Showing 42001 words to 45000 words out of 150281 words

Chapter 15 - MARTABARMU HAUSA NOVELS LUBNA SUFYAN .txt

23 Nov 2025

3986

sata dariya itama. Yanzun ma hira sukeyi, Aisha ce kawai take rike shi da hira haka har baya sanin lokaci yaja. Mamakin jin kiran magriba da akeyi sukayi

"Aisha kingani ko? Nace ma Ayya kafin Magriba zan koma"

Yanayin yanda yai maganar ya sata yin dariya

"Laifina ne kenan?"

Kai ya daga mata. Dakyar sukayi sallama bayan ya mata alkawarin zai dawo gobe. Sai lokacin ya mika mata ledar da take hannun shi. Wasu takalma ne da yar ajinsu take siyarwa yayi mishi kyau, taki biyu ya sai mata kala daban-daban. Duk da batasan ko meye ba taji dadi har ranta, Bilal na da kyauta, lokutta da yawa inta juya cikin dakinta taga wani karamin abu da Bilal ya siya mata sai taji ya dan saukaka mata kewar shi. Anan masallacin unguwar su Aisha yayi sallar Magriba, sannan ya wuce gida.

*

Babu abinda Layla ta dauki gyaran da Mami take yawan yi mata kan kayan da take sakawa banda takura da rashin wayewa irin ta Mami. Ita ta kasa gane yanda duniya take tafiya da zamani yanzun sam. Lokutta da dama Mami na sakata jin daman ace ta fito a kasashen turawa ne, da yanzun ta kai shekarun da zata iya zabarwa kanta duk abinda take so, idan ma gidan zata bari tayi zaman kanta zata iya yin hakan.

Ko facebook data bude, yawancin shafukan da take bi na fina-finan kasashen waje ne, sai kuma na jaruman su. Musamman ma su Kim Kardashian, sai kuma mawaka irin su Rihanna, Drake, Chris Brown da sauran su, dan tafi son wakokin wrap. Takan ji wakokin kasashen sudan, yanayin al'adarsu na burgeta matuka. Lokutta da dama ita kadai a daki tana amfani da mp3 dinta tun kafin tayi waya ta saka earpiece tana gwada kalar raye-rayen da takan gani a fina-finai. Sosai zakayi zaton ta koyi rawa idan kaga yanda take karya gabobin jikinta.

Yanzun kuwa da tayi waya abin ba kama hannun yaro, videos ne da ita kaca-kaca, a jikinta take jin da ace tazo a kasar jamus ko amurka babu abinda zai hanata zuwa makarantar koyon rawa. Ana zuwa gasar da takan gani a fina-finai. Sosai abin yake mata kyau idan ta hasaso, musamman idan ta cire fuskar jaruman ta dora musu ta Rayyan. Wani lokaci abin na bata dariya matuka

"Hamma da rawa"

Takan fadi ita kadai, sai dai ko baiyi ba ita a kanta rawar tayi mishi kyau, musamman ace ita da shi a tare

"Perfect..."

Layla take tsintar kanta da fadi idan ta hango ta da Rayyan din, tun kafin ta gane ma'anar soyayya take kallonta a fina-finai, shisa sam bata sha wahalar gane me take ji akan Rayyan din ba, tunma kafin tasan da gaske son shi takeyi. Duk da wani lokaci yana fita daga ranta na yan dakika, wasu ranakun harna yini daya

"Mayya..."

Kalmar na bakanta mata rai sosai, kuma da gaske ne, akan shi ita din mayyar ce, kome zai mata zuciyarta har tsalle takeyi idan tagan shi, kuma bata fasa daga waya ta kira shi sai dai idan bata da kati. Ko da ace shi da Bilal basa ABU ita kam batajin zata zauna karatu a garin Kano, saboda babu yanda za'ayi abarta ta zauna hostel idan dai a BUK ko Polytechnic take. Shisa bata fadawa kowa ba sanda zata yanki jamb, zabinta na farko ABU din ta saka, tana son samun abinda ake kira "full high institution experience" a turance.

