Showing 66001 words to 69000 words out of 150281 words
ko idanuwan Rayyan din ne ya saka cikin nashi amman hakan ya gagara. Numfashi Abbu ya sauke kirjin shi na mishi zafi
"Idan son ta kakeyi ka fadamun, itama zan tambayeta sai in muku aure..."
Sai lokacin Rayyan din ya dago yana saka idanuwan shi cikin na Abbu
"Kana son ta?"
Baisan dalilin shi na girgizawa Abbu kai ba, shi bai san me yasa kowa yake tsallen yanke mishi hukunci haka ba akan Layla. Baisan me yasa ba zasu barshi ya dora sunan akan alakar da take a tsakanin su ba, amman yanzun da Abbu ya tambaya sai yake ganin kamar a cikin idanuwan shi yana so amsar ta kasance eh, dalilin da yaji ya dauki Layla ya jefa can wani waje a bayan zuciyar shi, yanayin da baisan ya zai tsaida faruwar shi ba. Numfashi Abbu ya sake saukewa
"Amana ce ita din a wajena, rokon ka nakeyi ka rufa mun asiri, idan baka tayani kare martabar ta ba, karka taba ta, dan Allah Rayyan a karo na farko kayi abinda nace, badan ina so ba, sai dan shine dai-dai"
Shiru Rayyan yayi yana kara sadda kan shi kasa, dakyar Abbu ya iya mikewa, har jiri yakeji yana daukar shi sanda ya kai bakin kofa saboda kan shi da yake sarawa, har lokacin jin shi yake kamar yana yawo a duniyar mafarki
"Abbu..."
Yaji Rayyan din ya kira, da babu taimakon kofar da Abbu ya dafa tabbas da kafafuwan shi sun kasa daukar shi, rabon da yaji sunan shi a bakin Rayyan tun yana dan karami. Na rana daya ya kira shi haka bai taba ba
"Yaa Rabb"
Abbu ya fadi a cikin zuciyar shi, yana jin ko addu'o'in shi akan Rayyan dinne suka fara karbuwa, juyawa yayi yana kallon Rayyan da yake yawata idanuwan shi akan fuskar Abbun, akwai tarin abubuwa da yake so ya fadama Abbu amman kamar an shaqe shi haka yake ji. Idan bai fadi sauran da baisan ta inda zai fara ba, yana so ya fada mishi yanda tunanin zai taba martabar Layla yayi mishi ciwo sosai, yana kuma so ya tambaye shi ko shima a tsakanin shi da na shi mahaifin yana jin irin wannan abin da yake ji.
Yau yana so ya fadama Abbu abubuwa da yawa kamar yanda yake roke shi, ya fada mishi yanda yanzun haka yake ji kamar ana zare mishi rai kallon Abbun da yake, cikin tsokar jikin shi kamar an hura wuta. Amman ya kasa, babu kalma daya da zata iya fitowa daga makoshin shi da yake ji kamar an shaqe. Saiya sadda kan shi kasa kawai, numfashi Abbu ya sauke, ya dauki kiran da Rayyan din yayi mishi a matsayin amincewa da rokon shi.
"Nagode..."
Abbu ya fadi da sanyin murya yana ficewa daga dakin. Yau sai yake jin kamar akwai wata matsala mai girma tattare da Rayyan, matsalar da baisan ta inda zai fara shawo kanta ba. Amman addu'a, yana da yakini a kan addu'ar shi ba zata taba tashi banza ba, zai magana ta fahimta da Ayya, zai gaya mata da ta kara tsananta addu'arta akan Rayyan din, zai kuma yi magana da Mami itama dole. Rayyan ya kalle shi yau ya girgiza mishi kai a tambayar ko yana son Layla. Amman ya rasa dalilin da yasa ya kasa yarda, haka kawai zuciyar shi na mishi rawa akan abubuwa da yawa yau din nan.
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"
Shine abinda yake furtawa yana karawa har ya kai daki
"Allah ka musanya mun kaddarar duk da zaka dora akan yarana, Allah ka fini sanin zuciyata, amman ni inaji kamar kowacce kaddara ba zata dauku a wajena ba in har ta hada da yarana..."
