Showing 60001 words to 63000 words out of 150281 words
kwana daya yake da shi kafin jarabawar shi da ita kadai ta rage a zangon. Rayyan kwanciya yayi yana runtsa idanuwan shi da suka fara nauyi da alamun bacci, duk da yamma tayi. Idan baccin ya kwace mishi yasan sai dai wani ikon Allah zai samu ya runtsa da dare. Kuma kwakwalwar shi na bukatar hutun. Akwai tarin abubuwan da yake bukatar saka mata na jarabawar shi ta gaba.
A hankali bacci ya dauke shi da mafarkin Layla kwance a gefen shi da baisan dalilin da yasa ta kutso mishi cikin mafarki ba. Duk da yana wata duniya daban bai hana shi furta
"Mayya..."
Cikin kan shi a duniyar ba.
*
Rayyan suka tsaya jira su dukkan su, shine karshen gama jarabawa, duk sun riga shi. Aisha ma da aka kirata a gidan su dan azo daukarta ca tayi musu zasu taho tare da su Bilal, da yake babu wanda bai san shi ba a gidan, babu kuma wanda bai aminta da shi ba sai suka amince. Ran safiyar asabar duka suka shirya. Bilal yaje ya dauko motar daga gidan abokin Abbu, dan ran juma'a yaje yakai an duba lafiyarta ya kuma zuba mai. Daga gida da suka dauki kayan su makaranta Bilal ya nufa. Yana kallon Rayyan daya bude gidan baya ya zauna, baice mishi komai ba.
Dan tun jiya rabon da suyi magana, daya gaishe shi da safen nan kai kawai ya daga mishi, yan shiru-shirun sunzo fiye da kowanne lokaci, yakan dade Bilal bai gan shi a yanayin nan ba. Yasan ko me zai fada asarar bakin shi zaiyi, ba amsa zai samu ba. Abinda bai sani ba shine rabon Rayyan da ko gyangyadi kwana biyu cur, baccin ranar daya kan samu ya neme shi ya rasa. Duniyar a cunkushe yake jinta. Ga shi jiya ma bai samu ya ga Layla ba sam-sam. Ta zo ma gidan nasu da bata gan shi ba jiya batayi ba, ya sa ran zai ganta.
Watakila fushi take yi mishi tun shekaranjiya, ba zai iya tuna kan me yai balbaleta da fada ba, fadan kawai yake iya tunawa. Har waya da safen nan ya dauka da niyyar kiranta yaji ko ta gama shiryawa sai kuma ya fasa. Zai ganta babu jimawa, a bakin kofar hostel kuwa suka same su ita da Aisha suna ta hira. Bilal ya fita ya saka jakunkunan su a bayan mota. Aisha tsaye tayi cikin rashin sanin inda ya kamata ta shiga ta zauna ganin Rayyan din a baya, ta dauka ita da Layla ne zasu zauna a gaba. Layla ta samar mata mafita da ta bude bayan motar tana shiga. Hakan ya sata bude gidan gaba ta zauna, Bilal ma ya shigo yaja motar.
Sun gaisa dashi da safe, kara gaishe da shi Aisha tayi tana juyawa tace
"Hamma ina kwana"
Kai kawai Rayyan ya daga mata, da yake ta fahimci halin miskilancin shi da mutane da yawa zasu iya dauka wulakanci sai ta juya kawai. Layla kallon shi tayi, yayi kyau sosai sosai cikin farin yadi da ya saka. Yau harda hula, bawai baya saka manyan kaya bane kwata-kwata, yakan dai kwana biyu bai saka ba. Ga dinkin rigar dogon hannune mai links, ta kasa daina kallon shi, kyau yayi mata yau fiye da kowanne lokaci, zuciyarta har wani kumbura take da tarin soyayyar shi da batasan yawan ta ba. Amman inda take Rayyan bai kalla ba, asalima kan shi ya jingina da kujerar motar yana lumshe idanuwan shi.
"Hamma..."
