Showing 12001 words to 15000 words out of 150281 words
ribar saiya kawo mata abinta. Ko babu komai a ganin Maimuna zata samu wadatattun kudin da zataci gaba da naimarwa kanta da yaranta taimako wajen kariya daga sharrin masu sharri. Yanda Malam Mainasara yace tayi da rubutun haka tayi kuwa, sai dai tayi sa'a Ahmadi ya hanata fita da ranar komawar ta zagayo.
Sai da akayi wajen kwanaki takwas tsakani sannan ta sami dalilin da tayi amfani dashi wajen fitar. Mamaki ta dingayi tana karawa, saboda karyayyun tsinkayen da Malam Mainasara ya batane ya juye cikin wani farin kyalle ya nannade, ya jujjuya a gaban idanuwansu ita da Khadi, ana bude kyallen saiga tsinke mike kyam kamar ba'a karya shi ba
"Ma shaa Allah, aiki yayi yanda ake so. An samu damar karya sihirin"
Farin ciki fal ranta, farin cikin da batayi wasu dakika tanayi ba, tsoro ya maye gurbin shi, jin Khadi tace
"Saura raba soyayyar Haris da Ahmadi Malam, ya za'ayi da yaron?"
Zungurinta Maimuna tayi cikin tashin hankali, Khadin na zabga mata harara, taga alamar ko kadan Maimuna ba zatayi hankali ba har yanzun. Har wani abin tausayine a batun daya shafi kishiya
"Ni dai kar ayi mishi wani abu, idan sihirine a warware abin ya kaunace shi dai-dai da sauran yaran"
Maimuna ta fadi cikin rawar murya, ba jan yaran take a jikinta ba sam, bata dai tsangwamar su, idan sun zo bangarenta su zauna, idan abincine suka samu su Khalifa naci sukan ci dasu, suyi wasan su. Amman Haris har rawar jiki yaron yakeyi idan ta saka shi ya miko mata abu, ko kuma Ahmadi ya aiko shi bangarenta, da gudun shi yakan shigo. Harda murmushin nan da duk idan yayi sai taga kamar Ahmadi. Batasan kome takeji akan su Haris kauna bace, tafi alakanta shi da shakuwa da kuma shiga rai irin wanda yara suke dashi, wani garin magani ya dauka ya bata
"A ruwa zaki dan barbada yasha, shikenan"
Karba dai tayi kawai badan zuciyarta ta aminta ba, haka ta dawo gida tana jinta kamar marar lafiya. Duk shigowar dasu Haris din sukayi ranar ta kasa ko da mikewa balle ta barbada maganin ta san yanda zatayi ta bashi. A haka Ahmadi ya shigo ya sameta, yaran suka tarye shi da gudun su suna fadin
"Abbu sannu da dawowa"
Kamar yanda suke kiran Ahmadi da shi, Maryama kuma Mami. Amman duk a cikin yaran Haris ya zabi ya dauka, sai ta bishi da kallo, bataso yanda ya tabbatar mata da zancen Malam Mainasara ba, sam bata zaci Maryama na da zuciyar wannan muguntar ba. Ita kam ba zata saka ido Ahmadi ya dinga nuna bambanci a tsakanin yaran ba.
"Duk yaran baka ga kowa ba sai Haris kenan?"
Ta bukata, tsareta Ahmadi yai da idanuwa, duk rashin kunyarta tana bala'in shakkar shi, yanzun ma tsintar kanta tayi da sauke nata idanuwan. Saida ya sallami yaran ya basu alawa da biskit din daya siyo musu tsaraba, suka fice daga dakin, sannan ya kara kallon ta
"Me yake shiga kanki ne wani lokaci?"
Kallon shi tayi itama
"Ni babu abinda ya shiga kaina, amman kana nuna bambanci tsakanin yaran. Inma Haris kafi so bai kamata kana nunawa karara ba, ko ni zuciyata bata sosu ba, yara ai suna gani, kuma yaro baya mantuwa"
Numfashi Ahmadi ya sauke, Allah ne shaida yana kaunar yaran shi, idan ma akwai wanda yakeji daban a cikin su Zubaida ce. Kaunar da yake ma yarinyar daban take, sai yake jin kamar tafi kowa bukatar kaunar shi, dan kasancewarta mace, ko kallon su yake yana hasaso yanda rayuwa zata kasance musu, sai ya dinga ganin su Khalifa sunyi aure da iyalinsu suna zuwa duba shi badan suna bukatar shi ba, dan kyautatawa kawai, amman yakan hango Zubaida har karshen rayuwar su tana bukatar kulawar shi, kuma ba zataji kamar ta girmi taimako daga wajen shi ba.
