Showing 132001 words to 135000 words out of 150281 words

Chapter 45 - MARTABARMU HAUSA NOVELS LUBNA SUFYAN .txt

23 Nov 2025

3950

da ta jira amsar Layla din ba, dakinta ta koma. Zuciyar Layla har cikin tafukan hannayenta take jin su. Ta ga kiran shi amman bata daga ba, saboda yace mata zaizo bata bashi amsa ba, tunda safe da taga sakon shi take kuka. Yanzun ma idanuwan ta taji cike taf da hawaye, watakila idan yaga bata fita ba ya hakura ya kyaleta, batajin zata iya bari ya ganta a yanda take din nan. Cikinta ya fito sosai tunda ya shiga cikin wata na biyar, har awo na farko tayi, yanzun takan ji motsin abinda yake ciki, har bacci yakan tasheta idan yayi wannan kwakkwaran motsin.

Text taji a wayarta, ta mika hannu tana daukowa ta duba, Rayyan ne

"Ba zakici gaba da shareni ba, ba zan barki kici gaba da shareni ba. Idan baki fito ba zan shigo"

Hawayen da suka zubo mata ta share tana dafa gadon ta mike da dakyar. Cikin yasa tana kallon Mami da wata daraja ta daban yanzun. Ko juyi zatayi a bacci saita tashi zaune idanuwanta tar sannan take juya, ga wani irin ciwon jiki da take fama da shi naban mamaki. A kasan zuciyarta haka kawai take jin kamar kafarta daya a duniya take daya kuma a wani waje da bata da sunan da zata bashi har yanzun. Tana tallafe da cikinta ta fito daga dakinta, bata ga fuskar Rayyan ba, bayan kan shi kawai tagani, amman ya isa ya karyata mata duk wani tunani da tayi na binne mafarkin samun shi.

Saboda wata irin soyayyar shi ce ta taso mata tana saka har abinda yake cikinta yayi wani irin motsi daya sakata kiran sunan Allah cikin yanayin da ya saka Rayyan juyawa ya sauke idanuwan shi cikin na Layla da ta bude. Sai taji ta daburce, juyawa take shirin yi ta ruga, wani waje take son kasancewa da baya nan

"Layla... Dan Allah... Karki boye mun"

Rayyan din ya fadi cike da wani irin tsoro a muryar shi da yayi mata tasiri. Ganin ta tsaya tana juyowa yasa shi mikewa ya zagaya zuwa inda take yana fuskantarta. Jikin shi bari yakeyi daga ciki, hatta da zuciyar shi rawa takeyi mishi. Baice yanayinta bai taba shi ba, bai kuma yi kokarin boye hakan dan karta gani ba. A duk rana tun bayan daya sani da cikin jikinta yake kwana yana tashi. Amman hakan baisa yaji saukin ganinta dauke da shi ba, ganin shi ya fito sosai haka.

"Hamma"

Layla ta kira da wani yanayi a muryarta, tana saka har dayan hannunta ta kare cikinta kamar tana son boye shi saboda irin kallon da Rayyan din yake mata

"Kaima ka daina ganina ko? Ka daina ganina sai cikin da yake jikina"

Ta karasa maganar tana jin wani daci a zuciyarta da hawayen da suka zubo mata. Kai Rayyan yake girgiza mata, amman ya kasa hada idanuwa da ita har lokacin, cikin kuka tace

"Na sani, kowa baya gani sai cikin nan, kamar ba a jikina yake ba haka nakeji, ina jin kamar tare da cikin ni na bace, shisa kowa baya gani na"

Sai lokacin ya iya kallon idanuwanta da suke cike taf da hawaye yana furzar da numfashi ta bakin shi, bayajin akwai wasu kalamai na lallashi da zai fada mata

"Ina ganin ki, ina ganin ku duka ba zan miki karya ba. Amman ina ganin ki"

Cewar Rayyan yana dorawa da

"Na san na fadi abubuwa da yawa. Zan sake fadin wani yanzun. Zan aure ki, ba dan abinda ya faru ba, dan ina son ki, zan aure ki in har yanzun kina jin zaki iya rayuwa da ni"