Ta kira, muryarta iya kunnuwan shi, jiya fushin da ta kwana tana yi mishi bai yini ba, son ganin shi ya danne mata komai. Yanayin da har ya saka tunanin ko da gaske ne? Maitar da Mami take karyata cewa ta gada ta bangaren mahaifiyar ta, duk da zuwa yanzun shi kadai dinne yake kiranta da
"Mayya..."
Saboda idan har da gaske bata kasance mayya ba ya kamata ace zuciyarta ta hakure da shi, ya kamata ta sama musu sauki su duka biyun, sai dai kamar yanda batasan lokacin da ta fara son shi ba, haka bata san ta inda zata fara dai nawa ba. Idan ma yaji bai nuna mata alamar hakan ba, son jin muryar shi takeyi da dukkan zuciyarta
"Hamma"
Ta sake furtawa, tana dan kallon su Bilal, hira suke sosai, da alama hankulan su baya kanta. Sake kallon Rayyan da bai motsa ba har lokacin tayi, tun kiran farko da tayi mishi yaji ta, asalima tun daga nesa ya hango ta, ta saka material ruwan toka, sai farin mayafi, yau idanuwanta ya fara hangowa zuciyar shi na tsinkewa, sai dai yana dauke idanuwan shi daga kallon nata ya mayar dasu kan yanda tayi kyau sosai, sai yaji yanayin daya kwana biyu baiji ba, riketa yake so yayi, wani kusanci yake son samu da ita komin kankantar shi. A kwanakin nan biyu da yayi su a hargitse ganinta ya saka shi jin kamar daya riketa koyayane wani abu zai natsa mishi.
Dakyar ya raba idanuwan shi daga kanta yana kallon Bilal da suka hada ido ta mudubin gaban motar, kai Bilal din ya girgiza mishi a hankali, kamar yana san abinda yake tunani, kamar yana son fada mishi karya fara aiwatarwa. Wani irin yanayi zuciyar shi ta shiga lokaci daya, idanuwan shi a bude suke, kuma safiya ce, baisan me yasa yake ganin duhu ba. Tana zagayo ta shigo ya zabi ya rufe idanuwan shi, har wani dumi jikin shi yake dauka da son rike ko da hannunta ne. Ya rasa kalar sabon da yayi haka da haduwar da jikin su yake yawan yi.
Jin Layla tayi shiru yasa shi kara runtsa idanuwan shi yana kokarin fitar da numfashi a tsanake, ba lokaci yake gani ba, banda sautin karar mota da yake nuna alamar sun dauki hanya babu abinda yake ji, sai numfashin Layla da baisan ya akayi kunnuwan shi suka tsinto mishi shi ba, kusan yanajin bugun zuciyar ta ta hakan. Kafin yaji dumin hannunta cikin nashi da yake akan kafar shi. Kamar hannun na da ikon kan shi na budewa ta saka yatsunta a ciki tana dumtsawa, yanayin da yaji har kasan zuciyar shi
"Nagode..."
Ya furta a hankali yana kara dumtsa hannunta, saurin kallon fuskar shi tayi, sai taji kamar godiya yayi mata, amman bata ga alamar ya motsa komai a fuskar shi ba. Da badan wasa da yake da hannunta da ta saka a cikin na shi ba sai ta iya rantsewa da cewar bacci yakeyi. Wata irin ajiyar zuciya ta sauke, tana jin kamar yau akwai abinda yake damun shi fiye da kullum, watakila kuma tunaninta ne kawai. Aisha bacci tayi dan ita sai dai in iskar mota bata fara kadata ba. Ta mudubi Bilal yake kallon su, da alama Rayyan ma bacci yakeyi, Layla kuma ta kwanta a kujerar ne tana fuskantar shi, idanuwanta akan shi kamar a duka duniya babu wani abu da ya taba daukar hankalinta irin Rayyan din yana bacci.
Yanayine da ya sa na wasu dakika Bilal ya manta da tuqi yakeyi saboda zafin da kirjin shi ya dauka. Yana kallo Layla ta daga hannunta da nufin taba fuskar Rayyan din, duk daukarta bacci yake, kamar zare ta gani a gefen fuskar tashi kan kasumbar da ta sha gyara, lokacin da yai saurin damkar hannunta da dayan hannun shi, lokacin kuma da Bilal ya taka motar yana kaucewa karawa wata mota da ta ke tahowa, B Rayyan ba hatta Aisha sai da ta bude idanuwanta tana fadin
"Subhanallah..."
