Showing 57001 words to 60000 words out of 150281 words
yayi kamar zai shaqe jin Rayyan din na ma sauro masifa
"Dan ubanka idan sha zakayi ba zaka sha ka wuce ba, sai kana mun ihu a kunne"
Yanzun ma dariya ya tsinci kan shi dayi. Yana karasawa dakin. Bacci Rayyan yakeyi akan tebir, ko tunanin ciwon wuya bayayi. Cikin dakin sosai ya shiga, ya dauki maganin sauro na fesawa yana dan fesa musu saboda Rayyan din. Hannu ya saka cikin net din yana janyo dayan pillow din, ya mayar ya gyara. Dan bubbuga Rayyan din yayi daya bude idanuwan shi da suke cike da bacci
"Ka sa pillow hamma, wuyanka zaiyi ciwo"
Karbar pillow din Rayyan yayi yana ajiyewa ya mayar da kan shi ya dora, idanuwan shi ya lumshe saboda baccin da yake cikin su, sai yakejin kamar yayi kwanaki baiyi bacci ba. Wani irin numfashi Bilal ya sauke yana jinjina al'amarin su. Kafin ya fice, dan shima hamma yakeyi, idanuwan shi cike suke da bacci, hankalin shine ba'a kwance ba sai yanzun.
*
Zai iya cewa tunda safe yake tashi yayi wanka, wajen karfe hudu na safe wasu lokuttan. Yau ma da kan shi ya dora ruwa a kettle yaje ya sirka ya tashi Layla da ta dinga turo mishi baki kamar zatayi kuka. Duk da yasan babu mai fitowa sai da ya tsaya ta wajen hanyar bandakin har tayi wanka ta fito. Lokacin na shi ruwan yayi zafi, da duka kayan shi har wanda zai sake ya shiga bandakin. Yana fitowa ya tsoma wanda ya cire a wani bokitin yana zuwa ya wanke su. Alwala ya daura, saida ya kwankwasa dakin ganin Layla ta saki labulen, muryarta da alamar bacci ta amsa shi.
Hakan yasa shi ya shiga, ya sake komawa ta kudundune cikin bargo. Kai kawai Rayyan ya girgiza. Bayason jikin shi ya bushe shisa ya shafa mai, turaruka ya fesa, yana jin shi a dai-dai. Har wani shiru yake ji cikin kan shi babu wata hayaniya saboda baccin daya dan samu. Share dakin ya karayi yaji kamar ya taka kasa. Zuwa lokacin har anyi kiran sallar farko, masallaci ya fita, kafin a tashi sallah zai samu yayi raka'a biyun da yake sunna mai karfi kafin asuba. Ko da aka idar da sallar asuba ya dade a zaune cikin masallacin, ba lazumi yakeyi ba ko wani abu, kawai lokutta da dama yakan samu natsuwa a cikin masallaci.
Wani lokacin kuma kamar ana mintsinin shi haka yake so ya idar da sallah ya fita, shisa baya wasa da ranaku irin na yau. Sai da ya gaji da zaman sannan ya tashi ya fita. Dakin su ya koma, karfe takwas da rabi yake da darasi, yana nan zaune yana dan dudduba wasu abubuwan da bai fahimta ba har takwas saura, yana da biskit, da shayi ya hada yana cikin shane Hindu ta bude ido, tafi mintina biyar kafin tace
"Hamma...ina kwana"
Sai da ya ajiye kofin da yake hannun shi sannan ya amsa da
"Ya jikin ki?"
Taji sauki sosai, daman kwana biyun farko sunfi wahalar da ita
"Naji sauki..."
Ta furta a hankali, cigaba da shan shayin shi yayi harya gama
"Ina da lecture da safen nan"
Tashi zaune Layla tayi
"Nima haka... Karfe tara, sai mu wuce tare"
Kai Rayyan ya jinjina
"Zaki iya zuwa?"
Nade net din tayi tana sauko da kafafuwanta daga kan katifar
"Eh mana..."