Batason sa idon Mami, rayuwar jami'a take son barjewa yanda ya kamata. Ta kuma yi sa'ar samun 181 a jamb din, ta tsallake dakyar. Tasan me take so, fannin turanci ne ta zaba saboda tana son samu aiki da wata babbar jarida ko gidan radio. BBC ne harinta, ko ba komai watakila tana da rabon zuwa kasar waje. Shisa ta gama tsara yanda komai zai fito, bata shiga tashin hankali ba sai lokacin da aka fara saida fam din jarabawar tace daliban da zasu sami gurbin karatu. Saboda gefe Mami ta koma tana fadin

"Duk makarantun da suke garin Kano? Sai kinje Zaria? Zubaida data gama karatunta kinga tabar gari. Khalifa kan shi cikin garin nan yayi nashi karatun, babu inda zakije, gara ma kiyi magana da Abbunku a sama miki gurbin karatu ko a legal ne idan BUK din ba zata samu ba"

Kuka tayi ranar kamar idanuwanta zasu tsiyaye, dan kiri kiri taga Mami na neman ruguza mata tarin burin da take da shi, a tsayin zamanta da Mami bata taba jin maraici ba sai ranar, watakila inda iyayenta suna raye zasu taimaka mata wajen ganin ta cika burinta ba suyi kokarin zame mata katanga a tsakaninta da abinda take son zama ba. Da Abbu yasa aka kirata ma kuka ta fashe mishi da shi

"Abbu dan ina mace bazan iya tafiya wani waje karatu ba? Dan ina mace bani da 'yan cin zabi? Me yasa Mami ba take son hanani? Karatu ne fa ba wani abu marar kyau ba. Ita ya kamata ta karfafa mun gwiwa in cika burina"

Ta karasa tana wani irin kuka, sosai yake kula da duka yaran. A duk gidan kuma daga Layla sai Jabir ne sukayi wata irin wayewa, rayuwar turawa ita suka saka a gabansu, garama Layla ba sosai takan nuna ba, amman Jabir sai da ya tabbatar har turancin shi ya gyara shi yanda idan yana magana zaka rantse da Allah ba'a kasar najeriya yayi karatu ba, to Layla ma yaji haka take lankwasa harshe

"Jabir turai"

Shine tsokanar da yakan yiwa dan nashi idan yaji yana magana wani lokacin, ko Layla yakan tsokaneta

"Ke da Jabir sai kun tauna harshen ku wata rana"

Kuma da gaskiyar shi, Jabir shine ya fara sakata son gyara turancin ta, haka suke zama kullum tsayin shekara uku suna wannan wahalar, Mami idan tagan su takan ce

"Ikon Allah, lallai sa kai wanda yafi bauta ciwo, da Qur'ani ne kukewa wannan nacin, ba'a kasar Kano ba, har zagayen Najeriya sai an san da zaman ku"

Dariya kawai sukanyi dan a ganin su ita ba zata taba ganewa ba. Ko Jabir din "Languages" yake karanta a BUK, kuma yanzun da yake shekara ta biyu, a tarihin department din ba'a taba samun dalibi mai kokarin shi ba. Abbu ma kance

"Da alama Jabir zaka samu gwamnati ta dauki dawainiyar karatun ka zuwa kasar waje in har kaci gaba da tafiya a haka"

Itama Layla wannan burin take da shi, amman Mami na neman hanata. Shiru Abbu yayi dan baisan me ya kamata yace ma Layla din ba. Har ran shi yana son su da karatu, a matsayinta na 'ya mace musulunci yayi mata wata daraja mai girma, suma kuma ya basu 'yancin kareta da dukkan karfin su. Ya fahimci Mami tunda sunyi zancen tun kafin yasa ta turo mishi Layla

"Kana kallon yanda nake fama da Layla kan wannan rayuwar turawan data dorawa kanta... Ina ga ta bar inda babu idanuwan kowa?"

Mami din ta fadi muryarta na karyewa, har ranta tana tsoron barin Layla Kano. Karatu duk inda kake zakayi. Shima kuma ya aminta da abinda tace din, amman yanda Layla take kuka a gabanshi ya karyar mishi da zuciya

"Abbu idan kaima ka hana zaku sakani yin wani tunani daban"

Layla ta furta tana tashi tabar shi anan zaune. Ya jima shiru, maganganunta sun jefa shi wani tunani daban, harga Allah yafi basu kulawa ita da Bilal sai Haris da yanayin shine son kulawar. Amman ita da Bilal na minti daya bayason suji rashin iyayen su, yasan zafin maraici duk da yayi wayon sanin nashi iyayen, su da basuyi wannan wayan ba baisan abinda sukeji ba, yana kokarin ganin basuji komai ba. Bayason Layla taji kamar dan bata fito daga jikinsu bane suke son zama katanga tsakaninta da burinta.