Shima Bilal din duk wata addu'a da tazo bakin shi yi yake. Sun kusan mintina biyu kafin ya samu natsuwa dan ya rage gudun motar sosai. Rayyan kuma hannun Layla daya damqa ya saki yana kokarin saka idanuwan shi cikin nata duk da yanda zuciyar shi tayi wata irin dokawa
"La hawla wala quwwata ila billah"
Ya furta a cikin kan shi ganin kamar ya hada idanuwa da mage, kwayar ce kawai da ta Layla take a zagaye, ta mage kuma a tsaye. Dan runtsa idanuwan shi yayi, yana komawa cikin kujerar ya kwanta yana bata damar sauke nata, tana kula da yanda ba kullum yake kallon cikin idanuwanta ba. Kamar yasan duk idan yayi sai taji wani abu yana fisgarta a cikin su kamar igiyar ruwa. Bata da wasu kalamai da zasu fassara asalin yanda take ji duk idan ya kalleta, ta sha kallon mutane sun nitse a cikin ruwa a fina-finai daban-daban, takan kuma ji a labaran yau da kullum. Bata taba hasaso yanda yanayin yake ba sai lokacin farko da ta fara mallakar hankalinta, lokacin da Rayyan ya saka idanuwan shi a cikin nata.
Sai taji ta tsundum cikin ruwan da batasan da bata ganin farkon shi balle karshen shi, take numfashi ya soma mata barazana, yau ma hakan take ji, dan har bakinta ta dan bude tana fitar da iska daga cikin shi. Zuu din wayarta ya dan taimaka mata sosai, da alama sun dan sake shiga wajen da network ya dawo, dan daga fuskar wayar tayi tana saurin mayar da ita ta kife, ta kalli Rayyan taga ya mayar da kan shi, idanuwan shi a rufe suke kuma, duk da haka zuciyarta kamar zata fito saboda bugun da ta kara, sakonnin duka daga group din
"Sirrin ma'aurata zalla"
Yake fitowa, group din da tun tana hangen su Nanaa da kawayenta sun tattaru a ajinsu ana shewa ana kus-kus a kai cikin yanayin da yai bala'in jan hankalinta har ta fara lekasu, ba sai an gaya mata ba, tasan su Nana sun girmeta, kamar basuyi nasarar da tayi ta samun makaranta da wuri ba. Da yake sun jima suna son yin magana da ita tana sha musu kamshi dan yanayin wayewar su baiyi dai-dai da ra'ayinta ba, har group din ya zama sanadin da take kula su. Ranar da aka sakata wuni tayi da waya a cikin aljihun wando, sai take ganin duk wani sako da yake shigowa ta manhajar WhatsApp dinta kamar wani na kallon ta, kamar wani na kallon kalar abinda take gani take kuma karantawa da bai kamata tayi ba.
Rannan da Ainau Mardiyya da suke kusa da dakin su sanda ta shiga ayi mata kitso suna hirar waya sai taji kamar da ita Ainau take, kasancewarta daliba itama yar aji hudu, sauran yan dakin nasu ma duk yan aji hudune, a cikin su kuma Dina ce takan mata kitso, wata yar asalin garin Kaduna yaren bajju, taji hausa kamar bahaushiya. Hirar illar wayar da tafi amfaninta yawa a zamanin sukeyi, Ainau na fadin
"Yanzun fa zamani yazo da kana iya kokarin ka akan tarbiyar yaranka, kana tsaye ba dare ba rana, da addu'a dan neman kariyar abinda baka gani wayar hannu na warware maka tufka"
Dayar yar dakin su Ainau din Kamila na karbe zancen da
"Wallahi, abin da tsoro, idan baka kai zuciya nesa ba, waya tsaf zata zama halakar ka, ka hana yara waya wani katon banza ya yaudare su da kwadaita musu ita a waje..."