Bai mata maganar taci wani abu ba, tunda yasan daga ita har Bilal basa iya cin abinci da safe haka. Shikam ko da asuba ne zaici, sai dai in bayajin yunwa. Iya abinda zai tafi dashi na ranar ya harhada ya dauko jakar shi yana kara shiryata ya saka a ciki. Ta riga da ta sake kayanta sanda ta fito, ta mayar da wancen cikin ledar da tazo da ita. Mayafin da ta ajiye akan gado ta janyo, doguwar rigace ta atamfa, mikewa Layla tayi tana duba ledar ta dauko dankwalin rigar ta ajiye. Ta karasa ta dauki ledar ruwa, fuskarta da bakinta take son daurayewa. Anan bakin kofa ta tsaya, tana jin idanuwan wani da batasan waye ba a cikin gidan yana kallonta, ko daga kai batayi ba harta karasa ta koma dakin.
Dankwalin ta daura tana rataya mayafin a kafadarta
"Muje?"
Ta cewa Rayyan, ba kwalliya bace a fuskarta, har lokacin idanuwanta da alamar bacci, amman zuciyar shi dokawa take kamar zata fito waje. Sam ya rasa yanda zaiyi da abinda yake ji akan Layla yanzun, bayason yanda take birkita mishi lissafi haka. Tare suka fito, jan dakin kawai yayi, idan Bilal ya fito ya rufe, yana da mukulli a jakar shi. Baibi takan wasu cikin yan gidan da suke ta binsu da kallo ba har suka fice daga gidan
"Hamma kana sauri"
Layla ta fadi, juyawa Rayyan din yayi, ya kamo hannunta, suka taka zuwa titi, saboda ita yau zai hau abin hawa da safe zuwa makaranta, saboda kuma bata da lafiya.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 1, 2020
14
Kwance yake yana juyi. Maganganun Bilal ne suke mishi yawo, duk idan ya zauna haka kawai sai su dinga dawo mishi. Baisan me yasa Bilal din zai fada mishi su ba
"Tuntuni ya kamata in maka magana Hamma, tun ranar farko da naga hannun Layla cikin naka ya kamata in tuna maka rashin dacewar haka, in tuna maka yanda tasowa gida daya a karkashin kulawar Abbu bai saka halaccin nan a tsakanin ku ba. Ka daina tabata, idan kana son ta ne kayi wani abu a kai ta zama mallakin ka, amman ka daina..."
Bai amsa Bilal din ba sanda yayi mishi maganar, a cikin makaranta ne, shi yayi jarabawar safe, Bilal din kuma yana da ta azahar, haka ma Layla, baisan dalilin su na shigowa makarantar tun wajen sha biyu saura ba. Layla na karasowa wajen yaji ta riko mishi hannu ta baya, kusan rabin jikinta akan nashi, zai iya cewa ta rungume shine ta gefe
"Hamma..."
Ta fadi cike da wani nishadi da baisan dalilin ta nayin shi ba. Kuma a gaban Bilal din ya bambareta daga jikin shi. Ba zai manta da hawaye tabar wajen ba. Bai tuna rana daya da ya cewa Bilal shi yana son Layla ba, maganar ma wata irin dirar mikiya tayi mishi, tana hautsina wani abu a tare da shi da baisan yana a nutse ba. Yana zaman shi lafiya, yana lallaba rashin natsuwar da yake fama da ita a duk rana, Bilal yazo ya kara mishi wani tunani na daban. Ya saka shi yana neman ma'anar alakar da take tsakanin shi da Layla. Bai saba yawan magana ba, rabin da kwata na maganar da yakeyi a rayuwar shi tsakanin shi da kan shine, a iya tunanin shi maganganun suke makalewa.
Kuma bai saba yiwa kan shi karya ba, yasan yanda yake jin Layla da ban da yanda yake jin su Rukayya, da sai yace ita din matsayin kanwa take a wajen shi. Duk da a ranar ne maganganun Bilal suka saka shi tantance hakan. Shi baice yana son ta ba, bai taba tunanin wata soyayya ba, bayajin yana da natsuwar janyo wata duniyar shi da take a hargitse. Me yasa ma Bilal din zai hargitsa mishi lissafi har haka, yanzun yana saka duk lokacin da jikin Layla zai hadu da nashi sai yaji wani irin tashin hankali na daban. Ya kuma rasa ta inda zai fara hanata rike shi ko da shi bai kokarin riketa ba.