Haris na da kwalafaci, a iya zaman da yake da yaran shi yana kula da dabi'un su, Haris na cikin yaran da suke yunwar kulawa, ko yanayin shi ka gani yanda yake so yayi komai dan ya faranta maka ko zaka kula shi ya isa ka fahimta, ba bambanci yake nunawa ba, kaunar su yake nuna musu dai-dai bukatar su, amman idan yai kokarin fahimtar da Maimuna zata sauya zancen shi zuwa wani abin. Shisa ya sake zancen gabaki daya
"Yaya Ayuba kemun maganar kara bude wani shago, ina jin zan mishi zancen zaki kawo wani abu ko yaduka ne a siyo a juya miki...."
Kai kawai ta iya jinjinawa, ta kula da maganar Haris ne bayaso ayi. Shisa ta kyale shi, washegari kuwa da safe saiga yaran sun shigo dakinta, tana hada shayi. Zuciyarta na rawa ta sami kofi ta shiga kitchen, anan ta kwanto maganin da yake nade cikin karbun zaninta, sai take ganin kamar Ahmadi zai fito ya ganta, barbadawa tayi a kofi tana saurin zuba ruwan shayi a ciki, dan shekawa tayi, ko bai shanye ba inta samu ya kurba hakan ma ya isa. Tana shiga daki ta ajiye kofin a kasa ta nufi inda Bilal yake rike da cokali mai yatsu da batasan inda ya dauko shi ba karya cake ido ko wani waje. Kama shi tayi ta karbe cokalin, kallonta yakeyi da ido kawai tunda da wahalar gaske kaji kukan shi.
Tana juyowa taga kofin shayin da ta ajiye a hannun Rayyan, ya kuma daga ya kafa bakin shi
"Rayyan...."
Ta kira cikin tashin hankali, kafin ta karasa ta karbe kofin harya shanye. Dago shi tayi gabaki daya ta rikice
"Na shiga uku ni Maimuna.... Na shiga uku, Rayyan...."
Take furtawa tana tale bakin shi kamar hakan zai dawo da abinda yasha, kafin ta saka hannu tana taba fuskar shi, goshin shi da wuyan shi, har hannu tasa cikin rigar shi taji ko ya fara alamun zazzabi, bata taba tsorata irin haka ba, sauke shi tayi kasa dan sai buntsurewa yake yi tana tsugunnawa itama
"Dan ubanka ka tsaya kafin in kwada maka mari"
Ta fadi jikinta ko ina na bari da tashin hankali, dai-dai shigowar Ahmadi
"Lafiya? Me ya faru? Me ya same shi?"
Ya jero mata tambayoyin ganin yanda take a rikice
"Kamar wani abu naga yakai bakin shi, kafin inzo harya hadiye"
Ta furta muryarta na rawa, dana sani ne yai mata rumfa, saboda tashin hankalin da take ciki na rashin sanin mai maganin zaiyi tunda a kan idanuwanta taga karfin aiki irin na Malami Mainasara.
"Bakwajin magana wallahi, na rasa me yasa kuke ajiye kananun abubuwa da yaran nan zasu iya dauka su hadiye...."
Ahmadi ya karasa maganar yana daukar Rayyan da a lokacin duka shekarun shi basu karasa hudu ba
"Me ka ci Rayyan? Fadamun kaji?"
Kai Rayyan din ya girgiza mishi alamar shi baici komai ba. Babu dabar da Ahmadi bai mishi ba, amman yace shi shayi kawai yasha. Barin shi yayi tunda zai fita aiki, yace ma Maimuna din da taga ko zazzabi ya fara ta dauke shi ta kai shi asibiti, kudi ya dauka ya bata, duk da yakan ba kowaccen su kudi su ajiye tsaron laluri koda wani abu na gaggawa zai taso shi yana wajen aiki. Yinin ranar Rayyan wasan shi yake kamar komai bai faru ba, itace ta wuni ta kuma kwana da zazzabi.