Tabe baki Dina da takewa Layla kitson tayi
"Idan ka basu ma ba tsira kayi ba, kinsan wani group dana gani kwanaki kuwa? Hankalina yayi bala'in tashi, a wayar Gift kanwata nagani...nasa Maman mu ta karbe, amman naki nutsuwa"
Sosai Layla ta takura, tanajin kamar da ita suke, kamar wata ta leka wayarta taga abinda yake faruwa, taga tarin labaran da bata taba cin karo da abinda ya girgiza duniyarta yana rike tunaninta irin kalar labaran ba, abinda take hasashe ne ake nuna mata yanda yake faruwa cikin yanayin da bata taba hangowa ba, ita kuma Allah yayita cikin jerin mutane masu bin kwakkwafi, dole tana sauka gida zata fadama Naana zata fita daga group din idan sun koma makaranta sai a mayar da ita, saboda Mami na da kula, Mami na kuma da bincike, kuma a karo na farko zuciyarta a tsorace take da Mami taga wannan group din.
Rayyan daya kara dumtsa hannunta yana murza yatsunta ya yanke mata tunaninta dan yanayine da taji har tsakiyar kwanyarta, sai yake tuna mata daya daga cikin labaran da ake tattaunawa a kai jiya a group din, wani abu daya tsaya mata a makoshi ta hadiye tana jin wani irin yanayi da bata da fassarar shi yana saukar mata. A haka suka shiga garin Kano, tana jinta sama-sama. Aisha suka fara saukewa suna wucewa gida. Sanda suka sauka, kafafuwanta babu kwari take jinsu, Rayyan kuma bai jirata ba ya shige gida, hada idanuwa tayi da Bilal da yake binta da kallo cikin wani sanyin yanayi kamar yana son karantarta har zuci.
"Ka sha maganin ciwon kai"
Ta fadi tana wuce shi, launin idanuwan shi sun canza, shisa ta gane kan shine yake ciwo, barin shi tayi a tsaye kamar batayi komai ba, kamar bata taba zuciyar shi ba. Tun da ya tashi yake dan jin ciwon kan, amman ita da Rayyan ne suka kara mishi wani sabon ciwon kan, ta kula kamar ko da yaushe, ta kuma gane kan shi yana ciwo. Numfashi yaja yana fitarwa kan shi kamar zai bude, cikin gida ya shige shima, sun fitar da jakunkunan daga baya.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 2, 2020
15
Su Rayyan ne suke makaranta, sune da karatu amman Ayya ce take ramewa saboda tunani. Duk yanda Bilal yake jaddada mata cewa lafiyar su Rayyan din kalau hankalin ta ya kasa kwanciya. Asalin abinda take son ji Bilal ba zaj fada mata, balle kuma tunda suka tafin basu dawo ba sai yanzun da akayi hutun karshen zango. Da kanta ta nemi Hajiya Dije saboda ta samu a shiga tsakanin Rayyan da Layla, harma da Bilal din. Bata da natsuwar binta wani waje ma, tace taje mata ne, tashin farko dubu sittin Ayya ta tura ma Hajiya Dije. Abinda bata sani ba shine wajen shekaru hudu kenan komai ya kwance a gidan Hajiya Dije.
Tunda maigidanta ya dawo da uwargidan shi, ga yara da take dana sanin cusa musu bakin hali tun suna da kankantar su, mazan kusan duk suna da sana'ar su ta kasuwanci da sukeyi. Amman basa bata kudi, idan ta tambaya sai dai suji abinda zatayi da su, idan ta kama su siya mata ne su siya. Komai ta samu kamawa takeyi ta karyar wajen dilla lai ta kai ma Malamai, to yanzun ma tunda ya kamata tana mishi barbade yai mata saki daya, dakyar aka samu aka maida auren, duk wani abu da zai fito daga bangarenta ya daina ci balle ta samo kan shi. Gani takeyi bokan uwargidan tane yafi wanda take bi.