Musamman idan Bilal din yana wajen, sai ya kasa hada idanuwa da shi, akwai tarin abubuwa da Bilal yake nuna mishi bai kamata ba, amman yawancin su tun kafin ya fadi ya rigada ya sani, baisan yanda zai ya bari bane ba. Yawan hada jiki da Layla na daya daga cikin abin da ya kasa gano rashin dacewar shi sai da Bilal din ya tunasar da shi, sai dai kamar ko sa yaushe, ya kara kasancewa cikin jerin abinda baisan ta inda zai bari ba. Bilal ya sake mishi magana jiya, shine magana ta biyu akan abu daya
"Nace maka idan son ta kakeyi kayi wani abu a kai ba zaka saurareni ba wannan karin ma ko?"
Batare da ya daga kai ya kalli Bilal din ba ya amsa da
"Ni bance maka son ta nake yi ba"
Kai Bilal ya jinjina yana furta
"Yayi kyau"
Rayyan zai karya idan yace abin baya damun shi, gabaki daya komai ya kara jagule mishi. Shisa jiya yana gama jarabawar shi ya fita daga cikin makarantar bai jira Bilal ko Layla ba. Amman da tunanin ta cike da kan shi ya kwana, yau ma yana gama jarabawa ya gudo gida. Ya san za taita neman shi. Yana ma iya ganinta tazo gidan. Ko motsi yaji cikin gidan sai ya lumshe idanuwan shi yana jiran yaji shigowar ta, har bayan azahar, ko abinci ma ya kasa ci. Har zane ya fara, amman ya kasa samun natsuwa, mikewa yayi ya dauki riga ya saka a jikin shi, dan ya cire yabar singlet ne sanda ya dawo sallar azahar.
Alwala yayi tun daga gida, saboda kar lokacin sallah ya kama shi a inda ba zai samu ruwan leda da zai alwala ba, ba shi bane zai saka ruwa a butar da baisan rabonta da wanki ba ya kuskura bakin shi, ya kuma wanke fuskar shi ya dauki wasu cutukan. Mikar hanyar da zata hada shi da makarantar su yayi, sanda ya shiga kuwa ana kiran sallar la'asar. Dan haka ya wuce masallaci ya gabatar da sallah yana fitowa, hanyar department din su Layla ya tsinci kan shi da nufa. Yasan ta fito daga jarabawa, tun daga nesa kuwa ya hangota da wasu riga da wando da sukayi mishi kama dana kasar indiyawa, sai dai tsakar rigar har kugunta, ya nade kanta da mayafin da ya rufe iya wuyanta.
Dariya takeyi da alama, su hudune a tsaye. Ita da kawarta da har yanzun bai san sunanta ba, Anisa kawai ya sani a duk tarkacen kawayen Layla da bata rabuwa da yawo da su a cikin makaranta. Itama dan dakin su daya da Laylar, sam baka raba bakinta da kiran Anisa. Wani irin zafi yaji kirjin shi ya dauka ganin daya daga cikin samarin ya rankwafa kusan saitin kunnen Layla yayi mata maganar da tasa ta kwashewa da wata irin dariya. Daga yanayin yaron duk da bai karasa ba, yasan da wahalar gaske ya wuce sa'an Layla din. Shisa zafin kirjin shi ya karu, bai ga dalilin da zaisa ta dinga dariya da yan yara kananu haka ba.
Har tuntube yake duk da babu wasu duwatsu a hanyar
"Layla!"
Ya kira daga nesa kafin ya karasa, muryar shi dauke da kashedi da wani irin yanayi da ba zai fassaru ba duk a tattare, ita ma Layla juyawa tayi tana hango Rayyan din, akwai wani abu tattare da fuskar shi da yake sanar mata da wahala bai dauketa da mari ba inya karaso, duk da hannun shi kan sauka jikinta da tayi laifi da batayi ba, wannan karin dai tana ganin tayi laifin ne amman bata san kona meye ba, ga kafafuwan ta kamar an dasa su a wajen. Da niyyar zuwa gidan su da sun gama labarin da sukeyi take tsaye a wajen.
Saboda bata gan shi ba, jiya da ta kira wayar shi bai dauka ba, ta kira Bilal dan ya ba shi, yana karba yace
"Ba kin kira ban dauka ba? Meye?"