Shine kalaman shi a cikin sujjada, a tsorace yake da lamarin rayuwar gabaki daya. A tsorace yake da kaddarar da yake hangowa kamar tana kusanto yaran shi, kaddarar da yake son amfani da addu'a ya gina katanga a tsakaninta da yaran shi. Domin sune raunin shi, abinda zai taba su zai taba shi fiye da su.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 5, 2020
16
Kwance take a cikin hostel a kan gado, ta lumshe idanuwanta, ba dan gadon yafi nata na gida ba, amman wani irin nishadi take ji yana shigar ta, nishadin da bata da kalaman misalta shi. Ta dauka ita da Zaria sai a mafarki, yanda Mami ta dauki fushi da ita har kasan ranta ta hakura da karatu a Zaria. Ta jigata, ta sha wahala, akan gwiwoyin ta da hawaye cike taf da idanuwanta ta tsugunna tana baiwa Mamin hakuri saboda bata ga abinda tayi mai zafin da zaisa Mami ta daina mata magana ba
"Ban san sau nawa zan jaddada miki MARTABAR MU a matsayin 'ya'ya mata ba kafin ki fara kare taki"
Mami ta fadi tana dorawa da
"Bance ki dubani ba, ki duba kanki da maraicin ki, yanzun mutunci ne ace kuna wannan rike junan ke da Rayyan?"
Hawayen da suka tsiyayowa Layla ta goge da hannu
"Ni dai Mami dan Allah kiyi hakuri, nace ba zan kara ba, na daina, dan Allah kiyi hakuri"
Numfashi Mamin ta sauke
"In zakiyi hankali dai kiyi, dan an Abbun ku ya tambayi Rayyan din yace ba son ki yake ba..."
Duk wani abu da Mami ta fada bayan nan bai karasa kunnuwa Layla da suka toshe da kalaman Mamin na karshe ba, har kuma ta baro gidan bata samu wani nishadi ba sai yanzun da take a kwance. Kwananta hudu da wani irin zazzabi da ya wajigata. Mami bata taba mata karya ba tun tasowarta, amman kiri-kiri ranar ta tsinci kanta da karyata Mamin, saboda karta komawa Rayyan shisa tayi mata karyar da bakin shi yace wa Abbu baya sonta. Bata tsammaci ya sota ba, batama san da gaske ta daga burinta akan shi ba sai da Mami ta fada mata kalaman da taji kirjinta kamar an kunna wuta a ciki.
Kwana tayi tana kuka, da safe fuskarta kamar kwabin alkubus saboda yanda ta kumbura, Mami bata ce mata komai ba, ko wanke-wanke tanayi tana kuka haka ta karasa shi ranar. Kuma yanzun ma da ta tuno kalaman sai da taji wani irin daci ya taso mata yayi tsaye a karkashin makoshin ta.
"Mami sai dai kiyi hakuri, amman ni ba zan rabu da Hamma ba, ko ya rabu dani ni ba zan rabu da shi ba. Mayya ce, amman mayyar shi"
Ta furta a hankali, kalmomin "Mayyar shi" din na zauna mata. Abin ya hade yayi mata yawa, saboda har suka bar gidan Rayyan baya mata magana, baya kiranta ya saka tayi mishi wani abu. Idan daga nesa ya hangota zai kalli wani wajen, ita kuma tsoron Mami yasa ko a waya ta kasa kiran shi. Ranar da zata koma makaranta babu kalar wa'azi da nasihar da Mami batayi mata ba, duk da batasan me Abbu ya fadawa Mami ta yarda tabarta komawa Zaria ba. Amman tana da yakinin yana da alaka da yanda watanni shidda ne kacal suka ragewa Rayyan din ya kammala karatun shi gabaki daya.
A mota wannan karin gidan gaba ya zauna, daga ita har Bilal bai musu magana ba, Aisha ma da suka biya suka dauketa, da ta gaishe da shi Layla bata ga yayi alamar yaji ba ballantana ya amsa, muryar shi take son ji da dukkan zuciyarta, amman yayi shiru, cikin kujera ma ya shige yanda ko wuya ta dan leqa ba zata iya ganin shi ba har suka sauka. Bata gaji ba dan da ta sauka ta zagaya ta bangaren shi tace
"Hamma..."
