Showing 117001 words to 120000 words out of 150281 words
Dikko ne, bamu fahimci me kake cewa ba"
A nutse yayiwa kawu bayanin hatsarin da motar ta samu a hanyar Zaria, hatsarin da aka dade ba'a ga irin shi ba, saboda doguwar motar gabaki daya babu wanda aka fitar a ciki, wasu ma sun zama toka, iya gawarwakin da aka samu fitarwa basu fi goma ba idan aka hada jimillarsu, suma wasu duk sun hade da yan uwan su, yanayin da bai bar ma mutanen da suka kawo musu dauki wani zabi daya wuce hade su gabaki daya aka yayyafa musu ruwa aka sallace su hadi da haqa kabari daya aka hade su ba. Shi kan shi kawu babu inda jikin shi baya kyarma, saboda a tunanin shi ma ya kasa hasaso yanda lamarin ya kasance
"Bilal ya rasu"
Ya furta a hankali yana dorawa da
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"
Abbu ma abinda yake fadi kenan yana maimaitawa, bayason bama kwakwalwar shi wani space nayin tunanin komai. Sun kai mintina goma a wajen kafin ya iya samun karfin jan motar suna nufar gida. Da suka karasa ma aka bude musu ya shiga yayi parking, duka yan gidan babu wanda bai tashi ba. Sun zo harabar da ake ajiye motocin sunyi tsaitsaye ne kamar suna jiran dawowar su Abbu din. Shi kan shi Yaya Ayuba da ya fito yana ganin su tsaitsaye yaji kamar ya koma cikin motar, amman daga Abbu har Rayyan babu wanda ya iya ko motsawa balle yayi tunanin ko zasu fito.
Ayya ce ta karaso wajen da sauri, kallo daya zakayi mata kaga yanda idanuwanta suka kankance suka sake launi saboda kukan da tayi, kukan da yanzun ne zata soma shi.
"Kun gan shi?"
Ta tambaya, Yaya Ayuba na girgiza mata kai hadi da dauke idanuwan shi daga kanta. Ya daiyi mamakin ganin harsu Khalifa a cikin gidan. Suna hada idanuwa da Khalifa ya tako ya karaso inda Yaya Ayuba da yaji shi gefe yake
"Khalifa ya rasu... Bilal ya rasu"
Yaya Ayuba ya furta girman kalaman na dukan shi, cikin tashin hankali Khalifa yake kallon shi, da hankalin shi, a tsayin rayuwar shi baisan wani abu rashi ba, wani daya taba shakuwa da shi bai taba rasuwa ba, yaune rana ta farko da aka fara sanar da shi labarin mutuwar da ya saka gwiwoyin kafafuwan shi yin sanyi gabaki daya, da Yaya Ayuba bai riko shi ba sai yakai kasa
"Subhanallahi, Khalifa"
Yaya Ayuba ya fadi, a zaton shi tunda Khalifan ne Babba a gidan, zaifi sauki shiya fara sani kafin a san yanda za'a sanar da Ayya da ta karaso wajen tana kallon Yaya Ayuba
"Me ya faru? Me akayi?"
Kan shi Khalifa ya dafe yana saki, numfashi yake fitarwa ta baki ko zai samu saukin abinda yake ji, amman komai kara hade mishi waje daya yake. Gurin motar Ayya ta karasa tana bude bangaren da Abbu yake, kan shi taga ya hade da gaban motar, a tsorace ta dafa shi, ya kasa dagowa
"Ahmadi"
Ta kira, amman bai ko motsa ba, mantawa tayi da yaranta na wajen, mantawa tayi akwai kowa banda ita da shi, ta saka hannuwanta tana dago da shi
"Ahmadi..."