Yana ganin tayi yarinta ta fahimci cewa basa nufin komai a kanta sai alkhairi, komai da zasuyi dan su kareta ne badan komai ba. Abin ya dame shi, kwana yayi yana juyi, washegari kam yana tashi daga aiki saida ya biya wajen abokin shi Nasiru dan ya nemi shawarar shi, bai boye mishi komai ba

"Ina tsoron tafiyar ta karatu wani gari, har raina ina tsoron hakan saboda ita macece"

Murmushi Nasiru yayi

"Kai kasan indan tani ne yara mata ba zasu wuce matakin sakandire ba, Allah yasan Nabila tayi karatune saboda miji bai fito ba sanda ta gama, Zainabu fa? Ita da kanta ta zabi auren da miji ya fito, sakandiren ma bata samu gamawa ba"

Kai Abbu ya jinjina mishi, duka shine shaida, yanda Nasiru yasan sirrikan shi, haka shima, suna neman shawarar juna a dukkan lamurran su

"Meye muke gudu Ahmadi? Lalacewar yaran ce abin gudu, gani muke idan suna gaban idanuwan mu zamu fi kare su yanda ya kamata. Ni ma tunanin da nakeyi kenan yasa nake son nisanta matan da zurfin karatun boko...sai dai rayuwa ta koyamun ba dabarar mu a tarbiyar yara... Ka duba Bashari, a gaban idona tarbiyar tashi take ta tabarbarewa, duka, zagi babu wanda bamuyi ba, yanzun ba addu'a muka koma ba? Shine aka fara samun dan cigaba"

Numfashi Abbu ya sauke

"Hakane, kana ganin in barta ta tafi?"

Kai Nasiru ya girgiza mishi

"Ba ina cewa kabarta ta tafi bane kai tsaye, ina fada maka karka labe a bayan gudun lalacewar tarbiyya wajen hanata zuwan. A gaban idanuwanka abinda kake gudu zai iya faruwa, kai dai kayi iya yinka wajen tarbiyar, ka kuma roki Allah ya kare abinda idanuwanka ba zasu gani ba..."

Maganganun Nasirun sun kara daure mishi kai, duk yanda yaso ya furta da bakin shi cewa yabar Layla ta tafi Zaria yaki, shawarar shi duka akwai kofar zabi daya barma Ahmadin. Haka Yaya Ayuba da ya same shi da zancen

"Ba gari ba, kaga Nadiya Madina tayo karatunta, duk kuwa da tarin surutun da akai tayi a kai. Gata ta kammala ta dawo lafiya tana dakin mijinta. Kamar yanda kace Nasiru ya fada maka ne, tarbiya iya yinka zakayi, sauran da yafi karfin ka ka hada da addu'a. Karka barta ta tafi sai kana da yakinin duka zuciyarka ta amince maka da tafiyar, idan baka aminta ba hakurin zaifi zama alkhairi. Idan bata fahimce ka ba yau, wata rana zata fahimce ka"

Akan shawarwarin nasu yaita tunani har kwana biyu kafin ya natsu da barin Layla ta tafi, ranar har tsakar dare ya tashi yayi sallah yana rokon Allah daya kare mishi yaran shi, ya rabasu da abokai gurbatattu. Dakyar ya shawo kan Mami

"Shikenan, Allah yasa hakan ya zama alkhairi"

Shine maganarta da wani irin sanyin murya daya taba shi. Layla tayi murna kamar zata goya Abbu. Neman hutun kwana daya yayi a wajen aiki da lokacin jarabawar nata yazo, da kanshi ya dauketa suka tafi har garin Zaria, kwana daya sukayi ta zana jarabawar suka dawo. Ya fadawa Ayya zaije Zaria, dalilin ne bai sanar da ita ba, saboda bai jima da sukayi rikici akan karar Rayyan da Layla ba, idan taji zataje Zaria karatu wani sabon tashin hankalin da bai shirya ba za'ayi a gidan.

