Showing 114001 words to 117000 words out of 150281 words

Chapter 39 - MARTABARMU HAUSA NOVELS LUBNA SUFYAN .txt

23 Nov 2025

3944

lokacin daya dauka a tsaye ba, yasan dai kafafuwan shi da kansu suka gaji suna kaishi kasa, da yake akwai kafet cike da dakin nan ya kwanta shima. Ciwo yake ji, ciwon da yake bukatar lallashi ko ya yake, kuka yake nema watakila idan yayi irin wanda Layla takeyi zai samu sauki. Abu daya ne yake mishi yawo, dan yace ba zai auri Layla ba baya nufin yana son ta kusa da wani, balle ace wanin ya kasance Bilal, mutuwa kawai zaiyi ya tabbatar yanzun. Dan kirjin shi kamar an zauna a kai haka yake ji. Me yasa Bilal zai mishi haka? Ya kasa samun wannan amsar, idan kuskure zaiyi me yasa sai akan Layla?

Duk da dazun yana jin surutun da yake yi a bakin kofa, ya zabi yin kamar baiji shi bane ba. Shisa bayason juya kalaman, baya son yin wani tunani da zai hada da yiwa Bilal uzuri, abinda yayi mishi ba zai yafu ba, ba zai iya yafe musu ba daga shi har Layla. Har cikin kasusuwan jikin shi yake jin hakan, yana so suji ciwo kalar wanda shima yake ji. Amman hakan baya nufin yana son ganin Layla a tare da Bilal, yama Abbu zai fara cewa Bilal ya auri Layla. Yana tunanin baccine ya fara fisgar shi, dan kiran sallar farko da akayine ya saka shi bude idanuwan shi dakyar yana tunanin inda yake.

Kafin komai ya dawo mishi yana saka shi dafe kirjin shi da yake ciwo. Dakyar ya iya mikewa, ko ina na jikin shi ma ciwo yakeyi. Abbu da yake kwance ya kalla, sai da yaga ya juya kwanciya sannan ya fice daga dakin. Fitilun gidan duka a kunne suke yau. Dakin su ya nufa, yana shiga zuciyar shi tayi wata irin dokawa da yanayin yanda yaga an fiffido kaya, tun bai karasa cikin dakin ba kafafuwan shi suke rawa, kan tebir din shi yaga takarda a ajiye, ya dauka yana budewa, da daya daga cikin fensiran zanen shi akayi rubutun da yake ganin yana rabe mishi biyu, saida ya runtsa idanuwan shi ya bude su tukunna ya iya karantawa da muryar Bilal a zuciyar shi

"Nayi kuskure na sani, ba zan kara shiga tsakanin ka da Layla fiye da yanda nayi ba Hamma, ba saika yafe mun ba, dan Allah ita ka duba zuciyarka, nasan akwai wajen da zai iya yafe mata, ka yafe mata. Ka dora duka laifin a kaina. Nagode da tarin kaunar ka, ka kula da kan ka, ka kula da Ayya"

Ya karanta wasikar yafi sau ashirin kafin asalin ma'anar ta ya zauna mishi, cikin wani irin tashin hankali ya fito daga dakin, tun daga bakin kofar yake fadin

"Ayya!"

Yana kara kwala mata kira harya karasa bakin kofar dakinta inda suka hade saboda daman ba bacci takeyi ba, kiran shi ne ya sata mikewa tana tahowa da sauri, ko da yana yaro kome yake bukata bai taba mata irin wannan kiran ba, yana ganinta kafafuwan shi na kasa daukar shi

"Ayya ya tafi... Ayya tafiya yayi... Bilal tafiya yayi ya bar ni... Dan ba zan yafe mishi ba sai nace ya tafi? Me yasa zai tafi? Ina ya tafi Ayya?"

Duka zancen shi a baibai take jin shi, jijjigata Rayyan ya fara yi, saboda yasan babu inda Bilal zaice bai fada mata ba, gara ta gaya mishi ya bishi ya dawo da shi.

"Ki fadamun inda ya tafi Ayya... Kinga ni me yace mun..."