Sai da ta dafa kujerar da take gefenta sannan ta iya tsugunnawa saboda yanda kalaman shi suka daketa. Numfashi take fitarwa wani irin kuka na kwace mata. Tsugunnawa yayi shima, idan zai fada mata sau dari ba zai gaji ba, saboda bayason wannan kadaicin da yake gani a cikin idanuwanta, bayason yanda take jin kamar ita kadai ta rage a duniyarta, kamar babu wanda zai taba fahimtar halin da take ciki, wannan yanayin shi yake kaika fadawa depression, abinda zaiyi komai da yake karkashin ikon shi na ganin bai bari Layla ta dandana wannan duhun ba.

"Na fadama Ayya, ta mana fatan alkhairi. Bake kadai bace ba, ba zan fahimta ba nasani. Amman ina tare dake, koma menene ni da ke muna tare"

Kamar maganganun shi na kara tunzurata, kuka takeyi sosai, bai hanata ba, bai dai daina gaya mata yana tare da ita ba cikin wata murya da take kara karya mata gabban jikinta. Ba zatace ga iya lokacin da suka dauka a haka ba, ta dai tuna yanda ta samu dakyar tana mikewa.

"Ina tare da ke"

Da Rayyan ya fadi ce ta rakata dakinta, ya kai mintina biyar kafin shima ya iya mikewa. Idan ma bata yarda ba zaici gaba da fada mata daga nan har lokacin da zata yarda da shi. Saboda wannan zaman da sukayi kawai ya kara tabbatar mishi da ana halittar wani dan wani, dan yanajin zuciyar shi an halitta mishi itane kawai dan ta dokawa Layla ita kadai, ita din tashi ce kamar yanda yake fadi a ko da yaushe.

"Aure zanyi Bilal, har yanzun ba zaka dawo ba ko? Da gaske wannan karin ba zan yafe maka ba"

Shine abinda ya fadi bayan ya shiga daki da dukkan zuciyar shi yana fatan Bilal din zaiji shi ko ta wanne haline. Saboda kwanakin sun fara mishi tsayi.

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 16, 2021.

31

"Abbu ka yafe mun, dan Allah Abbu ka yafe mun, duk ku yafe mun..."

Shine kalaman da sukewa Abbu amsa kuwwa a cikin kunnuwan shi harma da kai. Muryar Layla na zauna mishi da wani yanayi, yanda tayi maganar kamar tana saka ran fitar duk abinda yake cikinta zaizo ne da ajalinta. Da kan shi shekaranjiya bayan sun sake kwasowa zuwa asibiti cikin dare ya samu likitan yace

"Wai ba zakuyi mata aiki ku ciro abinda yake cikin nata bane? Tun da satin nan ya kama yarinyar nan take cikin wahala, dan Allah ku duba lamarin"

Murmushin karfafa gwiwa likitan yayi mishi yana kuma bashi tabbacin babu wata matsala dan wasu matan nayin haka. Ba zai manta ba, ko Mami takan yi doguwar nakuda, ta Layla din ce dai take tsaya mishi a rai fiye da duk wadanda yagani a baya. Nakudar ce saita taho mata gabaki daya sunzo asibiti sai kuma ta lafa ace ba haihuwar bace su sake kwasa su koma, yau ne karo na hudu a sati daya. Ita take ciwon amman zai iya rantsewa rashin natsuwa ya saka sunyi zuru-zuru gabaki dayan su. Yau kam ko da sunce ba haihuwar bace shikam zaice a barta a asibitin ne kawai.

Bai san akwai tsoron da zai danne na ganin jikan da zai diro ahalin su da gurbataccen asalin da bashi da masaniya a kai ba sai yau. Ko da yake zaice akan cikin Layla ya fahimci ba mata kadai ke da gulma ba, ba kuma su kadai tsegumi ya tattara ya zaunawa ba. Tun bai gane kallon da akeyi mishi a masallaci ba, da yanda har wani dan jinjina kai wasu a cikin mutanen unguwar sukeyi kamar alamun tausaya mishi duk idan sun hada idanuwa, ciki harda mutanen da gaisuwar musulunci ce kawai take giftawa a tsakanin su.

