Showing 63001 words to 66000 words out of 150281 words

Chapter 22 - MARTABARMU HAUSA NOVELS LUBNA SUFYAN .txt

23 Nov 2025

3990

Shikenan..."

Ta karashe muryarta na karyewa cikin yanayin da yasa Bilal fadin

"Dan Allah kiyi hakuri....zai gyara ai..."

Kai ta jinjina, dakyar ta iya cewa

"Hmm...Allah ya shirya"

Nan Bilal ya zauna yana ta mata labari har saida ya ga ta warware tukunna ya tafi. Shisa tayi kewar shi matuqa a watannin nan da baizo ba. Duk wata hanya da zaibi ya rage mata damuwa ya sani. Yafi kowa fahimtarta, akwai halayenta da ko Abbu baisan yanda zaiyi da su ba amman Bilal ya sani. Zata iya cewa idan da na zama amini to Bilal ne amininta, duk wata damuwarta ko ta waya idan ta kira shi ta kai karar Abbu da Mami sai ya lallaba ya bata hakuri, saiya nuna mata yanda yake goyon bayanta, cikin dabarar shi. Neman Malamanta ne kawai abu daya da Bilal bai sani ba, abu daya da ba zata iya rabawa da shi ba saboda bata so yayi mata wani kallo na daban.

Mami kuwa tun da suka dawo sai ta tsinci kanta da bin Layla da ido a duk al'amurranta, tun kafin tafiyar su wayewar da yarinyar tayi ya wuce shekarunta, amman yanzun sai take ganin wata irin wayewa ta ban mamaki ta kara shigarta, kamar idanuwanta sun kara budewa. Bakinta bai daina bin Layla da addu'a ba ko a zaune take. Musamman da take makaranta, sai taita yawan tsintar kanta da faduwar gaba na rashin dalili, kuma tasan duk akan damuwar Layla ne da ta saka a ranta. Sai ta kirata sau nawa a rana, a duk karshen wayar tana jaddada mata

"Dan Allah ki kula Layla, ke mace ce. Kiyi kokarin kare martabar ki a dukkan al'lamurran ki. Ba lallai sai a shigar ki ba, martabar ki na tare da abinda harshen ki zai furta, tana kuma tare da mu'amallar ki da mutane, musamman maza... Ki kula, ki rufamun asiri ki rufawa kanki asiri"

Ta kan amsa da

"In shaa Allah"

Wani lokacin kuma ta kanyi shirun da yake karawa Mami damuwa, sai taji kamar ko Layla nayin wani abu da bai kamata ba shisa tayi shiru tana jinjina kalamanta na ranar, a lokutta irin wannan da ta sauke wayar take fadin

"Allah ka taimakeni, Allah ka bani ikon sauke amanar da na dauka"

Amman zuciyarta na rawa sosai. Jiya cikin dare ta farka, sabonta ne duk idan ta farka taji ba kishi bane ko wani matsi na fitsari da makamancin shi ya tasheta to fa sai tayi kokarin yin sallah ko da raka'a biyu ce tayi addu'a. Ta kanji kamar akwai dalilin da yasa Allah ya dawo mata da ruhinta a dai-dai lokacin. Watakila wani abune zai sameta, ko ahalinta shisa Allah ya bata damar sake kaddarar ta hanyar addu'a. Jiyan harta ninke dardumarta sai taji son ta duba Layla, wajen karfe biyu da rabi, tana kama kofarta da take kullewa a kwanakin nan sai tayi nasarar jinta a bude, turawa tayi taga Layla ta kife wayarta da saurin gaske.

Kwan fitilar dakin ta kunna, haske na gaurayewa da yake akwai wutar lantarki

"Layla?"

Ta kira tana karewa Layla da take zare mata idanuwanta da ta ga sun sake launi da alamar baccin da yake cikin su da kuma wani abu daban da ba zata ce ko menene ba

"Karfe nawa yanzun? Baki yi sallah ba bakiyi komai ba dan ubanki kin zauna danna waya?"

