma"

Ya iya fada, muryar shi na fitowa a shake

"Kana ina? Me ya faru?"

Haris ya tambaya cike da kulawa, yanzun da ya dawo kamar kowa yake jin yanda bai cancanci tarin kaunar da yan uwan shi sukeyi mishi ba, saboda sam bai tuna wani lokaci daya nuna musu ko da kadan a cikin kalar kaunar da sukeyi mishi ba. Amman yana tuna yanda duk ture sun da yayi bai hana su kokarin kusantar shi ba. Kaunar su daban take, kaunar su na da alaka da jinin shi da yake yawo a nasu.

"Rayyan kayi mun magana dan Allah"

Numfashi ya sauke

"Zaria, ina Zaria Hamma"

Haris ya dan jima kafin yace

"Zan kwashe kayan, munyi maganar da Ayya, ka bar shi karshen makon nan da yardar Allah zan shigo Zaria din"

Numfashin Rayyan ya sake saukewa

"Kar ka bayar da komai, duka komai da komai"

Duk da baya gani yasan kai Haris din yake daga mishi

"Babu abinda zan bayar, duka zaka zo gida ka samu kayan. Ka dai fito daga gidan idan kana can, kana jina, ka fito ka tafi...zaka iya ai ko?"

Dan murmushi ya kwacewa Rayyan

"Ba yaro bane ni Hamma..."

Yanajin dariyar Haris din, bai jira yace wani abu ba ya sauke wayar daga kunnen shi yana katse kiran kafin ya mayar da ita aljihun shi. Da gaske kirjin shi zafi yakeyi, kasancewa a cikin dakin ya dawo mishi da abubuwan daya dauka ya rabu da su. Kasancewar shi a dakin ta saka mishi wasi-wasin da bayason zurfafa tunanin shi a kai sam. Shisa ya dauki shawarar Haris din ya fice daga dakin ya mayar da shi ya kulle yana fita daga gidan. Ko daya karasa ya shiga motar da ta mayar da shi Kaduna bai daina jin kirjin shi na zafi ba.

"Magana fa nake tayi maka"

Muryar Bappa ta daki kunnen shi tana dawo da shi daga tunanin daya zurfafa ciki. Mikewa yayi yana fadin

"Dole dai saika fitar da ni..."

Bappa bai kula shi ba ya juya, shima bayan Bappa yabi har suka fita daga gidan zuwa inda motar Bappan take suna shiga.

*

Ba zatace duka duniyar ta daina yi mata dadi ba, saboda yanzun duniyarta ta tattaru ta dawo cikin dakinta. Anan take gudanar da rayuwarta ta yau da kullum, ko da safe ba kullum take samun karfin zuwa su gaisa da Mami din ba. Sai dai ita ta shigo ta dubata, saboda cikinta daya fara fitowa sosai, bata son Mami na ganinta, kowa ma na gidan bataso yana ganin ta. Sai taga kamar basa ganin komai a tare da ita, kamar hatta da sunanta ya bace, banda cikinta babu wani abu da kowa yake gani a tattare da ita yanzun. Jafar ne kadai yakan fito da ita falo wasu lokuttan.

"Malama fito kiga wani abu"

Yakan ce, duk iya kokarin shi na ganin bai nuna cikin jikinta ya dame shi ba, a muryar shi takan ji canjin da ya faru da rayuwar su gabaki daya. Ta kan biye Jafar din suyi kallo tare har su danyi hirar film din, amman gabaki daya babu wani abu da take jin dadin shi. Ba dai ta iya cin wani abu sai mai manja, in dai ba girkinta ita kadai Mami takeyi mata ba to duka dakin su an koma cin abinci ne da manja. Shima kawai wasu lokuttan takan ji idan bataci ba kamar zata mutu, sai kuma yoghurt da baya yanke musu a cikin fridge.

Lokutta kamar irin yau da take zaune dafe da cikinta, hawaye ne masu ciwo suke zubar mata, tun tana daukar zasu kare har ta daina yanzun. Takan yi kukan halin da take ciki, takan kuma yi kukan rashin Bilal ba kadan ba, a hankali a hankali mutuwar ta dinga tabata kamar ciwonta ba zaiyi mata sauki ba. Anisa kuwa yanzun ba sosai suke magana ba, tunda Layla ta fada mata anwa Abbu transfer ne zuwa kudu, shine suka koma gabaki dayan su, sukan gaisa lokaci zuwa lokaci ne. Zuwa yanzun makaranta ce karshen abinda yake ranta, ta rigada ta cire karatun daga zuciyarta.