Cikin ikon Allah Layla ta ci jarabawar inda ta sami gurbin karatu a jami'ar Ahmadu Bello. Ba ta da kalaman da zata dora farin cikinta a kai ranar, Abbu da kanshi yaje Zaria ya amso mata admission letter dinta, kuma a hankali ita da Mami suke shirin tafiyar tata, tana kokarin ganin duka ranakun batayi wani abu da zai bata ran Mamin ba, kananun kaya ma ta daga musu, dogayen riguna take ta fama dasu.

Abbu kuwa aikawa yayi aka kira mishi Bilal ranar daya amso admission letter din Layla. Yana shigowa bayan sun gaisa ya zauna, Abbu ya mika mishi takardar, amsa Bilal yayi yana dubawa, duk kuwa da Layla ta fada mishi, yayi mata murna sosai da sosai

"Nagani Abbu, ta fadamun..."

Dan lokacin da ta gaya mishi inda ta cika a jamb dinta ta dora da

"Babu wanda na fadawa fa, kai kadaj na gayawa"

Cikin idanuwa ya kalleta

"Me yasa?"

Ya tambaya cikin son sani, dan daga mishi kafadu tayi, kawai saboda shi dinne, saboda tasan zai goyi bayanta, zai tayata son abinda take so, zai karfafa mata gwiwa

"Saboda kawai kaine"

Ta karasa maganar tana saka shi furta

"Hmmm"

Cikin rashin sanin abinda ya kamata yace, lokutta irin haka sai ta saka yaji kamar yana da wani muhimmanci mai girma a rayuwarta. Sai ya ganta tare da Rayyan take karyata mishi hakan. Sai da Abbu ya gyara murya tukunna yace

"Layla kanwa ce a wajen ka, ko bance ka kula da ita ba zakayi. Amman ina so da bakina in roki alfarmar nan, Bilal ka kula da ita, dan Allah ka kula da ita, kudin amana ne a wajena, akan Layla ina so in raba amanar da kai"

Wani irin nauyi Bilal yaji kalaman Abbu sunyi mishi, nauyi sosai

"Ka kula da ita kamar yanda kake tunanin zan kula da ita, a zaman da zatayi a Zaria ka kareta daga dukkan abinda zaka iya kamar yanda kake tunanin ina kare ku, alfarma ce nake nema a wajen ka"

Wannan karin dakyar Bilal yake fitar da numfashi saboda nauyin da kalaman Abbu sukayi mishi, abinda yake roko a wajen shi abune mai girma, amana yake bashi, ya kuma san daraja da hukunci hakan a matakin addini

"In shaa Allah Abbu zanyi kokari"

Ya furta muryar shi can kasan makoshi, kai kawai Abbu ya jinjina, dakyar Bilal din ya iya tashi dan duk gabban jikin shi a sanyaye yake jinsu, har yakai kofa Abbu yace

"Bilal..."

Juyowa yayi

"Ka kula da Rayyan, ka kula da Hamman ka"

Ya karashe maganar cike da roko a idanuwan shi, bai taba cewa Bilal din ya kula da Rayyan ba, saboda yana ganin yanda yake wannan kokarin a duk rana, ya kuma sha jin Ayya nawa Bilal din wannan rokon, yau din Abbu wani irin rauni yake ji naban mamaki, shisa kalaman suka subuce mishi, kai kawai Bilal ya iya daga mishi, da nauyin zuciya ya fice daga dakin Abbu yana nufar bangaren su, inda ya hango Layla ta dora hannunta akan kafadar Rayyan da alama akwai abinda take fada mishi, tureta yayi yana fadin kalaman da Bilal baiji ba, yana kallo Layla ta juya, Rayyan din na kamo hannunta ya dawo da ita.