A cikin irin mutanen ne wani ya iya samun karfin gwiwar tarar shi sun fito daga masallaci yana fadin

"Alhaji ashe kuma haka wannan lamari ya faru da yar wajen ka? Allah ya kiyaye na gaba, kasan yarane yanzun ka haife su baka haifi halin su ba, kana iya kokarin ka akan tarbiyar su suna dauko maka magana. Allah dai yasa an dauki hukunci mai karfi akan yaron da yayi ta'asar"

Tunda ya fara magana kallon shi kawai Abbu yakeyi, shi da kan shi sai da ya tsargu ya fara kame-kame yana barin wajen. Amman tabbas zantukan shi sun rigada sun isar da sakon da yake son su isar a zuciyar Abbu, mutane sunyi gaskiya, zancen duniya baya boyuwa, ba kuma komai bane idan ka binne yake kwanciya lafiya, wasu hawaye yaji masu zafin gaske sun taru a cikin idanuwan shi. Da girman shi da komai, ashe kallon tausayin da kowa yake mishi kenan a cikin unguwar, kallon yanda martabar gidan shi da ahalin shi ta tabu. A ranar sai da ya kasa hakuri yake labartawa Mami abinda ya faru, sai dai murmushi tayi mai cike da karayar zuciya.

Don dai batason kara daga mishi hankali shisa bata fada mishi ya taushi zuciyar shi ba, ba zatace ga lokacin da maganar cikin Layla ta bullu a cikin dangin su ba, ko ta hanyar da hakan ya faru. Duk da tana son dora alhakin akan Anty Uwani, dan itace ta zo gidan tayi sa'ar ganin giccin Layla, duk da a lokacin akwai hijabi a jikin Layla, kuma cikin duka bai shige watanni ukku ba. Da farko bata kawo komai a ranta ba akan yawan ziyarar da yan uwa na jiki da na nesa suke kawo mata ba, sai da suka fara tambayar inda Layla take da yanda suka kwana biyu basu ganta ba, suna yin tambayar idanuwan su na yawo a cikin gidan kamar zasu iya hangota ta cikin daya daga bangwayen da suke zagaye da dakin.

"Tana lafiya. Alhamdulillah"

Shine amsar da suke samu, sai ko murmushi mai ciwon gaske daga wajen Mami din, tana so tace musu Layla tana makaranta ko dan gujema tarin tambayoyin su, shisa a irin lokuttan take zabar ta mike ta kawo musu abin sha ko ta kawo wani zancen da zai sa su kyaleta, amman sai sun san yanda sukayi suka dawo da zancen akan Layla. Tun tana kuka bayan tafiyar kowanne a cikin su har zuciyarta ta bushe. Duk zuwan bai musu ba sai da suka dinga turo yaran su 'yan matan suna kusan yini a gidan. Haka makota ma da suka fara mata zarya, har mutanen da bata taba sanin da zaman su a cikin unguwar ba.

A lokacin ma cikin Layla ya shiga wata na bakwai, sun fita kenan zasuje awo, ita da Layla da Jabir da zai kaisu, basu karasa fita kwalta ba Layla ta zage gilashin bangarenta tana zura kanta saboda amai daya taso mata. Hakan yasa dole Jabir din yayi parking a gefe ta fito, wahala ma tasha dan batayi aman ba. Sai ruwa da Jabir ya dauko mata na roba ta kuskure bakinta tana kuma wanke fuskarta. Mami ma hankalinta yana kan Layla da ta jigata, tun da rabonta da wasu amai tun cikin na karami, taji Jabir yace

"Da kin karaso ai saiki fi ganin mu da kyau"

Hakan ya sata daga kai ta sauke shi kan matar da bata ga fuskarta ba sai bayanta saboda ta wuce da sauri har tana tuntube, kai kawai Mami ta jinjina suka shiga mota suna tafiya. Har suka kai Jabir na kwashewa matar albarka

"Aikin banza, shisa rayuwar turawa tayi wallahi, babu wanda ya damu da kai ballantana"