Wasikar Ayya ta karanta, fahimtarta ne yake mata wahala saboda babu yanda Bilal zai tafi wani waje bata sani ba, balle ace irin wannan tafiyar, ture Rayyan tayi tana nufar dakin su ya rufa mata baya, kayan Bilal ne tagani a zube, batayi magana ba ta sake fitowa tana jin Rayyan na biye da ita har cikin dakinta inda ta dauki wayarta, tana mamakin yanda komai yayi mata shiru, lambar Bilal ta kira a kashe, duka lambobin shi a kashe, Rayyan ta kalla da shima yaji a kashe ne, kai dai kawai yake girgiza mata, duniyar na kara hargitse mishi, runtsa idanuwan shi yayi yana sake bude su da wani irin matsananincin tsoro daya ziyarce shi

"Ayya dan Allah..."

Cewar Rayyan yana dafa bango ya sulale kasa, a cikin daki yake, amman duniyar duka yake ji tayi mishi fili, babu kowa a cikinta sai shi kadai, bai san inda zai nufa batare da Bilal ba

"Ayya ki ce mun bai tafi ba, dan Allah kice ya dawo"

Rayyan yake fadi yana jin iska ta daina kaiwa cikin kan shi, kafin wani irin duhu ya rufe mishi idanuwa ruf, yana saka Ayya tsugunnawa ta riko shi kafin ya karasa kaiwa kasa, kan shi a jikinta yake da wani nauyi da batayi zato ba, nata kan ta dora a na shi, tunda take bata san akwai tashin hankali makamancin wannan ba, a wahalce ta dago, muryar da zatayi amfani da ita wajen neman taimako take nema ta rasa yau.

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 1, 2021.

27

Ko sallamar Abbu daya dawo daga masallaci kan shi tsaye ya nufo bangaren ta bataji ba. Zuciyar shi na wata irin dokawa ganin ta rike da Rayyan din

"Rayyan..."

Ya kira muryar shi na fitowa yar karama saboda tsoron da yake ciki.

"Me ya same shi? Me ya faru?"

Saboda ya ga fitar Rayyan din daga dakin shi, kuma lafiya kalau ya gan shi. Baisan me yake a kwance haka kamar gawa ba. Ayya da sai lokacin hawaye masu zafin gaske suka zubo mata ta dago tana kallon Abbu, bakinta take so ta bude tayi magana amman ta kasa, saboda zafin da zuciyarta takeyi. Ta dauka raba soyayyar Abbu shine abu mafi daci da zata dandana a zaman duniyarta gabaki daya. Saboda Abbu ne komai nata, sai yanzun da take tunanin inda Bilal ya nufa a cikin duniyar da babu aminci, a rayuwar da naka ma da wahala ya taimaka maka balle wanda baka sani ba.

Kafafuwan Abbu har rawa yake sanda ya kara bandaki ya dibo ruwa ya dawo. Da kan shi ya tsugunna yana dibar ruwan a hannun shi ya shafama Rayyan a fuskar shi, sai da yayi hakan kusan sau biyar sannan Rayyan din yaja wani irin numfashi mai nauyi yana mikewa gabaki daya

"Bilal"

Ya kira daga lungun zuciyar shi yana kallon Abbu

"Abbu tafiya yayi... Bilal tafiya yayi"

Cike da rashin fahimta Abbu yake kallon Rayyan din, kafin ya maida duban shi kan Ayya da ta saka fuskarta cikin tafukan hannunta tana wani irin kuka marar sauti, bayani yake so wani yayi mishi yanda zai fahimta. Dube-dube Rayyan yayi yana dauko takardar da Bilal ya bar mishi da take can gefe ya mikawa Abbu, sai da ya karanta babu adadi kafin kalaman su zauna mishi. Baiyi magana ba ya mike tsaye, aljihun shi ya laluba yana zaro wayar shi da sabo ya saka shi daukarta ya zira bayan yayi alwala zai fita masallaci.

Jikin shi babu inda baya bari, dakyar ya iya saka lambobin sirri ya bude wayar. Sakkoni ya gani da hannun shi ya dangwalo batare da yayi niyya ba. Ganin sakon Bilal a sama ya saka shi saurin budewa:

"Kayi hakuri Abbu, ka yafe mun dan Allah, watakila zan samu sauki a duk inda rayuwa zata jefani. Ka yafe mun ban rike amanar da ka bani ba, ban kula da Layla yanda nai maka alkawari ba. Nagode da karbata da kayi,  nagode da yanda ban taba jin maraici a karkashin kulawar ka ba. Ina fatan nisan da zanyi ya saukaka muku komai"

Sosai Abbu yake jin kan shi na sarawa

"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"

Ya furta yana saka Rayyan saurin fadin

"Menene Abbu? Ya fada maka inda yaje?"