Gilashin murfin motar ya daga yana jan shi sama ya jingina kai a jiki yanda ko fuskar shi ma ba zata gani ba. Za kuwa tayi karya idan tace abin bai mata zafi ba. Dakyar ta danne hawayen da taji suna shirin zubo mata, duk da kwakwalwar ta na son ta tirsasawa zuciyarta tuno maganar Mami, ta tauna taga ko da gaskiya a ciki taqi yarda, hakan zai iya barazana da zaman lafiyarta fiye da yanda take ciki yanzun. Ko Rayyan baya son ta bai fadawa Abbu ba, bai fada ba, tana da sauran buri akan zai kalleta da fuskar soyayya wata rana, idan ma baiyi ba ya aminta da tarin soyayyar da ita takeyi mishi, ya ishe su.
Wayarta ta dauka da take ajiye a gefe jin sakonnin da suke ta shigowa. Tun a hanya an mayar da ita group daman, duk yanda taso ta daina karance-karance da takeyi sai ta tsinci kanta da kasawa, duk idan Nanaa ta turo mata sai ta karanta. Da kanta tace a mayar da ita tun tana mota, duk da wani abu a kasan zuciyar ta na son nuna mata tarin kuskuren da yake cikin hakan, yanayin da take jine ya rinjayi wancen kashedin. Gara taji da abu daya, duk da kome ta karanta din sai ta dinga hasaso Rayyan a tare da ita, cikin yanayin koma meye yake faruwa a abinda take karantawar.
Mafarkai takeyi a kwanakin nan da suka kara addabarta, kallo daya zakayi mata kaga tsantsar ramar da tayi, sai idanuwan. Amman wuyanta duk kasusuwan sun kara fitowa. Sosai taji dadin shigowa Anisa da suka rungume juna kamar sun shekara basa tare
"Nayi kewar ki"
Cewar Anisa tana kara rungume Layla din, sai kace tunda akayi hutu basa manne a waya da chatting
"Nima haka Allah...tun dazun nake duba hanya"
Layla ta karasa tana sakin Anisa, suka karasa suna zama
"Yunwa nake ji, su Yaya zasu kawoni suka tafiyar su yawo..."
Cewar Anisa, Layla ma najin yunwa ta taso mata, tunawa tayi ko abinci bata ci ba itama, ba yanda Mami batayi ba taqi saboda tana zumudin barin gidan.
"Ko mu dafa indomie? Sai mu siyo kwai?"
Dan shiru Anisa tayi tana nazari kafin ta jinjina kai, Indomie din zatafi musu sauri akan duk wani abu da zasuyi tunani. Sai su dora a risho daya, dayan kuma su soya kwai a kai. Layla ta fita siyo musu kwan, Anisa kuma ta dora indomie din.
*
Sosai yake mamaki idan yaji mutane na hirar wani abu da ya saka su nishadi, ko suna hirar ranakun farin cikin su. Baisan ko farin ciki shine lokuttan da Bilal kan fadi wani abu da zai saka shi dariya ba, ko kuma lokuttan da Layla zata kalle shi kamar duniyar ta babu wani abu da take gani banda shi, ko da ya bata mata raine. Akwai wani yanayi mabanbanta da zuciyar shi take shiga a duka lokuttan, amman yanda ake labarin farin ciki yana saka shi tunani sosai. Watakila shi har yanzun bai san wannan yanayin ba, kullum duniyar a cunkushe yake jinta.
Ko da yaushe akwai wani duhu a cikin kan shi, akwai wani kunci da ya zame mishi abokin zama. Akwai ranakun da yakan samu saukin kuncin idan yana tare da Bilal, yakan samu saukin shi sosai duk idan yana tare da Layla, musamman idan hannun shi yana cikin nata. A kwanakin nan ko zanen da yakan dan samu ya rage mishi cunkoson cikin kan shi ya kasa samun natsuwar yi. Ba karamin kokari yayi ba nakin neman Layla. Ba dan Abbu ko Mami ba, sai dan ita din da kanta, ba zai iya jure ganin Mami ta daketa saboda shi ba.