Lumshe idanuwan shi yayi zuciyar shi na wani irin dokawa, ta ina zai fara? Wanne alkawari ne ya dauka mai girma haka? Ya daukar wa Abbu alkawarin zai kula da Layla kamar yanda Abbun zai kula da ita, idan tana matsayin yar shi, idan tana matsayin kanwar shi bayason tana rungumar namijin da ba muharraminta ba kamar hakan ba komai bane ba, bayason ta kusa da Rayyan, Abbu yace ya kareta daga dukkan abinda zai iya. Abbu ya kara da fadin ya kula da Rayyan, akwai tarin ma'anoni da yake tattare da kalmar "kulawa"

Ta ina zai fara kare Layla daga dukkan abinda zai iya?
Ta ina zai fara idan abin farko da yake son kareta daga shi Rayyan ne?
Ta ina zai fara kula da Rayyan idan bai hana shi daukar ma kan shi zunuban da suke tattare da wannan rungume-rungumen da sukeyi ba?
Ta ina zai fara hana shi abinda ya shafi Layla?
Ta ina zai fara kula da su idan matakin farko ya hada da rabasu da junan su?

Kaddarar su mai girma ce
Kaddarar su ta fara tun kafin sanin su.

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 23, 2020

11

Kallon Abbu takeyi, bakin shi motsi yakeyi, da alama magana yakeyi, sautin maganar tashi ce bata karasawa kunnuwanta. Sosai take kallon shi tana kokarin fahimtar sauran zantukan da yakeyi tunda ta daina ganewa daga

"....Tare da Layla zasu koma Zaria, itama ta sami gurbin karatu acan..."

Duk abinda ya fada kafin wannan kalaman batajin suna da wani muhimmanci a wajenta, abinda yake fada bayansu kuwa bata ma ji ba sam-sam. Ko bayan nashi bakin ya daina motsi, ta bude nata yafi sau biyar tana rufewa cikin rashin sanin abinda ya kamata ta fadi. Tashin hankali take ciki, irin wanda bata taba hangowa ba, a gaban idanuwanta abinda take tunani ba matsala bane yake zame mata katuwar matsala.

Wanne irin Malami ne wannan mai zafi Mami take da shi, zuwa yanzun Ayya zata iya rantsewa duk wani sirri nata a hannun Mami yake. In ba haka ba, babu yanda za'ayi data like wata kofar sai Mami ta sake huda mata wata. Duka yaushe ta samu kan Rayyan din haka, yaushe ta samu harya dauki waya ya kirata. Wannan zuwan ne har sau biyu da kan shi ya sameta yana gaisheta. Kuma ita da idanuwanta bata ganshi tare da Layla ba, har wani bacci takeyi mai cike da natsuwa a tsayin hutun nan da su Rayyan din sukayi.

Saboda tana ganin duk kudadenta da ta bawa Malam basu tashi a banza ba, aiki yaci. Ashe tana bacci Mami nacan tana wargaza mata abinda ta kashe maqudan kudi wajen ganin ta kulla. Ta rasa kalar bala'in nan, ta kuma rasa yanda zatayi da karan tsaye da Mami tayi mata a makoshi.

"Layla naji kace zataje Zaria... Ahmadi Layla..."

Cewar Ayya tana kallon shi kamar wadda bata cikin hayyacinta, wannan rikicin da yake gani cikin idanuwanta shi yake gudu yasa bai fada mata maganar tafiyar Layla Zaria ba. Wani zaiyi tunanin yana tsoron rikicin Ayya ne, kuma ba haka bane ba, yana gudun abinda zai bata mata rai sosai da sosai. Saboda yasan matar shi, kusan tare da juna suka mallaki hankalin su, babu kalar rikici da shirmen ta da baigani ba tun kuruciya. Ta rigada ta sakama kanta tunanin cewa Mami na bibiyarta, abinda duk zai fada mata kuwa ba sauraren shi zatayi ba, ya sani.

In ba ranar da Allah ya nuna mata tagani da idanuwanta cewa Mami bata bibiyarta ba, ba zata taba cire wannan tunanin daga ranta ba. Shisa ya kasa samun kwarin gwiwar fada mata Layla zataje Zaria. Yasan tunanin farko da zata fara bana cewa Layla da kanta ta zabi Zaria bane, sam Ayya ba zatayi wannan tunanin ba, idan yace mata bada son ran Mami za'ayi tafiyar ba zai ja musu wata matsalar, kishin shi zaisa ta dauka yana kokarin goyon bayan Mami ne, yanzun dole ya nuna mata yana tare da ita dari bisa dari ko dan a samu zaman lafiya

"Eh, ta samu gurbin karatu a can, tana son karantar bangaren yaren turanci"

Abbu yai maganar cikin taushin murya, kallon shin dai Ayya takeyi, kafin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login