Rayyan na kokarin kiranta, shima batasan me zatace mishi ba a yanzun. Ko wanka ta shiga bata tsayawa kallon kanta, saboda bata son ganin yanda gabaki daya jikinta ya canza. Jiya ma sai taga kamar har fuskarta ta canza, bata san ko dan ta jima bata kallo mudubi bane ba. Yau ma sam batayi marmarin kallo ba, da ta sau wata doguwar riga ta zira a jikinta sai ta koma kan gadonta. Idan har bata son ganin kanta, tana da yakinin Rayyan ma ba zaiso ganinta ba, ita da kanta ba zataso yaga canjin da yake tare da ita ba.

Zatayi karya idan tace zuciyarta bata mata zafi, amman a cikin abubuwan da ta nisanta zuciyarta da su, samun Rayyan na daya daga cikin su. Ba abu bane mai sauki, amman da duk ranar da zata wayi gari da yanda take kokarin yin wani tunani na daban, tana hasaso dirowar abin da yake cikinta. Tana kuma tunanin yanda rayuwa zata kasance mata bayan hakan, duk ta yanda ta hasaso abin ba mai sauki bane, tsoro da zullumi sun bata taimako wajen danne Rayyan can kasan zuciyarta.

Alamun shigowar sako take ta ji, hawayenta ta share tana sauke ajiyar zuciya, kafin ta dauki wayar tana budewa ta duba. Sai da taji zuciyarta tayo wani tsalle kamar zata baro kirjinta, mamaki na dirar mata ganin Rayyan ne yayi mata magana a manhajar whatsapp

"Layla"

Sakon shi na farko kenan

"Na siya waya"

Ta sake karantawa

"Bakya magana dani kwana biyu ko?"

Murmushi tayi me ciwo, ta fara rubutu yafi a kirga tana gogewa cikin rashin sanin abinda ya kamata tace, kafin ta yanke hukuncin fadin gaskiya, abubuwan da suka rage mata basu da yawa, ba zata bari gaskiyarta ta kwace mata ba, musamman ma a wajen shi

"Komai ne baya mun dadi Hamma, duniyar duka ta tsaya mun waje daya"

Kallon shi tayi yanata rubutu

"Zai wuce wata rana, ki daure"

Kai ta jinjina kawai, har zata ajiye wayar saboda bata san me zatace mishi ba ya sake fadin

"Ki turomun duka hotunan mu"

Bata san me yasa taji cewa harda na Bilal yake nufi ba, duk da bai ambaci suna ba. Jikinta har bari yakeyi lokacin da ta shiga gallery din, tana binciko hotunan da ta kasa dubawa duk yanda taso yin hakan. Idanuwanta cike taf da hawayen da batayi kokarin hanasu zubowa ba ta fara tura mishi duk wani hoto na Bilal da taci karo da shi, kafin ta tura mishi nashi da take da shi, sai na shi shida Bilal wanda idan Bilal ya saka takan ce ya tura mata. Kuka takeyi sosai lokacin da ta gama tura mishi dan harda hotunan Aisha da Bilal din da yawan gaske a wayarta. Hotunan da suka sakata tunanin Aisha da halin da take ciki a yanzun.

Bataji shigowar Mami da ta juya a hankali ba, dan Abbu yace ta dinga barin Layla tanayin kukan, dan akwai sauki a cikin shi. Yana nufin tana fito da abinda yake damunta bata barshi a cikinta ba. Amman da wahala, batasan ba cikin Layla bane kawai jarabawa harda damuwar da take gani shimfide a fuskarta a duk rana. Shi kadai yakan jijjiga zuciyarta. Amman ta bar komai a hannun Allah, shi daya kadarta musu ya san yanda zaiyi dasu. Sharar da take kitchen ta dauka dan ta fita da ita can harabar gidan ta zuba a babban wajen da suke zubawa sai a fita da ita duk sati.

Ta dawo ne taci karo da Ayya, zasu iya haduwa irin wannan fiye da goma basu cewa juna komai ba, shisa abin yayi mata wani iri yau da taji tace

"Maryama"

Mamakine bayyane a fuskar Mami sanda ta juya, saboda yanayin da taji a muryar Ayya bana tashin hankali bane ba

"Ya Layla?"