Mami ta karashe a fadace, wayar nan tana ci mata tuwo a kwarya, daman da rana sanda zasu ci abinci duk sai da ta amshe a hannunta da na Jabir tukunna suka maida hankali suna cinye abinci suka sake daukar wayoyin. Yau dai a tsorace Layla take kallonta, ko kadan bata san cewa bata kulle dakin ba. Kamar sanda ta dauko ruwane wajen karfe sha biyu, hankalinta nakan labarin da take karantawa, shaf ta manta da ta kulle dakin. Hankalinta a tashe yake da yanayin labarin, ta fita daga group din. Idan an aiko wani mai zafine sai Nanaa ta mata copy ta tura mata.

Makoshinta da kamar an zuba kasa saboda yanda take fitar da numfashi yasa ta tashi ta dauko ruwan, ashe bata kulle kofa ba, har zazzabi take ji na rashin dalili kafin Mami ta shigo mata daki babu tsammani, zuciyarta har cikin bakinta taji saboda yanda ta tsorata, idan Mami taga abinda take karantawa kashinta ya bushe, ita da waya har abada, a jikinta take jin haka

"Bani wayar ki kwanta dan ubanki, marar hankali kawai"

Wani irin bugawa zuciyar Layla tayi, muryarta na rawa tace

"Dan Allah Mami kiyi hakuri, wallahi caji zan saka in kwanta yanzun daman..."

Layla ta karashe tana dauko wayar daga karkashin cinyarta, hannuwanta rawa suke sanda ta fita daga WhatsApp tsabar tashin hankali. Gabaki daya wayar ta kashe ta janyo cajar ta da take makale a bango ta saka wayar ta dora kan durowar gefen gadon. Tana jin idanuwan Mami akanta

"Akan wannan raba daren na kusa haramta miki wayar nan gabaki daya. Taya ba zakiyi fama da ciwon kai ba? Kullum ba zaki samawa kanki hutu ba"

Ita dai Layla kwanciya ta gyara tana jan bargo ta lullube har wuya, zuciyarta banda bugawa babu abinda takeyi, duk fadan Mami bakomai yake karasawa kunnuwanta ba, yanda ba zata sake kuskuren barin kofa a bude ba take tunani. Har Mami ta kashe mata kwan dakin tana ficewa hadi da ja mata kofa. Wucewa dakinta Mami tayi, amman har yau abin yayi mata tsaye a rai. Tana tunanin ko Layla ta fara kule-kulen samarine da suke riketa da hirarraki har cikin dare haka. Duk da tana tunanin akwai wani abu da yake wanzuwa a tsakanin Layla da Rayyan da su kan su basu fahimta ba har yanzun. Tsoro ne fal a ranta, saboda a lokaci irin wannan ba yara mata bane matsalar, su daman masu rauni ne, mazan ya kamata iyaye su tsawatarwa.

Allah ya sani saboda Layla take kokarin bin diddigi akan su Haris, tasan shi bashi da matsala, budurwar shi guda daya. Yar gidan Yaya Ayuba ce kuma, tasan baya kule-kule. Jabir ne damuwarta, kullum cikin mishi nasiha yake, idan wasu yake yaudara zai iya dawowa kan Layla

"Dan Allah Jabir ka kula, kaga kana da kanwa, ka tayata kare martabar ta wajen mutunta yaran wasu, karka cutar da 'yar kowa..."

Dariya yakan yi sosai

"Malama Mami"

Ya kan fadi yana dariya, har sai ta zage shi ko yaga tana shirin daukar wani abin dan ta kwada mishi tukunna yake tashi ya gudu daga dakin yana mata dariya. Tasan ba zata raba Layla da samari ba, ko dan yanda take da kyawu. Dan ta hanata raba dare tana hira abinda zasu fada din idan na banza ne har da rana ma sai su fade shi. Tana hana danna wayar daren ne dan ta kwanta ta samu wadataccen bacci, saboda yanda take yawan mitar ciwon kai. Sosai Mami na ganin wautar masu yankewa yaran da zasu gani tsakiyar dare suna chatting hukunci marar kyau.

Ba lallai maganganun banza sukeyi ba, maganar banza bata bukatar lokaci, zai iya yiwuwa hira suke ta yau da kullum da abokan su, kamar yanda kake zama kayi hira sosai da naka abokan, ko idan kayi baki hira tayi muku dadi sai a raba dare ana zantawa, zai iya zamana baccine ya kauracewa idanuwansu, zamani da yai musu sabo da waya yasa suka dauka suka shiga dan duba tsofin sakkoni su rage kewa, watakila, watakila dalilai ne mabanbanta. Akwai munafunci da son kai a yanke hukuncin cewa maganar banza yaran sukeyi da tsakar dare. Saboda kai me kakeyi kenan? Me ya kaika shiga manhajar da tsakar dare? Me ya kaika bincikowa kaga ko suna online ko basa nan? Gulma?