Har alkawari tayi na cewa in dai komai bai sami Rayyan ba, har abada ta daina bin Malamai zata cigaba da addu'a tana shan karya tambaya dai da kaikayi koma kan mashekiya, babu kalar addu'a da alkawurran da bata dingayi ba. Daga wannan zazzabin da takeyine ya juye mata laulayi mai zafin gaske. Ta sha wahala matuka, cikin da ta samu kuma na kara daga kimar aikin Malam Mainasara a idanuwanta. Bata yaye Rukayya ba kuma ta sami cikin Shamsu, kamar yanda tayi a haihuwar Khalifa da Zubaida, harma da Rayyan. Duk yanda Khadi taso su koma wajen Malam Mainasara kiyawa tayi, dan ta tsorata da lamarin shi akan Haris, batasan meye ya bata ba har Rayyan yasha, tsoro kuma ya hana ta furtawa kowa zancen, har aminiyar tata Khadi.
A cikin shekarun biyar din nan, a gaban idanuwanta Rayyan, Bilal da sauran yaran suke girma, amman na Rayyan da Bilal ba ita kadai yake baiwa mamaki ba, har mutanen da duk zasu gansu. Kowa zancen yanda suke tasowa kamar yan biyu yakeyi, duk da akwai banbancin shekara daya da watanni har shida a tsakanin su. Amman hatta tsayin su dayane, dan hasken fata kawai Rayyan yafi Bilal, dan shi Rayyan farine tas-tas, Ahmadi ne yakan kaisu aski, hatta da askin iri daya akeyi musu. Kowa yan biyunta yake kira, idan baka sani ba ba zaka taba cewa ba yan biyu bane, ita kanta Maimuna bata gyarawa mutane in sun fadi.
Balle kuma duk a cikin yaran Rayyan ake cewa yafi kowa kyau tunda shi yake kama da ita, shisa kamannin shi da Bilal ya baci, ko ita in ta gefen idanuwa suka gitta ko tana daga daki taji muryoyin su bata gane wanene a cikin su, balle duk kayan da Ahmadi zai siya iri daya yake siyarwa Bilal da Rayyan din.
"Ka dauki jakar ka?"
Ta tambayi Bilal din
"Hamma ya daukar muna..."
Ahmadi bai yarda da wani bai girmi wani da wasu shekaru ba, ko wata daya wani ya baka a cikin gidan saika bashi girman shi, kuma idan ya saka abu sai kayi. Da yake kaunar da take tsakanin shi da yaran mai girma ce, kowa bayason abinda Abbu zai mishi fada ko yayi fushi.
"Allah ya tsare, ka kula da Hamman ka kaji ko?"
Cewar Maimuna, duk da tasan Rayyan ne ya kamata ya kula da Bilal din, sai dai rigimar Rayyan a yan shekarun shi har mamaki take ba Maimuna, ga taurin kai kamar mutanen farko, idan abu yakeyi ko kashe shi zatayi saiya koma ya karasa, yanzun ma Ahmadi ya hana mata dukan shi, a cewar shi zai kangare. Taci gaba da mishi addu'a kawai. Amman ko yaran gidan Yaya Ayuba suka shigo, har wanda suka girmi Rayyan basa shiga gonar shi, duka yake musu, ga rikicin shi baya rabuwa, in ana fada dashi in bashi ya hakura ba, haduwa goma in kukayi sai ya kara cakumarka, abinda Maimuna ta kula dashi yan watannin nan, Bilal ne kawai zai shiga tsakani in ana fada da Rayyan din ya hakura.
Wani lokacin in Bilal yaita janye shi sai fadan ya koma kan Bilal din, tana kuma kula da yaron baya taba daga hannu da sunan ya rama duk wani duka da Rayyan din zai mishi, sai dai in karewa zaiyi, har sai yaga zuciyar shi tayi sanyi tukunna zaka ji yace mishi
"Ka daina fada Hamma, Ayya bata so, Abbu ma bayaso, nima bana so, ka daina"
Amman idan ba Bilal ba babu wanda ya isa ya taba fadan Rayyan cikin dadin rai, yana kuka yana zillewa zata samu ta rufe shi a daki. Amman ko kowa ya manta inya fito saiyaci gaba. Har kuka tayi shekaranjiya akan taurin kan Rayyan, sai take ganin kamar abinda yasha ne yake saka shi wannan abubuwan, kamar tana da laifi a kaddarar Rayyan, kuka takeyi har a sujjada tana rokon idan wani laifin ne ma Allah ya jarabceta ta wani fanni bata kan yaranta ba, kishi da Maryama ba tasan yanda zata bari ba, amman bin Malamai ta hakura dashi, duk da yanzun tana jin kamar ta aiki Khadi a buga mata kasa akan Rayyan, amman tana tsoron a gano mata abinda zai kara daga mata hankali.