Ya karasa yana mika hannu ya karbi wayar da Abbu ya miko mishi, karanta sakon yakeyi wani abu na tattarowa yayi mishi tsaye a kirjin shi, dago idanuwa yayi yana kallon Abbu cike da wani yanayi

"Amana ka bashi Abbu? Me yasa?"

Saboda bai ga dalilin da zai sa Abbu yace ya bashi amanar Layla ba, sun san yanda Bilal yake, su dukan su kowa yasan raunin Bilal,yanda bashi da wani aiki sai kula da kowa, furta kalaman ba zaiyi komai ba sai dora ma Bilal din wani nauyi da Rayyan bayajin Abbu ya fahimta

"Abbu ko bakace ba, ko baka furta da bakin ka ba Bilal zai kula da ita da duka zuciyar shi, me yasa ka dora mishi nauyin nan? Kaga ya tafi, saboda yana tunanin ya kasa sauke nauyin amanar daka bashi ya tafi... Kasa ya barni"

Yanda Rayyan din yake magana kamar ba a cikin hayyacin shi yake ba, wanda zai dora ma alhakin tafiyar Bilal yake nema, bai sami kowa ba sai Abbu a yanzun. Dube-dube yakeyi ganin Abbu ya sadda kan shi kasa ya kasa cewa komai, har saida ya hango wayar Ayya sannan.
Idan Bilal ya turoma Abbu sako, tabbas itama yasan ya tura mata, watakila ya fada mata inda zashi ita. Yana dauka yaga ko password babu ita, dan haka kanshi tsaye wajen sakkoni ya shiga, ya kuwa ga Bilal din ya turo mata itama:

"Ki yafe mun Ayya, zanyi kewar ki da yawa"

Dariya Rayyan yayi da bata da alaka da nishadi, saboda ko shi zai fita duk yanda magana mai tsayi bata hadasu da Ayya, iya abinda zai tura mata kenan. Bai taba sanin Bilal bashi da hankali ba sai yau. Wayar ya ajiye gefe yana samu ya mike

"Ina zaka je?"

Abbu ya bukata, amman Rayyan din bai kula shi ba ya wuce. Tsintar kafafuwan shi yayi da bin Rayyan din, kafin shima ya tafi, jin takun Abbu a bayan shi ya saka shi juyawa

"Abbu ba inda zanje, ka koma dan Allah... Ba inda zani"

Ba don ya yarda da kalaman Rayyan din ba, ya dai yi tsaye ne har sai da ya daina ganin Rayyan din da ya nufi dakin su. Kayan da Bilal ya baza ya fara harhadawa, watakila yabar wani abu da ko yane zai nuna alamar inda ya nufa, amman harya gama hadasu baiga komai ba. Gefen gadon ya zauna yana rasa kalar tunanin da ya kamata yayi, kafin wani abu cikin kan shi ya fada mishi baiyi sallar asuba ba. Alwala kam dan sabo ne shisa ya cikata dai-dai. Lokacin daya idar da sallah, bai san ta inda zai fara addu'a ba ko abinda zai roka, kawai yana rokon Allah Ya duba halin da yake ciki ya karbi sallar da yasan bashi da wadatacciyar nutsuwa a lokacin daya gabatar da ita.

Baisan iya lokacin daya dauka a zaune ba, rurin da wayar shi takeyi ce ta dawo da shi daga duniyar tunanin da yakeyi. A hargitse ya mike yana rasa inda zai gano wayar, har ta yanke tana sake daukar ruri

"Dan Allah ina dubawa ne Bilal, nasani, ni nasan babu inda zaka tafi ka barni"

Rayyan yake fadi yana cigaba da neman wayar kafin ya juyo ihunta cikin jakar shi da ko budeta baiyi ba. Lalubo wayar yayi, kafin ya daga ta sake yankewa, budewa yayi yana kallon lambar hadi da nazarin inda ya taba ganin ta, ko ma a ina ne yasan lambar, kafin a sake kira, bai tsaya jira ba ya daga wayar yana karawa a kunnen shi

"Hamma..."