Addu'a Mami tayi sosai da ta dan sama mata natsuwa. Da yake tun dawowar Layla bata barinta yin wani aiki, ita take su girki da gyaran gidan tunda bata da kwiya. Magriba da aka kira yasa Mami kiran sunan Allah tana mikewa dan taje ta gabatar da sallah.

*

Tsaye yake a bakin kofar dakin su ya dawo masallaci sallar isha'i. Wayar shi yake dubawa yana ganin sakonnin Mtn da suke ta cire mishi kudi na rashin dalili, harda su wani caller tune da baisan sanda yai subscribing ba. Karamin tsaki yaja, sakonnin ma duk sun taru sun cika mishi waya, ba dubawa ya cikayi ba. Ya goge duk na Mtn din. Ya shiga na bankin shi ma yana gogewa. Na Layla ya shiga, akwai wanda ma bai bude ba ashe, shifa waya sam bata dame shi ba. Balle kuma tunda suka dawo gida, in banda Layla babu wanda ya kira da wayar, sai fa Bilal da idan ya fita yana son gaya mishi wani abin ya kira shi.

Ya kara yawan kwayoyin da yake sha saboda ya daina samun bacci kwata-kwata, na ranar ma wahala yake mishi. Haushin komai da kowa yake ji, baison yin magana, ba kuma yaso ayi mishi. Surutun na kara mishi hayaniya cikin kan shi sosai da sosai. Yafi bukatar shiru akan komai yanzun. Sam baiji takun tafiyarta ba, sai hannuwanta da ta sakala cikin na shi tana fadin

"Hamma..."

Ba dan bata gan shi ba duk yinin ranar, ta gan shi bai dai kulata ba, inda take ma bai kalla ba, tunda suka dawo ya kara zama shiru-shiru

"Kaqi fadamun abinda yake damun ka ko?"

Ta furta da wani irin sanyin murya, saboda ta tabbatar akwai abinda yake damun shi, Rayyan na jinta a wajaje fiye da jikin shi, musamman da ta kara riko hannun shi tana dora kanta a damtsen hannun nashi, bai hanata ba, bai kuma daina duba sakonninta da yake dubawa ba, surutu takeyi amman tare da ita a jikin shi haka sai yake jin shirun da yake dan bukata a cikin kan shi, kamar karta raba jikin shi da nata, kamar ta zagaya duka hannuwanta ta bayan shi ta rike shi dam haka yake ji.

"Hamma..."

Layla ta kara kira tana jin kamar ta mayar da shi cikin ta saboda wani irin yanayi da taje ji. Da gaske tana son shi, tana kaunar shi da dukkan zuciyarta, a kwanakin nan tana hasaso rayuwa kala-kala a tare da shi. Wayar dai yake dannawa, yanda tayi luf a jikin shi da yanayin sunan shi da ta kira sun sa ya daina gane abinda yake karantawa. Su duka biyun suna wata duniya ne ta daban, har sai da suka ji muryar Mami da tace

"Layla?"

Cikin wani irin tashin hankali, dai-dai lokacin da Layla ta tittida kafarta tana son sumbatar gefen fuskar Rayyan din saboda yanda wata irin soyayyar shi take nuqurqusarta. Mami kuwa jikinta babu inda baya rawa, Layla din ta fito ta kira dan ta bata lambar Haris ta Etisalat din shi, wadda take ta kira taki shiga, ta tsammace ta wajen bangaren su Rayyan din daman, amman ba'a jikin shi makale ba, ba a cikin wannan mummunan yanayin da yasa numfashinta har tsaitsayawa yakeyi ba. Ga kafafuwan ta da taji suna barazanar kasa daukarta.