Ayya ta tambaya tana kallon Mami din, ba abinda taso fadi bane ba, a kwanakin nan da suka wuce mata da wani irin yanayi, baccin kirki bata samu. Saboda tana tunanin makomarta, tana kuma tunanin abinda zata cewa Allah idan mutuwa ta risketa da hakkin mutane da yawa a kanta. Idan ana maganar lahira bata tunanin wani girman kai na da amfani, ta sha fitowa da nufin samun Mami har cikin daki ta roki gafararta amman sai ta tsinci kanta da kasawa. Yau dinma na zatace ga abinda ya fito da ita ba, kuma sai ta hadu da Mami din, ta dauki hakan a matsayin wata ishara ta samun sauki, ba saita taka kafarata zuwa dakinta ba.

"Tana lafiya. Alhamdulillah"

Mami ta fadi tana shirin raba Ayya ta wuce

"Maryama..."

Ayya ta sake kira tana saka Mami tsayawa a karo na biyu

"Ban san ta ina zan fara ba"

Cewar Ayya da muryarta take rawa

"Cutar da nayi miki wanda kika sani da wanda baki sani ba..."

Kafin ta karasa Mami ta katseta da fadin

"Dan Allah Maimuna... Idan kin taba cutar dani ko kokarin hakan Allah ya zama shaida yau na yafe miki. A zaman mu ba zance ko a tunani ban soki da abinki ba, ki yafe mun nima"

Numfashi mai nauyin gaske Ayya ta sauke tana jin kamar an dauke mata dutse a kirjinta

"Nagode... Ba zan miki karya ba, hakan baya nufin ba zan neme ki da rigima ko ba zanyi tashin hankali ba"

Murmushi Mami tayi, murmushin da ta kwana biyu batayi kalar shi ba. Batace komai ba ta raba Ayya ta wuce, in dai wannan ne ta saba da shi, mai hali baya barin halin shi akace. Kishi da rigima halayen Ayya ne, batajin kuma wani abu zai taba canza hakan, bata tsammaci maganar da sukayi yanzun ta saka su zauna kamar aminan juna ba, ko su fara hira da mutuncin da basayi a da. Idan akwai abinda ya fara sakawa take ganin girman Ayya shine matar bata iya munafunci ba, abinda yake ranta ne zata nuna maka, idan kaji haushi ma bai dame ka ba.

Ko da wasa bata taba nuna tana sonta ba tun shigowarta, tana kula da yanda taso ta ture har yaranta, sai Haris yayi nasara a kanta, duk da batajin tana son sauran kamar Haris. Da zama da munafiki da zai nuna yana sonka a gabanka a bayanka ba haka ba, gara ka zauna da wanda zai kalli fuskarka ya fada maka baya yinka, hakan ba zaisa ka daga burinka a zaman ku ba. Rigimar Ayya ta jima da sabawa da ita, kamar yanzun yanda take jin wata rana zata zo da zasu saba da wannan yanayin da suke ciki, ranar da komai zaiyi musu sauki. Ayya ma dakinta ta wuce tana jin wani sauki ya saukar mata, tana jin yanda ta rage kadan daga cikin hakkin mutanen da take ji ya shake mata wuya.

*

Sosai yaji dadin yanda duk watannin daya dauka ko Ayya bata ce mishi yaushe zaije gida ba. Suna waya kullum, yana kiranta sau hudu har fiye da haka a rana, ba hira sukeyi ba, dan yakan ce

"Zan sake duba kine daman"

Kamar yanda yakan ji Bilal yace mata wasu lokuttan, so yake ya rage mata kewar Bilal da yasan tanayi a lokaci daya kuma bayason ya fama mata ciwon da baisan koya fara warke mata ba. Tun biyan farko da akayi musu Bappa yace mishi anayin wani adashi, yayi bayanin amman badan Rayyan ya gane ba, shi din bamai yawan siye-siye bane ba, badan abinda yake turawa account din Bilal ba, kusan fiye da rabin kudin haka suke zama account din shi. Ko lokacin da suke makaranta sai kudin Bilal ya kare na shi akwai dan saura

"Duk yanda kake ciro dubu dai-dai ga kudin nan ya kare"

Ya kan fada idan yaji Bilal na maganar kudin shi sun kare shi

"Koyon ajiye kudi yana da amfani, ko badan ka siya wani abu ba, tsaron lalura ne. Idan baka saba ware wasu ka ajiye ba tun kana kai kadai, zai maka wahala idan ka fara tara iyali"

Bappa ya fada mishi, ya sha dauka yana abubuwan shi a tsare sai yanzun daya hadu da Bappa, sosai yana koyon abubuwa a wajen shi, watakila mu'amala da mutane bashi da aibun da yake tunani. Tunda yanayin Bappa din yanzun yana koyar da shi abubuwa da dama