Ta sake kira, idanuwan shi Abbu ya saka cikin nata, kafin ya dago nashi hannuwan ya kama nata da yake jikin shi, kamar yana so ta taimaka mishi ya fito daga motar, hakan kuwa tayi, duk da yana fitowa sai ya kasa yin komai banda jingina bayan shi da motar yana zamewa a hankali ya zauna, har lokacin yana rike da hannuwan Ayya shisa itama ta bishi kasan tana tsugunnawa, da wani yanayin tashin hankali yake kallonta
"Ya rasu Maimuna... Bilal ya rasu"
Ba wannan bace mutuwa ta farko da aka fada mata, ance baka san daci na mutuwa ba sai ranar daka rasa mahaifa, miji ko da. Ta dandani mutuwa kala-kala, bata san ciwon rashin da daban yake ba sai yau, dan wani abune ya tsirga mata daga dan yatsan kafarta zuwa tsakiyar kanta, kafin komai ya tattaro ya dawo yana tokare mata kahon zuciya, kukan kowa da wani yanayi yake isa kunnuwanta, musamman Rukayya da ta karaso inda take tana jijjigata
"Ayya me suke cewa? Ayya kice mun karya ne, ki ce mun Hamma Bilal bai rasu ba"
Bata ko iya juyawa ba, hannuwa Abbu da yake rike da nata ne kawai abinda tasan yana rike da sauran hankalin da take tare da shi, haka Rukayya ta dinga bin duk wanda ta samu tana jijjiga shi, har ta karasa inda Mami take tsaye hawaye na zubar mata, wani nabin wani. Tun jiya Ayya ta fada musu abinda yake faruwa, tun jiyan kuma Rukayya take tunanin rayuwa da yanda komai zai iya canzawa cikin kankanin lokaci. Tun da ta taso Ayya ke fadin laifukan Mami, duk da sanda ta fara hankali ta gane rabin mitar Ayya din na tare da kishin da yake dawainiya da ita.
Mami bata taba ko da mata kallon banza ba, gaisuwar mutunci tana hadasu, wasu lokuttan ma har su danyi hira. Duk yanda Ayya taso ta ga laifin Mami bata taba gani ba, sai yau da ta karasa tana kama hannun Mami
"Kingani ko Mami? Muna zaman mu ki dauko mana Layla, da bata shigo rayuwar mu ba da yanzun bamu san tashin hankalin nan ba, da Hamma bai bar gida ba, da labarin mutuwar shi baizo mana ba... Wallahi ba zan yafe miki ba, Mami ba zan yafe miki ba..."
Rukayya take fadi tana durkushewa wani irin gunjin kuka na kwace mata. Duk abinda akeyi Rayyan na cikin motar, ba jinsu bane bayayi, kan shi yake ji kamar a wata duniya ta daban. Komai ne yake karasawa cikin kunnuwan shi kamar saukar ruwan saman da babu hadari, yana zaune ciki yaji muryar Haris na fadin
"Bilal ya rasu? Yaushe? Garin yaya?"
Kafin ya dora da
"Ina Rayyan?"
Baiji wani ya amsa shi ba, ya dai ji lokacin da Haris din ya bude murfin motar a bangaren da yake. Ya kuma ji hannun Haris ya kama na shi yana janyo shi ya fito da shi daga motar
"Rayyan... Rayyan"
Haris yake kira, amman baya ganin komai, ba shi da kalma ta hausa da zai misalta ganin shi da ita, abinda bature ke kira da "Blank" shine abinda yake faruwa da ganin shi. Yasan akwai mutane a zagaye da shi, amman baya ganin su, jin su kawai yakeyi. Da duk dakika kara jinsu yake, kukan su da maganganun su da yake tabbatar mishi da kalaman da yaji dai-dai ne, Bilal ya rasu, Bilal ya bar shi, ya mishi nisan da bashi da tabbas akan ranar da zai kamo shi
"Rayyan..."
Ya sake jin muryar Haris wannan karin yana jijjiga shi, iska yake nema, ko yayane ya samu ta isa cikin kwakwalwar shi, watakila ganin shi ya dawo, watakila ya daina jin duniyar na katantanwa da shi. Idanuwan shi ya lumshe yana jin wani shiru a cikin kunnuwan shi, kafin tunanin shi ya dauke gabaki daya.