Tun da ta shiga aji biyu sakandire ta zaunar da ita tana kara jaddada mata yanda babu halaccin wannan rirrike rirriken a tsakaninta da duka mazan gidan. Har misali tayi mata da su Rukayya, da yanda ko su basa rike hannun Rayyan. Sosai ta tsawatar mata saboda ta ganta da ta Rayyan din yazo nemanta ta rike mishi hannu. Ta dauka tun a lokacin ta bari, tunda a gabanta Rayyan din ya fisge hannun shi har duka ya kai mata, sai Mamin taji sanyi. Idan ita Layla bata da hankali Rayyan yana da shi.

Amman ko da Layla tana tunanin Rayyan din Yayanta ne, wannan rikon da tayi mishi ya wuce na yan uwantaka, idan ba idanuwanta bane suka gane mata kamar sumba Layla take shirin mannawa Rayyan din

"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..."

Mami ta fadi tana nufar Layla da ta raba jikinta daga na Rayyan da bayanannen tsoro a cikin idanuwanta

"Ma.. Mami"

Ta furta muryarta na fitowa a sarke, Mami na karasawa wani mari ta dauke Layla da shi tana kai mata dukan da Rayyan yaji har tsakiyar zuciyar shi. Lokaci daya kan shi ya sara yana daukar ciwo, bai dai motsa daga inda yake ba, idanuwan shi na kafe kan wayar da hankalin shi baya kai.

"Ashe baki da hankali? Ashe baku da hankali"

Cewar Mami da wani irin firgici marar misaltuwa, tana kara kaiwa Layla da take zubar da hawaye duka tana damko hannunta, Rayyan da yake tsaye Mami take kallo

"Idan ita bata da hankali kai baka da shi? Baka san haramcin da yake cikin abinda kuke aikatawa ba ko? Wallahi da Abbun ku zan hada ku, ba zan iya ba, ba zaku ja mana magana ba"

Mami ta karasa tana fisgar Layla zuwa bangaren Abbu, sai tirjewa takeyi saboda tsoron da yake cike da zuciyarta. Rayyan ba zaice ga abinda yake ji ba, amman jikin shi har bari yake daya kare Layla daga dukan Mami din, sosai zuciyar shi take jin ciwon dukan da tayi mata. Baice abinda tagani me kyau bane ba, har Bilal ya fada mishi ya daina baiji ba, ba laifin Layla bane ba, shine daya barta. Yaso ya bude baki yau ya gayawa Mami haka, amman baisan ta inda zai fara ba, shisa yayi shiru. Ya kasa barin wajen, yana nan tsaye har lokacin yaga Abbu yayo wajen, Mami na biye da shi, sai Layla da take biye da Mami din tana kukan da yake shigar mishi rai.

Yau yasan bayason hannun kowa ya taba jikin Laylar, bayason kowa ya zama dalilin kukanta idan bashi ba. Ita yake kallo har suka karaso wajen da Abbu yana kiran

"Rayyan?"

Saboda shima zuciyar shi bugawa takeyi, ya zauna kenan Mami ta shiga rike da Layla tana fadin

"Dan Allah kayi musu magana ko zasu jika, kayi musu magana kafin mu suja mana magana..."

Yanayin muryarta da yake cike da tsoro da karaya yasa Abbu tambayar

'Su wa? Lafiya? Me yake faruwa ne Maryama? Layla me ya faru?"

Ya karasa maganar yana mikewa, Layla da take kuka Abbu take kallo

"Dan Allah Abbu kayi hakuri, ba zan kara ba, ba zamu kara ba"

Saboda yaune karo na farko da tsoro matsananci ya cika mata zuciya haka. Kaunar da takewa Abbu mai girma ce, bataso yayi fushi da ita

"Wai me ya faru?"

Abbu ya sake tambaya dan duk zuciyar shi dokawa takeyi, Mami dakyar ta iya fadin

"Rungume na gansu ita da Rayyan"

Maganganun na fito mata da wani irin nauyi na tashin hankali. Wani sarawa Abbu yaji kan shi yayi kafin maganganun Mami su zauna mishi, ma'anar su da tashin hankalin su ya zauna mishi yana wujijjiga duk wani zaman lafiya da yake tare da shi. Marainiya, amanar da suka dauka shi da Mami, ai baisan kafafuwan shi sun taka ba sai da yaji shi a waje, kan shi tsaye bangaren su Rayyan din ya nufa yana kuwa hango shi a tsaye, suna karasawa hannun shi Abbu ya daga yana saka Rayyan lumshe idanuwan shi, saboda a karo na farko yau yayi tunanin hannun Abbu zai sauka a jikin shi. Bai bude idanuwan ba sai da yaji ya kama hannun shi.