Can kasan makoshi ta amsa shi da
"Bakomai"
Kashe wayar yayi a kunnenta, abin ya mata zafi, ta kirane taji lafiyar shi tunda taje neman shi har ajin su bata gan shi ba. Ya hanata magana da kowa a cikin ajin, shisa bata tambaya ba, wanda suka gwada mata magana ma bata amsa su ba ta wuce abinta. Sai dai ya bata mata rai kamar ko da yaushe da yanayin yanda ya balbaleta da fada dan ta kira shi, babu kalar abinda bata fada ba kafin bacci ya dauketa, na yanda zai sani, yanda ba zata kara neman shi ba, itama tayi fushi, amman tana tashi da safe bayan tayi sallar asuba wayar shi ta fara nema taji a kashe.
"Ka huta ai, kawa kanka Hamma"
Ta furta tana jin babu dadi a ranta, har suka shiga jarabawa tana gwada kiran shi amman wayar a rufe take jinta. Ta kira Bilal yace mata yana makaranta, idan ya gama jarabawa shima zai zo ya dubata. Rayyan na karasowa abokanta da suke tsaye ya fara tsarewa da idanuwa yana musu wani irin kallo kamar zai rufe su da duka, yaran ko sallama basu tsaya yiwa Layla ba suka kama hanya suna wuce wa
"Ina wuni..."
Yarinyar da take kokarin labewa kusa da Layla ta furta cikin siririyar murya, itama idanuwan Rayyan ya kafeta dasu, tana sadda kanta kasa ta juya tabi bayan sauran
"Hamma..."
Layla ta kira tana son tambayar shi dalilin da duk zai kokarar mata abokai haka, amman yanayin fuskar shi ta hanata furta komai
"Layla"
Wani saurayi daya zo wucewa ya kira da murmushi a fuskar shi yana dorawa da
"Ya jarabawar?"
Murmushin karfin hali tayi mishi, zatai magana Rayyan ya damqi hannunta yana kallon saurayin
"Bata son magana da kai"
Ya fadi yanajin wutar da take kirjin shi tana karuwa. Murmushin shi saurayin ya fadada yana wucewa batare da yace komai ba
"Uban kowa kulawa kikeyi? Bakya jin magana ko Layla?"
Kai ta girgiza mishi tana kokarin kwace hannunta da take ji ya rike shi kamar zai tsage mata kashi, kamar hakan yaji ya saki hannun nata yana kamo kunnenta guda daya yana sakata fadin
"Wayyoo Allah na Hamma...zaka tsigemun kunne... Hamma dan Allah"
Ta karasa muryarta na karyewa, sake murda kunnen ta yayi yana mangare mata kai, dai-dai lokacin da idanuwanta suka sauka cikin nashi tun karasowar shi wajen, saboda ya dade da koyon kallon fuskar ta batare da idanuwanta sun hadu ba, kwalli ta saka da eyeliner da yasa idanuwan nata kara gudun bugun da zuciyar shi takeyi
"Bar nan, mayya kawai"
Ya fadi yana sauke idanuwan shi daga cikin nata, idanuwan Layla cike taf da hawaye ta raba shi, tana kasa yiwa Bilal da yake tsaye bayan Rayyan din magana saboda kukan da yake shirin kwace mata. Shima baice mata komai ba, kusan ya riga Rayyan karasowa department din su Layla din, ya tsaya gaisawa da wani abokin shine daya kwana biyu basu hadu ba, akan idanuwan shi komai kuma ya faru. Sai da tabar wajen sannan yace
"Ka kori wanda suke tare, ka kuma kore ta itama"
Juyawa Rayyan din yayi yana kallon Bilal
"Bana son ganin ta da wasu"
Yana dorawa da
"Kuma ba kullum nake son ta a kusa da ni ba"
Rayyan ya karasa maganar kirjin shi na zafi har lokacin, juyawa yayi yana bin bayan Layla da sauri. Bilal ya bishi da kallo yana ganin Ikon Allah, da dan gudu ya hada har ya taddo Layla da ya kama hannunta tana fisgewa, sake kamata yayi yana yin gaba ya soma janta. Zuwa wannan lokacin Bilal kuma baisan kalar tunanin daya kamata yayi ba. Abu daya yake ganewa a halin yanzun, yanda zuciyar shi take zafi kamar zata fito daga kirjin shi. Kiri-kiri yake ganin shakuwar da soyayya mai zafi ce zata haifar a tsakanin Rayyan din da Layla amman Rayyan ya karyata.