"Ace shekaru kusan talatin amman kaga mutum baya tunanin abinda zaiyi da rayuwar shi, kudin duk da zasu shigo mishi ko bashi da abin siya saiya kirkira"

Lokutta da dama zantukan Bappa kan saka shi yayi murmushi, idan kaga yanda yake magana ko tsare-tsare sai kayi tunanin yanada yara fiye da goma da suke karkashin kulawar shi. Amman Bappa ya saka shi tunanin da gaske yana bukatar adana kudade, musamman da haka kawai Bappa din yace mishi

"Idan na koma karatu inajin idan ba nawa auren ba nakane zai dawo dani kasar nan"

Yana tuna mishi da cewa zai koma, duk da yanajin kamar babu nisan da zai yanke zumuncin da yake tsakanin su. A lokaci daya yana saka shi tunani akan abubuwa da yawa, tunani akan shi da Layla, baisan me take so ba a yanzun, amman shi ya kwana biyu da sanin abinda yake so. Da tunanin yake kwana yana tashi a satin, shisa ya yanke hukunci bin Bappa yau su tafi Kano tare, duk da baice komai ba yaga jin dadin hakan, tunda ya dade yana fama da shi da ko na rana daya ya bishi suje sai su dawo yana ki.

Ko bakomai ma yana son ganin Layla, kewarta yake ji har a kasusuwan jikin shi. Yaji dadin yanda Bappa ya sai da ya shiga ya gaishe da Ayya sannan ya wuce da nufin zai dawo da dare su fita da Rayyan din. Ayya ma taji dadin ganin shi, sai da yaje dakin su ya rage kayan jikin shi ya share dakin tas sannan ya shiga yayi wanka ya sake wasu kayan yana dawowa dakin Ayya. Anan ya zauna yaci abincin da ta zubo mishi, sai da ya gama ya dauke kwanonin ya kai kitchen sannan ya dawo ya zauna. Har yanzun bai saba magana da ita har haka ba.

Tauna abinda zai fada yakeyi, dagowa yayi yana kallon fuskarta

"Ayya ina so muyi magana ne daman"

Bata san me yake so ya fada ba, ta dai bashi dukkan hakalinta tun kafin yayi maganar

"Ina sauraren ka Rayyan"

Gyara zaman shi yayi

"Zan auri Layla, idan ta haihu zan aureta. Ina tara kudi Ayya, ban san ko zasu isa ba saboda gasu kama gida da su kayan lefe"

Bata san ya taji maganar ba, tunani dayane yake mata yawo kawai

"Babu wanda ya isa ya canza kaddara"

Ta kuma gani yanzun, duka kudadenta da ya kamata ace tayi wani abu muhimmi da shi ta kwashe ta baiwa Hajiya Dije da sunan a raba Layla da Rayyan, a raba harda Bilal da take gani a kusa da ita. Ga shi yanzun kaddarar da take zagaye da su ta hada su ukkun duka a gaban idanuwanta kuma da yake bata da iko a kai ba abinda zatayi

"Ayya..."

Rayyan ya kira saboda baisan me shirunta yake nufi ba, ya fara fada mata ne saboda yasan bata son Layla a kusa da shi, bata kuma son Mami, gara taji daga wajen shi. Rayuwar shi duka yayi ta ne cikin rashin daukar duk wani abu da zatace da muhimmanci, shisa yanzun zai fara, ya rigada ya yanke hukunci auren Layla, amman baya nufin zaiyi shi bada yardarta ba.

"Kiyi mun magana Ayya, ni din ban saba jin maganar ki ba, ina so in aureta, idan hakan na nufin in jira sai kin amince zan jira in dai bata da matsala da hakan itama, amman kice wani abu dan Allah"

Haka kawai taji zantukan shi sun karya mata zuciya. Kai ta jinjina kawai, muryarta na rawa tace

"Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya kaimu lokacin"

Numfashin da baisan yana rike da shi ba ya saki. Ya dan kara jimawa batare da sun cewa juna komai ba sannan ya mike ya fice, sai da yayo sallar azahar ya dawo sannan ya shiga bangaren Mami, itama suna gaisawa kan shi a kasa yace

"Layla fa? Ina so inyi magana da ita Mami"

Dan jim Mami tayi kafin ta mike, dakin Layla ta nufa tana Kwankwasawa kafin ta tura, tana zaune a kasa da alamar sallah tayi itama, dan ko hijabi bata cire ba

"Ga Rayyan a falo yana so yayi magana dake"

Mami ta fadi tana juyawa batare

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login