Har waje ta fito taga Ahmadi ya tattara kan yaran
"Ayya sai mun dawo"
Haris ya fadi da murmushin da baka raba fuskar yaran dashi, sai ta tsinci kanta da mayar mishi da murmushin
"Allah ya tsare, ku kula da kyau, ayi karatu kuma"
Kai ya jinjina, ya juya kenan sukai karo da Rayyan, da kafin wani yai motsi ya dauke Haris din da mari yana saka Ahmadi karasowa ya tallafe mishi kai
"Rayyan... Bana hanaka dukan yayyanka ba? Haris din ba Hamman ka bane ba? Ka bashi hakuri yanzun nan"
Kallon Ahmadi din Rayyan yayi kamar zaice wani abu, sai kuma ya fasa yana kama hanya ya nufi waje, Bilal na rufa mishi baya da saurin shi. Numfashi Ahmadi ya sauke
"Allah ka tausasa mun zafin zuciyar yaron nan. Allah ka tausasamun shi, kai kabani, Allah ka bani ikon sauke amana"
Yake fadi a cikin ranshi,kwatankwacin addu'ar da yakanyi wa duka yaran duk lokacin da zasuyi wani abu ba dai-dai ba, musamman Rayyan da bayason yawan dukan shi saboda kalar yaran ta fita daban duk a cikin yaran. Haris da yake tsaye ya sadda kan shi kasa Ahmadi ya kamo
"Haris saika dinga hakuri da kanin naka kaji ko?"
Murmushi Haris yayi mishi
"Ni na buge shi Abbu, bangani ba amman"
Kai kawai Ahmadi ya jinjina, yana kama hannun Haris din, ya juyo ya kalli Maimuna da fuskarta take dauke da ban hakuri kan halayen Rayyan din, murmushin karfin gwiwa yayi mata
"A dawo lafiya, ka kula da kanka"
Ya furta a hankali
"Kema haka"
Ya fadi suna ficewa, daki ta koma tana sauke numfashi. Da tunanin halayen Rayyan manne a zuciyarta.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 1, 2020
04
1993, Kano.
Zata iya cewa tunda Ahmadi yabarta tafiyar nan take shiri, kusan sati daya kenan. Sau daya ta taba tafiya mai nisan awa biyu. Wani lokaci ko da irin hakane, Ahmadi baya barinta
"Tsoro ya miki yawa Maryama... Shisa banason kina nisa ke kadai"
Yakan ce, kuma da gaskene, har tsiya akeyi mata a gida wasu lokuttan, ace da tazo a karkara ba zatayi kyawun gani ba. Dariya kawai takanyi ta kyale su, sau daya kafafuwanta suka taka kauyen Kankia da yake a jihar Katsina, shima rasuwa Mannira ce, matar Yayanta Deeni. Zata tuna yanda aka kai ruwa rana kafin a barshi auren Mannira, na daya bata kasance daga danginsu kamar yanda suka saba ba, duk da yanzun wasu na bijirewa auren dangin. Amman rabon tilar yarinyar su Laila ne kawai ya saka shi kafewa da watsi da maganganun da kowa yakeyi na yaren Mannira
"Ka rasa wa zaka jajibo kana zaune lafiya da matarka sai banufiya, salon duk tazo yanda ta lashe maka kurwa ta lashe kurwar sauran yaran ko?"
Maryama ta tuna maganganun Mahaifiyar su lokacin da yazo mata da zancen auren Mannirar, kowa a dangi da abinda yake fadi, mahaifin sune kawai ya bashi goyon baya, sosai ya dinga fada
"Nayi bincike, iyayen yarinyar nan mutanen kirkine, suna zaune da kowa lafiya. Ita ma nagartacciya ce, addinin musulunci dai shi muke bi, kuma a sharuddan da aka kafa mana na neman aure, bamuda wani dalili na hana shi aurenta"
Hakan yasa dole kowa ya hakura, amman badan anaso ba, yanda yan uwa suka daga hankalin su akan auren Deeni da Mannira, ko matar shi da zai hada zama da Mannirar bata tunanin ta damu haka, ko ita da suka zauna da Deenie suna zancen ta jinjina al'amarin matuka
"Ni banki ka kara aure ba Yaya, da ba'a karawa nima da ina gidan wani ba Ahmadi ba, amman banufiya fa, ka dai kara duba lamarin"
Dan yanda sukayi kaurin suna wajen shaidar da akeyi musu ta maita da tsafi na sanyaya jikinta
"Duk musuluncin banufe sai yayi tsafi"
Haka takanji ana fadi, tana kaunar Deeni har ranta, bata son abinda zaizo ya cutar dashi sam.