Lokacin da Ayya ta zo wajen, saboda Huda taje ta fada mata ga Mami can tana dukan Layla yanzun ta gansu wajen dakin Rayyan din, kuma ta ga Rayyan a tsaye a wajen. Shisa Ayya ta taso ta fito a bazame, ganin Abbu rike da hannun Rayyan ya sata fadin

"Lafiya? Me ya faru?"

Tana sauke idanuwan ta akan Mami da Layla da ta kara boyewa bayan Mami tana tsiyayar hawaye saboda kallon da Ayya ta watsa mata

"Me ya faru wai?"

Mami ce ta kalli Ayya tana amsawa da

"Me yasa ba zaki tambayi dan ki ba?"

A fadace Ayya ta kalleta

"Da yai uwar me zan tambaye shi? Maryama kinga ki kiyayeni..."

Sun kwana biyu basu shiga harkar juna ba, tunda Mami ba biye mata takeyi ba, amman yau ranta a bace yake matuqa, abinda duk Ayya taje ji itama tana dai-dai da ita

"Idan ban kiyayeki ba me zai faru? Maimuna ki fadamun abinda zai faru yau idan ban kiyayeki ba, kuma wallahi kija ma danki kunne, ya kyalemun yarinya, domin amana ce a wajena"

Da tashin hankali Ayya take kallon Mami jin maganganun ta, ta bude baki Abbu ya kalli su biyun

"Maryama ki wuce ki koma ciki"

Akwai wani yanayi a muryar shi da yasa Mami juyawa, Layla zata bi bayanta Abbu yace

"Ke ki tsaya..."

Sosai Ayya ta kalli Abbu

"Ahmadi ban..."

Wani irin kallo yai mata

"Kema ki wuce Maimuna"

Bata taba ganin shi a yanayin da take ganin shi ba yanzun shisa ta kama hanya tana wucewa cike da son sanin abinda ya faru. Sai da tabar wajen sannan Abbu ya kalli Layla da take ta tsiyayar da hawaye

"Kar in sake ji, kar kuma in sake gani..."

Saboda yana ganin dana sanin da yake shimfide a fuskarta, ga kuma tsoro, ko da nasiha ko fada zai mata babu wanda zata fahimta a halin da take ciki. Kai kawai take daga mishi tana share hawayenta da bayan hannun, ganin yaja Rayyan zasu wuce ya sata fadin

"Dan Allah Abbu karka dake shi, baiyi komai ba shi"

Numfashi Abbu ya fitar da kalaman ta yana girgiza kai kawai saboda baisan inda zai dauke su ya ajiye ba, dakin su Rayyan din yaja shi saboda gani yake kafin su koma bangaren shi kalaman da yake ta hadawa sun bace mishi, gefen gado yaja Rayyan da bai musa ba ya zauna. Tsugunnawar da yaga Abbu yayi yasa ka shi jin wani irin abu ya tsirga mishi cikin kai. Ga wajen da Abbu ya rike mishi hannu kamar an kona shi yake ji, radadi wajen yake mishi ba fitar hankali.

"Rayyan..."

Abbu ya kira zuciyar shi na wani irin ciwo, yau so yake yaji matsalar yaron na shi, amman yaki yarda su hada ido, gabaki daya iskar dakin tayiwa Rayyan kadan

"Rayyan dan Allah yau ka kalli idanuwa ka fadamun matsalar ka, ina so in sani. Idan da yanda zan taimaka maka zanyi, wallahi zanyi komai in taimaka maka, amman hakan ba zai yiwu ba sai ka mun magana"

Kan shi Rayyan ya kara sunkuyar wa kasa, kirjin shi kamar zai kama da wuta saboda iskar da bata kai mishi inda ya kamata. Baison magana da Abbu, bayason ganin shi, bayason jin muryar shi duk da yasan yana cikin jerin mutanen da ya kamata ace yana jin kusanci da su, ya kamata ace yana so

"Kayi mun magana"

Abbu ya sake fadi, ya kai mintina kusan goma a tsugunne yana so

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login