Ita dai batace mishi komai ba saboda jikinta da yake a sanyaye. Haka mutane suka dinga shigiwa gidan, wasu da uzurin an kwana biyu ba'a gaisa ba, ko zasu wuce shine suka biyo. Murmushi Mami takanyi, tasan gulmace da tsegumi kawai ya shigo da su, idan basu ga Layla ba ta boye tana daki, lokaci zaizo da zasu shigo gidan kukan duk abinda zata haifa in dai ya taka duniya zai tabbatar da zargin su idan tantama sukeyi. Ta jima da daina gujema kaddarar da ta same su, idan tana boyewa babu abinda zai karawa Layla sai tarin damuwa fiye da wadda take ciki.

Ga duk zuwa awon da zasuyi sai likita ya kara musu kashedi kan kwantar mata da hankali saboda jininta da ya hau, abinda ba'a so a tare da mai ciki. Yan uwanta ma gulmar sukeyi, dan wasu yan unguwa sunyi bata ga laifin su ba, masu dalilin da zasuyi mata uzuri ma basuyi ba, kowa dan yatsa ya daga ma kaddarar da ta same su kamar su din sunfi karfin hakan, kamar su din suna da dabarun kaucewa abinda ya sameta. Dan akwai matar da tana shigowa gidan sun gaisa ta zauna sai ga Jabir shima ya shigo ya gaishe da matar yana wucewa kitchen.

Kallon sani Mami takeyi mata, amman ta rasa inda tasan ta

"Nasan baki gane ni ba ko? Matar Balarabe ce da muka zauna nan baya"

Kai Mami ta jinjina, shekaru wajen tara ba wasa bane ba, kuma ko da can din da suka zauna anan unguwar tasu in ba jaje ko barka ba, babu abinda yake hadasu

"Allah Sarki, shekarun ne da yawa shisa, duk ina yaran, ya wajen Salamatu"

Wata yar dariya matar tayi

"Kowa lafiya, na shigo unguwar ne nake jin rasuwar Bilal, nace aikam zan shigo in muku gaisuwa. Allah yayi mishi Rahma"

Bayan Mami ta amsa tana shirin mikewa kenan dan ta kawo mata ruwa tace

"Allah dai ya kara karemu, ashe haka abubuwa duk suka faru, ga yar wajen ki din nan da akace kina riko ya take da suna ita kuma ta dauko magana, abin ya bani mamaki kwarai..."

Kallonta Mami takeyi, kafin ta iya yin wani tunani Jabir ya fito yana fadin

"Menene abin mamaki?"

Ko ina na jikin shi bari yake da bacin rai, sosai yanzun mutane suke bashi mamaki, yana kuma sake jinjina ma Rayyan da tun da wuri ya gane halayen mutane ya nisanta kan shi da su. Shima abinda yakeyi kenan yanzun, saboda su din basa gajiya da yin abubuwan da zakayi komai dan ka gujewa zama jinsun su

"Jabir"

Mami ta kira, kai ya girgiza mata yana fadin

"Layla! Layla!!"

Yana kallon matar da take ta kifkif da idanuwa cike da tarin rashin gaskiya

"Layla!"

Jabir ya sake kira lokacin da yayi dai-dai da fitowar Layla da take rike da bayanta, idanuwanta na fara sauka akan Jabir da yake takawa ya karasa inda take yana kamo hannunta, bin shi take cikin rashin fahimta harya zo da ita tsakiyar falon yana tsayar da ita a gaban matar

"Ki daina mamaki yanzun, ki gani da idanuwan ki, saiki fita ki sake tabbatar musu idan akwai mai sauran mamaki ya bari, idan suma zasu shigone su ganta su shigo"

Kanta Mami ta sadda kasa tana kai yatsanta a hankali ta share kwallan daya taru a cikin idanuwanta, zuciyarta na wata irin kuna, mikewa matar tayi babu ko sallama ta raba Layla ta wuce. Har lokacin jikin Jabir bari yakeyi. Sakin hannun Layla yayi yana wucewa dakinta da kan shi ya dauko hijabi ya mika mata

"Hamma..."