Har yanzun idan ya rufe idanuwan shi yakan ga marin da Mami tayi mata, zuciyar shi kuma na zafi sosai da hakan. Saboda Layla ne yayi nisa da ita badan wani ba, in dan Abbune babu wani abu da maganganun shi suka kara mishi banda tunzura shi ya kusanci Layla din, a lokaci daya kuma wasu daga cikin maganganun suna nisanta shi da ita. Yanayine da shi kan shi ya saka shi a cikin rudani marar misaltuwa. Ba bacci yake samu ba, shisa tsakanin safiya zuwa wata safiyar yake yi mishi nisa matuka. Idan ya ga Bilal yayi bacci sai ya kwanta akan bayan shi ya kalli ceiling din dakin yana tunanin da ba zai iya cewa takaimaimai na menene ba.
A kwanakin ko sallar daya kan tashi yayi sai jikin shi yayi matuqar nauyi. Bilal dai bai fasa mishi hira ba idan ya tashi, duk da baya iya ce mishi komai. Yana dai jin dadin hirar, fiye da yanda zai iya fada. Saboda ita kadai ce yake ji ta zame mishi katanga tsakanin shi da tabin hankali. Tun sanda ta shigo cikin motar yau da zasu dawo yake jinta a wajaje fiye da zuciyar shi, sai yake jin inda maganganun Abbu suka dauketa suka jefa yana budewa. Zai rantse yana jin idanuwanta na yawan neman fuskar shi kamar zasu huda kujerar da yake a kai su leqo shi. Bayan sun sauka ma haka, yana jin yanda take kokarin yi mishi magana.
Sai take kara mishi wahalar da yake ciki, saboda tana yi kamar ita ka dai take azabtuwa da nisan da sukayi da junan su. Duk yanda yake daurewa sai da tayi mishi magana
"Hamma..."
Kawai ta furta sai da tsikar jikin shi gabaki daya ta mike, komai yana neman kwance mishi, shisa ya daga gilashin motar. Jikin shi har bari yakeyi da son fita daga motar ya riketa a jikin shi, so yake ya zagaya hannuwan shi ya riketa dam, yaji duminta ko zai nutsar da hayaniyar da take cikin kan shi. Amman babu wannan damar, zaiyi duk kokarin da zai iya na ganin damar bata samu ba. Sanda suka karasa gida har wani numfashin wahala yake saukewa. Kayan su ma Bilal ne ya shigar musu da shi.
Basu huta ba suka fara share share, har wankin su labule sai da Rayyan din yayi. Yanajin Bilal na fadin
"Kabari a bayar a wanke mana"
Bai saurare shi ba, saboda yana son yin wani abu da zai rage mishi tunani. Sanda ya gama duk wani aiki da zai iya takalowa kan shi har azahar ta kusa, yanayin wanka ya fita yayi sallah ya dawo. Bilal ya sai musu biredi a hanya saiya dafa musu shayi, shi Bilal din yana zaune kan gado ya bude laptop din shi, Rayyan kuma yana zaune akan kujera da kofin shayin da yayi mishi zafi a hanny yana hurawa a hankali da iskar bakin shi cikin son ya huce.
Wani series film ne Bilal din yake kallo tun suna gida mai suna "Suits". Shi kallo ba damun shi yayi ba, idan Bilal ya saka wata rana sunayi tare, tunda ya fara sukan kalli wasu episodes din tare. Duk dai inda ya samu Bilal din na kallo shima dorawa yakeyi. Yanzun ma idanuwan shi ya natsa kan screen din laptop din suna kallon.
"Trevor din nan ba abokin Mike bane wai?"
Rayyan ya tambaya yana kurbar shayin shi, juyawa Bilal yayi saboda yana son tabbatar da cewa Rayyan din magana yayi bayan satikan daya dauka yana azumin yin maganar.