BAYAN KWANA UKU
Hannun shi yake ji kamar a daure, yayi kokarin motsa shi amman bayajin karfi ko kadan a jikin shi balle ya iya motsawa, idanuwan shi ma ya dauki wasu dakika yana kokarin motsa su cikin son ya bude su kafin ya samu nasarar yin hakan, wani haske da yaji yayi mishi yawa na saka shi mayar da su ya rufe gam saboda kan shi da ya fara sarawa, sake gwada bude idanuwan na shi yayi, yanayin dakin ya fara karewa kallo, yana kokarin fahimtar inda yake, kafin yabi hannun shi da kallo, karin ruwa ne a jiki
"Rayyan..."
Yaji wata murya da bai taba sanin ta ba ta kira shi, a hankali ya juya kan shi yana kallon mutumin da kayan jikin shi yasa shi gane likita ne, kafin ya tabbatar da a asibiti yake, runtsa idanuwan shi yayi yana sake bude su da tunanin me yake yi a asibiti, sake runtsa idanuwan shi yayi, komai na dawo mishi kamar shirin film kafin ya bude su yana wata irin mikewa, likitan ya dafa shi
"Akwai karin ruwa a jikin ka, kabi a hankali"
Hannun likitan da yake kafadarshi ya ture, yana jin makoshin shi kamar sahara ce a ciki saboda bushewa, karin ruwan da yake jikin shi ya fisge yana sauko da kafafuwan shi kasa, maganar da ta daina karasawa kunnuwan shi ita likitan yakeyi, da ya saka kafafuwan na shi a kasa ya taka sai yaji kamar sunyi mishi sanyi, kamar yayi kwanaki bai taka su ba, shigowar Haris da ya fita siyo wata allura ya saka shi daga kai ya kalli Haris din da yaga kamar ya rame
"Hamma mu tafi gida"
Da alamun gajiya a tattare da Haris din yace
"Yanzun ka tashi Rayyyan, dan Allah kayi hakuri ka kara warwarewa tukunna, kaji..."
Kai Rayyan yake girgizawa tunda Haris ya fara magana, ba zai zauna ba shi kam, yana son ya ga Ayya, yana son ganin Abbu, da dukkan zuciyar shi yake jin son ganin iyayen na shi kafin ya bude zuciyar shi da koma menene yake ji
"Dan Allah Hamma, rokon ka nakeyi, ka kaini wajen Ayya"
Kai Haris ya jinjina mishi, bashi da karfin yin gardama da Rayyan. A kwanakin nan ukku shi kadai yasan kalar tashin hankalin da ya gani.
"Ka zauna in zo to"
Wannan karin Rayyan baiyi musu ba ya koma ya zauna kan gadon. Da ido Haris yayi wa likitan nuni da su dan fita. Dakyar ya samu ya yarda su tafi da Rayyan din, dan likitan na tsoron yanda jinin Rayyan din ya hau, idan ya sake faduwa zai samu babbar matsala. Sai da Haris yayi ma likitan alkawarin zasu dawo sannan. Duk yanda Rayyan yaso yin musu da Haris ya kama hannun shi yana dorawa a kafadar shi saiya kasa, bashi da karfi ko kadan. Suna fita daga dakin Haris ya cire takalman kafar shi yana sa kafar shi daya ya tura su saitin Rayyan din da yaji wani abu ya tsaya mishi a wuya.
Saka takalman yayi, shi Haris din na takawa a haka har suka fita daga asibitin zuwa inda motar shi take, sai da ya taimakawa Rayyan ya shiga sannan ya zagaya ya shiga shima. Gida suka nufa, wannan karin ma sai da Haris ya taimaka mishi suka fita daga motar. Sai Rayyan din yake ganin kamar gidan ya canza, saboda akwai mutane a harabar gidan, an kafa rumfuna, ganin su na kara gudun bugun zuciyar shi. Yana jin Haris yayi musu sallama wasu na furta
"Ya karin hakuri?"
Yana amsa su da
"Mungode Allah"
Ya ja Rayyan din suka wuce, har dakin Ayya, nan ma akwai mutane, bai damu da su ba, idanuwan shi Ayya suke nema, harya hangota a zaune da hijabi a jikinta, zame jikin shi yayi daga na Haris da yake rike da shi
"Rayyan..."
Batare da ya kalli Haris ba yace
"Zan iya"
Tsaye Haris din yayi yana kallon Rayyan ya taka ya karasa inda Ayya take zaune yana tsugunnawa a gabanta
"Ayya"
Ya kira, sai lokacin ta kalle shi, idanuwanta duk sun kankance
"Rayyan..."