Muryar Aisha ta daki kunnen shi tana saka zuciyar shi matsewa a cikin kirjin shi, kafin ya amsa ta dora da fadin

"Hamma ina Nawan? Sakon shi nagani yanzun, bansan ko ya yarda wayar bane, saboda na kasa fahimtar duka zantukan da yakeyi"

Runtsa idanuwan shi Rayyan yayi, akwai wani yanayi tattare da muryar Aisha da yake kara bude bangarori da dama a cikin zuciyar shi

"Dan Allah ka fadamun...kai mun magana"

Sai da ya bude idanuwan shi sannan ya iya cewa

"Ina kike tunanin idan Bilal ya bar gida zai je?"

Ta kusan mintina uku kafin ta amsa shi, muryarta na fitowa a karye

"A watan nan yana yawan maganar kasancewa a wajen da kowa bai san shi ba, yana fadin Lagos ne kawai zakaje ka bace bat... Ban sani ba, ban san me yake faruwa ba, me yake faruwa Hamma? Me yasa zai tafi?"

Ta karasa maganar ne da alamar kukan da ya kwace mata, ba shi da amsar da zai bata, ba kuma shi da wasu kalamai da zai tausheta dasu, shima yana bukatar lallashine

"Ina zai tafi ya barni? Ta ina zan fara?"

Wani irin numfashi take saukewa kamar wadda aka shaqe

"Zan kiraki"

Rayyan ya fadi yana sauke wayar daga kunnen shi, dan yaji alamar zata kara hargitsa mishi lissafi ne. Yana da abubuwa da yawa a gaban shi. Mikewa yayi yana saka wayar a aljihun shi, sai da ya karasa bakin kofa sannan yayi tunanin saka takalma a kafafuwan shi, tashin hankali bai barshi yaji kasar da yake ta takawa ba yau. Yana fitowa daga daki yaci karo da Abbu

"Abbu zan duba a tasha, ina motocin Lagos suke lodi? Aisha tace Bilal yana maganar zuwa can ne"

Kai Abbu yake jinjina ma Rayyan, gabaki daya ya rasa abinda zaiyi tunani. Duniyar ta birkice mishi, yaran da yake tunanin yana duk wani kokari da yake karkashin ikon shi dan kare sune yake kallo yau kaddara na aikinta a kan su babu abinda zai iya. Bilal ne ya dauki kafar shi yabar gida yau, Bilal da gabaki daya rayuwar shi zagaye take da tasu, shine yau ya nufi inda baisan kowa ba, ya ture komai ya tafi saboda yana tunanin yayi musu wani laifi. Wani irin tsoro Abbu yake ji yana shigar shi, Rayyan yake kallo, yana tuna kalaman da yayi mishi jiya na yabar gida

"Ko da zan taba ce maka kabar mun gidana, karka tafi ko ina, kalaman ba zasu taba fitowa daga zuciyata ba"

Abbu ya fadi yana dorawa da

"Bari in dauko mukullin mota sai mu tafi"

Anan inda yabar Rayyan ya dawo ya same shi, sun karasa wajen motar ne Yaya Ayuba ya shigo, ko gaisawa ba suyi ba ya fara da tambayar

"Lafiya? Ina zaku je da sanyin safiyar nan?"

Abbu na bude murfin mota ya amsa shi

"Bilal ne ya bar gida, Rayyan yace kamar Lagos ya nufa. Shine zamu duba a tasha mugani"

Karasawa Yaya Ayuba yayi yana karbar mukullan motar daga hannun Abbu batare da yace komai ba. Shiga sukayi, Rayyan na bude gidan baya ya shiga. Da yake Yaya Ayuba yasan duk tashoshin da motocin Lagos suke lodi. Tunda kafin ya samu budin hawa jirgi idan tafiya kudu ta kama shi motar hayar yake bi. Rayyan ba tuqi ya iya ba, amman gani yake kamar Yaya Ayuba baya taka motar da sauri, saboda so yake kawai su karasa yaga Bilal din yaji dalilin da zai sa ya fara tunanin barin su.