Bilal ya rasa wa Rayyan yake kokarin karyatawa, kan shi, shi din, ko kuma soyayyar da take tsakanin su da alamu suka nuna basu da iko da ita. Lumshe idanuwan shi Bilal yayi yana sauke wata irin ajiyar zuciya. Yana bukatar Aisha a irin lokacin nan, idan tayi mishi hirarta zuciyar shi zatayi sanyi ya sani. Yau kanta ciwo yake yi, dan sai da ya fara rakata kofar hostel tukunna, tace mishi zata kwanta. Idan ya kirata ba zataki dagawa ba, idan kuma yace yana son suyi magana ma ba zata ki fitowa ba. Zai zamana mai son kan shi da yawa, hakan ya saka shi tafiya kawai.
Motar da Abbu ya basu ta zamana kamar horo yanzun. Kiri-kiri abokai suka durfafeta, sai a tafi yawo a kone man ba za'a zuba wani ba, ga yanda Bilal yaga suna wujijjigata tunda basu san ciwonta ba, shisa ya kira Abbu yaji ko akwai inda zai iya zuwa ya ajiye motar, duk idan bukatar amfani da ita ya tashi sai yaje ya dauko. Akwai abokin Abbu din anan Zaria, kuma da yake Samaru ne, sai babu nisa. Can din ya kaita ya ajiye. Rayyan bai ko tambaye shi ina motar take ba, tunda ko kafin ya kai haka yakan shirya ya taka zuwa makaranta. Sam abin hawa bawai ya dame shi bane ba.
Yanke hukunci tare machine yayi zuwa gida, ya hango kamar Rayyan tsaye ta wajen gate, karasawa Bilal yayi.
"Hamma..."
Ya kira, a gajiye Rayyan ya kalle shi
"Ina ta jiran ka tun dazun"
Ya kamata ace ya daina mamakin halayen Rayya
"Ni kake jira?"
Kai Rayyan ya daga mishi da ya saka shi jan numfashi
"Da ban biyo ta nan ba fa? Na samu machine daga cikin makaranta? Sai kayi ta jira anan din? Me yasa baka kira wayata ba?"
Kafadh Rayyan ya daga mishi kawai, bayason wata doguwar magana. Wayar shi baisan caji ya kare ba sai dazun, kuma ya ajiye a gidane. Ba wasu masu kiran shi yake da ba, amfanin wayar kalilan ne a wajen shi. Juyawa yayi ya fara tafiya, Bilal na bin shi suka jera suna fita daga cikin makarantar. Hannu ya saka a aljihu ya dauko kwalin sigarin shi
"Dan girman Allah Hamma kar ka sha, idan baka kokarin ragewa ba zaka iya daina wa ba sam"
Bilal ya fadi, yana kallon yanda lokaci yasa labban Rayyan har sun fara duhu saboda hayakin da yake bukama cikin shi, yau ma tunda sassafe da sigarin ya karya. Allah ne shaidar Bilal har a sallah yanzun addu'ar barin shan yake wa Rayyan. Kara daya ya zaro yana sakawa a bakin shi kafin ya mayar da kwalin aljihun shi, ya dauko lighter ya kunna. Sai da ya zuqa ya fitar da hayakin sannan yace
"Ka barni Bilal, bana jin dadi"
Numfashi Bilal ya fitar
"Sai aka ce sigari ce jin dadin?"
Kara sauri Rayyan yayi yana cigaba da zukar sigarin cike da kwarewa
"Allah ya kyauta"
Cewar Bilal da zuciyar shi take kara yin zafi. Kafin su kai gida sai da Rayyan din ya sha kara hudu na sigarin. Shayi suka sha da cin cin din da Layla ta kawo musu. Bilal na daukar takardun shi ya fice daga dakin dan karatu zai koma cikin makaranta yayi, tsallaken