"Abokin shi din nan da suke daki daya"
Rayyan ya sake fadi ganin kamar Bilal bai gane tambayar shi ba, idanuwa Bilal ya runtsa yana bude su akan Rayyan. Baisan yana rike da wani numfashi ba sai yanzun daya sauke shi. Sosai abinda duk yake damun Rayyan din yake ci mishi zuciya. Yayi tambayar duniya Rayyan yayi banza ya kyale shi, har fushi yayi ya gaji ya sauka da kan shi. Yakan dauki kwanaki biyu batare da yace komai ba, amman bai taba daukar wannan kwanakin shiru haka ba.
"Dan Allah Hamma karka sake tsoratani haka... Ko ba zan iya taimaka maka ba, ko banda maganin damuwar ka idan ka fadamun zan saurara. Wasu lokuttan kana bukatar wanda zai saurari matsalarka ne saika sami saukin ta..."
Idanuwan Rayyan din na kan laptop har lokacin yana kuma shan shayin shi a nutse, yaji duk wani abu da Bilal ya fadi
"Shine, abokin shin nan ne"
Ya fadi maimakon amsa Bilal din, kai Bilal ya jinjina mishi, sanin in dai ba wannan hirar da Rayyan ya fara ba, sam ba zai saurari wata daban ba.
"Shine fa..."
Ya tabbatar ma Rayyan da ya girgiza kai
"Yasa bana son mutane, har kasan raina zan yafe komai banda cin amanar mutanen dana yadda dasu"
Dariya Bilal yayi
"To a duniya waye zaici amanar ka Hamma? Da wa ka yarda?"
Dan jim Rayyan yayi, akwai tarin abubuwa da mutane suke da su da bayaso sam shisa yake zabar kadaici akan tarayya da su
"Kuma idan wani yaji kana maganar mutane saiya dauka ba daga jinsi daya kuka fito..."
Kafadu Rayyan ya dan daga
"Kai..."
Ya furta yana sa Bilal kallon shi
"Na yarda da kai da Layla..."
Rayyan yayi maganar muryar shi can kasa yana dorawa da
"Sai Abbu da Ayya"
Duk yanda bayajin kusanci da su, yana jin ya yarda dasu, basu taba cutar da shi ba, basu taba mishi karya ba. Shisa ya yarda dasu, bayason karya da dukkan zuciyar shi, ba kuma ya son cin amana kamar yanda ya fadi. Yanzun bashi Trevor yaci amana ba, amman har ran shi yake jin abin, mu'amala da mutane babu komai a cikinta sai wahala.
"Mu din kenan ba za'a yafe mana ba?"
Bilal ya tambaya yana murmushi, kai Rayyan ya girgiza mishi, yana saka idanuwan shi a cikin na Bilal din
"Ba zai yafu bane..."
Yanayin da yayi maganar na saka wani abu tsirgawa Bilal din. Shirune ya ziyarci dakin suna maida hankalin su kan film din da suke kallo, wannan karin kowa da abinda yake tunani a cikin kan shi.
*
"Hamma..."
Layla ta fadi cike da farin ciki tana zagaya hannuwanta a bayan shi ta rike shi. Idanuwan shi Rayyan ya lumshe yana jin wani irin yanayi da ba zai misaltu ba, sosai a watanni shiddan sa suka wuce mishi a hankali yaso nisanta da Layla, amman ya kasa. Yana bukatar ta a kusa da shi in har zai sami natsuwar kammala jarabawar zangon. Satin farko da suka dawo makaranta ta zo wajen shi, inda ya saba zama. A gefe ta zauna batare da tace mishi komai ba. Sun kai mintina arba'in a zaune kawai. Shirune da yake cike da ma'anonin da basa bukatar kalamai. Shirune daya samar mishi da natsuwar da baiyi zato ba.
Da zata tafi, jakar shi ya bude ya zaro jacket yana mika mata, babu musu ta amsa ta saka a jikinta. Ita kanta ta samu natsuwa, da gangan a ranar ta saka doguwar rigar. Tana son ko yaya ne ta ga wani kusanci da yake a tsakanin su tunda baya mata magana. Haka taci gaba da zuwa su zauna shiru kawai, a ranakun da