Ta fadi muryarta na rawa, idanuwanta cike da hawaye, kai Jabir ya girgiza. Zuciyar shi sam ba zata iya dauka ba. Baice abinda Layla tayi bashi da muni ba, amman tsakaninta ne da Ubangiji, a cikin duk tarin mutanen da suke mata surutu, suke nunata da yatsa babu wanda za'a binne su a tare, sanda za'a kaita a rufo a barta da ayyukanta ba lallai su sani ba, addu'ar neman Rahma ma ba lallai bane su bita da ita. Baisan inda tarin mutanen suka shiga ba a lokacin da ta samu makaranta, lokacin da tayi saukar Al'Qur'ani mai girma, duka bai gansu sun shigo tayata murna ko jinjina ma su Mami kan kokarin su ba.

Sai yanzun da kowa yake tunanin sunyi kuskure a rikon Layla, sai yanzun da ita kanta Layla din wani abu mai muni ya sameta, tarin mutanen da basu da masaniya akan kominta sune a gaba wajen yanke mata hukuncin da basuda hurumin yin haka. Yana gab da fara sakawa mutane hannu idan yana gidan suka shigo, baisan me yasa Mami bata binsu da tabarya ba, shi bashida wannan hakurin sam

"Ba zaki kare duka rayuwarki a cikin bango hudu na dakin ki ba Layla, idan baki fita da cikin nan ba zaki fita da yaro ko yarinya. Mutane suna magana yanzun, ba zasu daina magana ba, karki barsu, karki bari su takura ki fiye da yanda kike a takure"

Jabir ya karasa maganar da wani irin yanayi a muryar shi da yasa hawayen da ke cikin idanuwan ta zuba

"Jabir ka kyaleta, me yasa baka da hankaline kai?"

Mami tayi maganar tana kokarin tarbe kukan da yake barazanar kwace mata, hijabin Layla ta karba tana sakawa a jikinta. Zuciyarta na wata irin dokawa kamar zata baro kirjinta. Mami bata hana su ba, tana kallo Jabir ya koma ya daukowa Layla takalmanta, fitar sukayi, daga farkon layin har titi, Layla tana jinta kamar babu kaya a jikinta saboda kallon da mutane suke binta da shi, kamar yanda Jabir ya fadane, ba zata cigaba da boyewa ba har abada, zancen ya rigada ya bazu, gara ta fara koyan yanda zatayi rayuwa da tabon da yake jikinta.

Sanda suka koma numfashi ma dakyar take fitar da shi, har bakin kofar dakinta Jabir ya rakata sannan ya tsaya yana fadin

"Babu hakkin mutane a kanki. Ba zan miki karya ba kin sani, duka rayuwar ki ta duniya ce ta samu tangarda, ba zancen zancen ki ba zai wuce a baku nan mutane ba, amman duk sanda zaki gifta zaki tuna musu abinda yake adane a zukatan sune, bansan al'adun mu na hausawa basawa mata adalci ba sai yanzun Layla, sai da rashin adalcin ya biyo ta cikin gidan mu...."

Wani irin numfashi Jabir yaja, bayason hawayen shi su zuba a gabanta, zai kara karya mata zuciya

"Ba zaki iya gyara tsakanin ki da mutane ba, ki gyara abinda kike da tabbas akan shi, ki gyara tsakanin ki da Allah, sai Ya tausaya miki ya gyara duniyar ki, karki bar su, karki bari su takura ki fiye da yanda kike a takure, kina jina"

Kai ta daga mishi tana goge hawayenta. Sai da yaga ta shiga daki sannan ya juya yana komawa wajen Mami ma da tun da suka fita tana zaune tana wani irin kuka mai cin rai

"Dan Allah ki rage sanyin halin nan Mami, ki daina barin mutane suna bi takan ki akan abinda baya karkashin ikon ki, idan ba zaki iya korar su ba Mami ki daina sauraren me zasu ce suna bata miki rai, dan Allah. Wallahi zuciyata zafi takeyi mun, sosai da sosai"

Cewar Jabir yana ficewa daga dakin saboda bayason ganin kukan da Mami takeyi. Har Abbu ya samu da daren ranar, dan Abbu ba zai manta yanda Jabir ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login