Kudi Kawu Ayuba ya bama cikin yan kamasho na tashar, kafin kace wani abu an dauko musu wani babban littafi da jerin sunayen mutanen da suka hau motocin Lagos daga daren jiya zuwa wayewar gari, motocin safe. Amman ko daya babu sunan Bilal a ciki, duk da Rayyan yaki aminta, wanda ba shi ya duba ba da kan shi sai da ya karba ya sake dubawa, tashoshi suka dinga bi har wajen karfe tara na safe, saboda duk inda sukaje sai sun tsaya an duba list sannan suke barin wajen. Suna hanyar nufar wata tashar da akayi musu kwatance, wayar Rayyan ta fara ihu, bai bi ta kanta ba harta yanke, saboda wani abu na fada mishi ba Bilal bane ba.

Sake kira akayi, ko waye ma bai hakura ba a karo na biyu, ya sake kiran a karo na uku

"Rayyan ba wayar ka bace take kara?"

Yaya Ayuba da yake tuqi ya tambaya, Rayyan din bai amsa shi ba, dan daga jikin shi yayi yana zaro wayar daga aljihun shi, dubawa yayi yaga ko Aisha ce, dan bashi da wata magana da zai fada mata, da akwai daya kirata kamar yanda yai mata alkawari. Wata lamba ce yagani daban, karamin tsaki yayi yana shirin saka wayar a silent kar a dame shi aka sake kira, dagawa yayi ya kara a kunnen shi yana fadin

"Waye?"

A hasale, ta dayan bangaren aka furta

"Daga tashar Mass ne, mun dauki lambar cikin lambobin da daya daga cikin fasinjan da motar su ta tashi karfe hudu na safiyar yau daga nan Kano zuwa Lagos ne mai suna Bilal Abdullahi Dikko..."

Zaman shi Rayyan ya kara gyarawa yana kai hannu yana wuyan rigar shi da haka kawai yaji kamar ya shaqe shi

"Ni ne, ina Bilal din?"

Ya furta a kagauce, dan jim yaji anyi cikin yanayin da ya saka shi fadin

"Hello, ina Bilal din? Wacce unguwa tashar taku take?"

Yana kallon Abbu ya juyo da jikin shi gabaki daya daga gaban motar yana fuskantar shi

"Bilal ne ya bada lambata a tashar shine suka kira ni"

Ya tsinci kan shi da fadama Abbu daya sauke wani numfashi da baisan yana rike da shi ba, Rayyan kuwa hankalin shi ya mayar kan wayar jin har lokacin ba'a kara cewa komai ba, ya bude baki zai magana yaji muryar mutumin ta daki kunnen shi da wata iska mai karfin gaske

"Sun sami hatsari ne..."

Cikin wata irin murya da Rayyan baisan daga inda ta fito ba ko yanda akayi ya iya motsa labban shi yace

"Hatsari? A ina? A ina? Suna ina yanzun?"

Wannan karin iskar yake ji tana kadawa a ko ina na jikin shi da yayi wani irin sanyi na ban mamaki, baya tunanin ya fahimci abinda aka fada din, saboda kunnen shi yaji daga wajen

"...Babu wanda ya fita a motar, da tankar mai suka hade..."

Abinda aka fada kafin nan da bayan nan duk bai jisu ba, iya inda yaji din ma bai fahimta ba shisa ya mikawa Abbu wayar

"Ban gane me yake fada ba Abbu, kaji me yace"

Abinda mutumin ya fadama Bilal shi ya sake maimaitawa Abbu da wayar ta subuce daga hannun shi yana furta

"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"

Yana sake maimaitawa ko ina na jikin shi na bari, duniyar gabaki daya tana hargitse mishi

"Menene? Me ya faru?"

Yaya Ayuba yake tambaya saboda yanayin Abbu din duk ya hargitsa shi, shisa ya sauka daga kan titi yana yin parking din motar, wayar Rayyan da take jikin Abbu ya dauka, kiran ya yanke. Bai bi takan su Abbu ba ya sake duba lambar da yake itace kan kiran karshe da ya shigo, sau hudu yana kira duk ana ce mishi busy alamar ana kira da layin, sai ana biyar tukunna ta shiga

"Ina kira akan Bilal Abdullahi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login