Ta furta, yanda muryarta ta karye na tabbatar mishi da abinda yake son ji, dakyar ya dafa kasa yana mikewa, batayi kokarin hana shi ba harya bar dakin. Wuce Haris daya bi bayan shi yayi, bango yake dafawa yana tafiya saboda rashin karfin da yake ji, dakin su ya nufa yana kama kofar ya bude ya shiga, jin Haris a bayan shi ya saka shi juyawa
"Dan Allah Hamma, ina son zama ni ka dai ne... Dan Allah"
Sai da Haris ya sauke numfashi tukunna ya dan daga kai, su duk sunyi kukan su, ciwon bai fara rage musu ba, amman sun yarda da cewa Allah da ya basu Bilal ya karbi abin shi, Rayyan na bukatar lokaci yaji mutuwar shima, ya yarda da sun rasa Bilal, ya rasa Bilal. Shisa ya juya, anan inda yake tsaye Rayyan ya durkushe yana zama da gwiyoyin shi a kasa, zafin kirjin shi yakeyi, kamar an tura mishi wani abu a ciki haka yake ji, idanuwan shi ya lumshe
"Ya rasu Maimuna... Bilal ya rasu"
Kalaman Abbu suka dawo mishi, wani irin numfashi yake fisga kamar rayuwar duka na barin shi, sunan Allah yake son kira ko zai samu sauki amman ya kasa motsa labban shi, hade kan shi yayi da jikin shi saboda kirjin shi da yake zafi, kafin yaji an dago shi
"Rayyan"
Yaji muryar Abbu da ta saka shi dora kan shi a jikin Abbun
"Kayi hakuri Rayyan, hakuri zamuyi, bamu da wani zabi daya wuce duk muyi hakuri"
Kai Rayyan yake girgizawa Abbu, kalaman Abbu din na saka wasu irin hawaye masu zafin gaske zubo mishi. Da komai na jikin shi yake son yarda da mutuwar Bilal
"Kun ga gawar? Kun binne shi Abbu?"
Ya bukata wasu hawayen na zubo mishi, yana jin hannuwan Abbu a jikin shi kamar wata fanka da take fifita mishi ciwukan da ke mishi azabar ciwo
"Bamu gani ba, baya nufin bai rasu ba, naga motar, munje ni da Yaya Ayuba, babu wanda ya fita a motar Rayyan... Kuma Bilal ita ya shiga... Kayi hakuri dan Allah, kayi hakuri"
Wani irin gunjin kuka ya kwace ma Rayyan, kuka yakeyi kamar yaro dan shekara biyu, kukan da idan wani yace zaiyi irin shi koma meye zai faru da shi kuwa zai karyata. Amman yau kara shigewa jikin Abbu yake yana kuka kamar ran shi zai fita, baiga ta inda zai fara yarda ya rasa Bilal bayan ko gawar shi baigani ba, akwai wani abu a kasan zuciyar shi da yake fada mishi bai rasa Bilal ba, koya ne da yaji a jikin shi, da yaji cewa yana gab ko kuma ya rasa Bilal din gabaki daya
"Ab.. Abbu zuciyata... Kirjina Abbu"
Rayyan yake fadi yana jin kamar shima yabi Bilal din koma ina yake ko zai samu sauki. Kara gyara zaman shi Abbu yayi yana sake riko Rayyan, rabon daya rike shi a jikin shi haka tun yana dan karami, bai taba zaton zai sake samun dama irin haka ba, sai dai yanayin ba mai dadi bane balle yace zaiyi wannan tunanin. Rike yake da Rayyan da sai rashin Bilal yasa shi kasancewa karkashin inuwa daya haka da shi. Da dukkan zuciyar shi yake jinjina kokarin iyayen da suka taba binne yaron su. A gefen zuciyar shi addu'ar samun saukin karbar rashin Bilal yake yiwa Rayyan da har lokacin kuka yake a jikin Abbu kamar ba zai taba dainawa ba.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 4, 2021.