Shisa take ganin Ayya rashin godiyar Allah ne yake damunta, sam matsalarta ba matsala bace ba, kukan dadi takeyi, ta ga Laylar da Ayya take ta daga hankali a kai, yarinya ce mai kyawun gaske, yarinyar da gari banza duk kyan Rayyan din shima sai yayi gaske ya samo me kyawun Layla. Mijinta abinda duk take so shi yakeyi, kaffa-kaffa yake da bacin ranta batare da wani aikin malami ko boka ba. Amman kullum bata rasa abin mita, shisa ta samu saniyar tatse, ranar da sukaje wajen wani Malamin tare kudi ake tsulawa Ayya idan sun tafi Hajiya Dije ta koma ta karbo. Rabonta da zuwa ma Ayya wajen wani Malami na kwarai tun wanda yai mata aiki akan Haris da tambayar duniya da tayiwa Ayya akan zancen aikin sai tasan dabarar da tayi suka fada wata hirar.
Watakila taji tsoro ne batayi amfani da maganij ba, duk kudin da ta kashe a kai. Tunda kwanaki ma da taje gidan ta ga Haris din ya shigo har bangaren Ayya yana gaishe da ita, harma da yar hira sukayi yana shiga Kitchen ya zuba tuwo da tayi, ba zata manta cewa Ayya
"Haris dinne nan?"
Saboda ita bata ga alamar lalacewa a tare da shi ko daya ba, mikewa Ayya tayi yana amsa ta da
"Shine, bari in dauko miki leshin da nake magana"
Murmushi kawai Hajiya Dije tayi, tasan dan karta tayar mata da zancen Haris ne. Wannan kuma duk matsalar Ayya dinne a ganinta. Yanzun dai a sama ta sami saniyar tatse. Danma kudin a wajen bin 'yan tsubbu suke tafiya itama. Duk kan mijinta da take tunanin an janye hankalin shi daga kaine. Ayya kuwa ranar wata zuciya aka kawo mata an yayyanka turbude da magani akace ta wanke ta zuba ruwan a bakin kofar dakin su Rayyan, sai ta ajiye zuciyar tayi mishi girki da ita duk idan yazo, daga shi har Bilal din a tabbata sun ci, to zai zama kamar ta kwato musu tasu zuciyar ce da Layla ta lashe.
Karba Ayya tayi, da fari maganin yayi mata kama da ararrabi saboda kalar shi, kamar ta dandana da ta wanke, sai tayi saurin kauda tunanin daga ranta. Duk irin wannan was-wasin kan bata aiki wani lokacin. Yanda akace tayi haka tayi, zuciyar ta kulle a leda ta saka a fridge, take ta ajiyarta tunda su Rayyan din sunki zuwa, sai a satin da tayi waya da Bilal ya tsayar mata ranar zuwan nasu. Cous-cous ta dafa musu da ya sha hanta da zuciyar da kuma kayan hadi. Aikam ranar tas suka cinye shi da Bilal, danma Bilal ya tsaya taince albasar da take ciki.
Duk da haka taki samun natsuwa, rabin rayuwar ta tun zuwan su jikin window take yinta, ko baccin rana ta daina samu tana runtsawa, dan ko ta kwanta sai taji kamar an gitta, da sauri take dirkowa daga kujera ta leqa ta ga ko Layla ce. Ga Rayyan din da ta dan fara gane kan shi kafin ya tafi ya kara hargitse mata. Ko sau daya bai tako dakin ba, itama da taje ta same su a bangaren su kan shi a kasa suka gaisa, surutun duniya da tayi baice mata uffan ba. Haka ta fita cikin kunar rai, Bilal ne ma yabi bayanta yana lallashinta
"Ayya kinsan halin shi ai, kuma baya ma jin dadi kwana biyu tunda muka dawo, nima shiru-shirun ake tayi mun"
Ya karashe da murmushi, ranta na suya tace
"Dan uban shi dan bayajin dadi sai inta magana yanaji na yaki dagowa balle inyi tunanin zai tanka? Har yaushe zai san ina da muhimmanci mai girma a rayuwar shi Bilal? Ace yafi karfin ya taso yazo ya gaishe dani ko da sau dayane a rana?