"Ke dai kiyimun fatan alkhairi kawai"
Deeni ya fadi yana dariya, sai gashi daga baya kowa na yabon kirkinta. Cikin kankanin lokaci ta shiga zukatan jama'a. Maryama da kowa sun alakanta hakan bayan rasuwar Mannira mintina kadan bayan haihuwar 'yarta mace. Mutuwar ta daki Deeni ba kadan ba, har akayi jana'iza baisan inda kan shi yake ba. Kowa ya budi baki ca yakeyi rabone kawai ya hada kaddarar Mannira da Deeni, shisa duk yanda akaso hana shi aurenta yaki ji, ashe ma zaman nasu bamai tsayi bane, tunda duka watannin su sha hudu. To lokacin ne tafiyar da tayi mai tsayi, shekaru kusan biyu kenan da suka wuce.
Lokaci zuwa lokaci takan yi tunanin yarinyar, saboda tun a wajen rasuwa kowa ya kalleta sai yayi magana kan kalar idanuwanta. Tasan ba kasafai ake samun irin idanuwan a cikin mutane ba, musamman anan yankin Najeriya. Amman sai take ganin gara idanuwan yarinyar da taci suna Layla akan na wani bawan Allah data taba gani, har gobe ko ita kadai ta tuna sai tsikar jikinta ta tashi, saboda sak kalar idanuwan miciji, sai da tayi zaton ko tayi gamo ne. Ahmadi yaita mata dariya, yake cewa a wajen aikin su akwai wani bature nashi idanuwan kalar ganye, koraye ne sosai. To ita kam gara mata bature, wannan ba abin mamaki bane, amman a jikin bakar fata, dole abin ya girgizata.
Shisa da taga Layla ta kara jinjina ma Ikon Allah, dan Shi ya banbanta halitta a tsakanin mutane, bata da kalar da zata misalta idanuwan Layla dashi, ko kyanwa kowacce da kalar nata idanuwan. Amman tabbas ta wata kyanwa kawai ta taba gani da kalar idanuwan yarinyar. Kalar surutun da akeyi tun a wajen rasuwar Mannira, sam Maryama ba zaci za'ayi bakwai yarinyar bata bi mahaifiyarta ba. Tun tana tsammanin bayan dawowar su labarin rasuwar Layla zai iso musu harta daina.
Yau dinma har tasha Ahmadi ya rakata, da yake kwana biyu zatayi, daga ita sai Marwan ta taho. Sauran yaran tabar su wajen Maimuna da fuskarta babu yabo babu fallasa tace mata
"Allah ya tsare, ki gaida su"
Da tayi mata sallama, babu wani abu da zatayi da Maimuna zata zauna lafiya da ita. Shisa yanzun inta gaya mata maganar da taji ba zata iya dauka ba, ramawa takeyi. Yaranta ne kawai ta kula Maimuna na budewa hakora, kishinta sai yazowa Maryama da sauki tunda bata saka yaran a cikin rashin jituwar su. Hankalinta kwance tabarsu a gida, suma basu damu ba tunda ko unguwa zata fita a gida takan barsu. Ranta kal tanata kallon gari har suka isa kankia.
Furaira uwargidan Deeni ta karbeta hannu bibbiyu, ta sauketa kamar yanda ta saba taryar su, shisa kowa a danginsu baya gajiya da fadar alkhairinta. Sai dai ta girgiza matuka da ganin dan uwan nata, damuwar da take shimfide akan fuskar shi mai yawa ce, duk da murmushin da yake mata da suke gaisawa, tana ganin yanda bai kai cikin idanuwan shi ba. Tunda ta isa ta jima bata ga giccin Layla ba, kafin daga baya yarinyar da take bacci ta taso ta fito. Farat daya Maryama