28
Kwance take, dakyar take iya daga idanuwanta. Haris ne ma ya kirata a waya yana tambayar ta ko tana son cin wani abu, tace mishi yoghurt. Da yawa ya siyo ya kai mata daya har daki, sauran yace ya saka mata a fridge. Shima ko rabi bata sha ba ya fita daga ranta, kusan aman shi tayi. Hannun ta dafe yake da cikinta da ta fara ganin alamar ya dan taso, saboda bata da tumbi da can. Lumshe idanuwanta tayi tana jin suna mata wani radadi saboda kukan da takeyi, ko hasken waya bata so a cikin idanuwan nata. Bata taba tunanin zata kwana ta yini ta sake kwana ta yini tana kuka ba sai da labarin rasuwar Bilal ya daki kunnenta.
Ita safiyar ranar da akayi rasuwar bacci ta dan samu, saboda ta kwana tana kuka, ta kwana cikin tashin hankalin rabuwa da Rayyan, ta kira shi yafi sau hamsin bai daga ba, ko ya daina son ta tana son ya saurareta, tana son ta fada mishi batasan yanda akayi abinda ya faru din ya faru ba. Tana son ta bashi uzurin da kowa ya kasa yi mata, ta kare kanta kamar yanda Ayya ta kare Bilal, yanda ta kira abinda ya faru da su da sunan kuskure. Saboda idan Rayyan da kan shi ya barta ina zata je? Wa zai karbeta? Waye ba zai dora alhakin komai a kanta ba?
Kuskurenta ne daukar kafafuwanta taje gidan su, ta rigada ta san wannan, bata tsaya ba har dakin su. Amman batajin tana da laifi a cikin jirin da ya fara dibarta cikin yan mintina kadan da zamanta. Ta zauna ne ta dan huta, ta maida numfashi, bama zata ce ga dalili kwara daya da yasa ta zauna ba, tunda ko Rayyan yana nan ba ko yaushe take zama ba, baya bari, da ta shigo yake mikewa. Da taji maganar shi kamar yanda ya hana mata zama a dakin, da gidan ma gabaki daya ko da suna nan, balle kuma basa nan, watakila da bata zo in da take ba yanzun.
Da tarin burin da take da shi na auren Rayyan bai ruguje ba. Da bata ga tsanarta a cikin idanuwan shi ba. Abbu ya kara hargitsata da furucin shi, saboda idan duniya duka zata hade da ita a waje daya bata hango yanda zata fara zaman aure da Bilal ba. Ko na minti daya zuciyarta bata taba doka mishi ta wannan fannin ba, yanda zata fara kwanciya ta tashi da shi karkashin inuwar aure da sanin ya rabata da komai da take takama da shi, banda Martabar ta harda Rayyan, harda Hamman ta. Ba laifi take kokarin dora mishi ba, amman zata iya farawa idan suka kasance inuwa daya.
Tashin hankali ne shimfide take hangoma rayuwarta da ta birkice cikin kankanin lokaci. Da tunani kala-kala a ranta har gari ya waye, da tayi alwalar asuba ma sai da ta koma ta dan kwanta saboda sanyin da ta dinga ji da yake akwai zazzabi a jikinta. Ta samu bacci ne ba jimawa, dan ji tayi kamar tana bude idanuwanta ta mayar da su ta rufe ne taji kamar an fasa kuka, yanayin da ya sakata bude idanuwa babu shiri, ba kuma karya kunnuwanta sukayi mata ba, kuka ne, dakyar ta iya saukowa daga kan gadon, da yake window din dakinta ta wajen harabar motocin gidan ne, zagayawa tayi ta leka ta hango kusan kowa na gidan a wajen. Kafin kunnuwanta su tsinto mata
"Bilal ya rasu"
Cikin muryar da bata san ko waye bama, bangon wajen ta dafa tana runtsa idanuwanta, duniyar na wulwula mata kafin wani abu ya tsirga mata a ciki yana saka bayanta amsawa. Babu shiri ta durkusa saboda azabar da ta dirar mata ga kidimar mutuwar Bilal da take mata kamar almara, sunan Allah duk wanda yazo bakinta shi take kira, tana dafe cikinta da kamar ana tsinka wani abu a ciki, kafin wasu irin hawaye kamar an