Showing 21001 words to 24000 words out of 150281 words
Aisha yafi samun damar tsokanar shi da yawa haka. Ko Rayyan din aka tsare ba zaice ga asalin yanda soyayya take ba balle kuma shi. Kawai yanajin Aisha har ran shine, baisan ko haka soyayya take ba, amman yasan ko dariya tayi sai ya ga kamar Layla, idan tana mishi surutunta ma, kominta yana mishi kamar Layla. Zai rantse lokutta da yawa har idanuwan Layla yake gani a cikin nata.
Shi dai yasan Layla ce dalilin kusancin shi da Aisha, Layla ce sanadin fara maganar shi da Aisha, idan akwai wani abu bayan wannan baisan shi ba. Saboda duka gidan Layla ce kawai take kula da ran shi ya baci, kowa kawai dauka yake ran Bilal baya baci, ba'awa Bilal laifi, ba zai manta ranar da tace mishi
"Hamma na rana daya ka nuna ranka ya baci, ka daina bari a cikin ka"
Murmushin da yakan yi ko da ranshi a bace yake shi yai mata
"Waye yace miki raina ya baci"
Dariya tayi
"Murmushin ka baya kaiwa cikin idanuwanka. Idan kayi murmushi ko kayi dariya harda idanuwan ka kakeyi, idan ranka ya baci idanuwanka basa dariya... Bansan ya zan maka bayani ka gane ba"
Numfashi kawai ya sauke
"Me yasa ba zaka fadama Hamma Rayyan ya bata maka rai ba?"
Kai kawai ya jinjina mata. Kuma tun daga ranar ko a haduwa sukayi tai mishi magana yanayin murmushi zata ce
"Waya bata ma Hamma Bilal rai?"
Ita kadai take ganewa, kuma ita kadai yakan fadama ran shi ya baci wani lokacin. Ayya damuwar Rayyan kawai ta isheta, shisa baya taba nuna yana cikin matsala, ko rashin lafiya saiya kwanta sosai da sosai ake ganewa. Sai yayi ciwo a tsaye ya warke babu wanda yasani sai Layla. Yanzun ma mikewa yayi yana ficewa daga dakin, wata irin yunwa yake ji, bangaren Mami zashi yaga ko ta dafa wani abin da yake ci, tuwo Ayya tayi miyar taushe, bayason dafaffiyar albasa, ko a dafaduka aka saka saiya tsince tas yake iya cin abincin. Yanzun tunda Rayyan ya zuba yaga tayi yawan da baisan ya zaiyi ya tsince ba, shisa ya hakura ya fito kawai.
Bai karasa bangaren Mami da yake lallabawa kar Ayya tagan shi ba, yasan bataso yana cin abincin Mami din, amman zuwa yanzun sai dai ta bishi da ido kawai, tunda taga ba zata iya hana shi ba, shine abu guda daya da Bilal ya taba gardama mata a kai, ta hana shi yaki hanuwa, amman kome zatace yayi baya taba nuna mata bayaso ko a fuskar shi kuwa. Layla yaci karo da ita
"Hamma..."
Ta furta da fara'a a fuskarta
"Me kuka dafa Layla?"
Bilal ya tambaya
"Wake da shinkafa ne, akwai miya. Amman yayyanka kayan miyar Mami tayi, bari ingani dai..."
Ta furta tana juyawa ta koma ciki, ta kai mintina kusan goma kafin ta fito da filet a hannunta da abinci harda cokali a ciki.
"Na ciccire albasar, amman saika duba akwai kadan a ciki..."
Karba yayi yana murmushi
"Ni nace bana cin albasa?"
Dariya Layla tayi
"Ba saika fada ba, kana barin shi a plate din abincinka da yawa...."
Wannan karin shi yayi dariyar
"Ke kam Allah ya shiryeki"
Yanajin dariyarta harya wuce, tun a hanya ya fara cin abincin saboda yunwar da yakeji, harya karasa daki
"Kai ba zaka daina cin abincin matar can ba, Ayya ta hana, sai an barbada maka abu tukunna ko?"
Saida Bilal ya hadiye abincin da yake bakin shi tukunna yace
"Abu nawa Ayya ta hanaka baka daina ba? Kuma kasan zato babu kyau ko a addini..."
Cewar Bilal din yana kara cakuda abincin hadi da diba ya saka a bakin shi
"Ni daban, kai daban, bana so kana cin abincin ta, amman ba zaka jini ba"
Shiru yayi ya kyale Rayyan din, idan wannan maganar ce sun saba, Ayya tagaji, shi dinne ya kasa hakura har yanzun. Duk cikin karatun duniya da ake mishi babu wanda ya rike da kyau irin cewa Mami zata barbada mishi abu yaci. Abincin shi yaci gaba daci kan shi a tsaye, yana ganin Rayyan din ya mike ya dauko uniform din shi da safa
"Wanki zakayi?"
Kai Rayyan ya girgiza
"Me yasa zan wanke, Layla zata wanke mun"
Yanda yayi maganar zaka rantse da Allah Layla din yar aiki ce a gidan ba 'ya ba.
"Layla baiwar kace? Me yasa kaci ka takurama yarinyar nan ne wai?"
Kallon shi Rayyan yayi
"Me yasa ita bata damu ba sai kai?"
Kai kawai Bilal ya jinjina, yana kallon Rayyan din ya fita. Ba shiga bangaren Mami yakeyi ba, idan ba wani yaron zai daka ya ruga ya shiga bangaren nata ba, itama sam bata shiga harkar shi tunda rashin kunya yake mata kamar zai daketa.
"Layla!"
Ya kira, itama sai lokacin da ta zubama Bilal abinci ta samu ta zuba nata, tana zaune da remote a hannunta da ta kasa tsayawa waje daya taji ya kwala mata kira
"Rayyan ne ko?"
Mami ta tambaya, duk da muryar su shida Bilal din ba ko yaushe ake banbance taba, amman tasan idan Bilal ne zai shiga har ciki, ba zai tsaya daga bakin kofa yana kwala ma Layla kira haka ba. Cokalinta ta mayar cikin abincin tana mikewa, marin da yayi mata yau da safe ta fadama kanta tana zaune zai zo nemanta, zatayi banza da shi, haka ma tacewa Mami data shiga tana kuka
"Ina zaune zai kirani, kinsan Allah Mami ba zanje ba nima, kowa yayi harkar shi"
Murmushi kawai Mami tayi, ita yanzun ta daina tsoma bakinta a tsakanin su. Tun tasowar Layla idan Rayyan din yai mata wani duka har ranta Mami take ji, tayi fada da Ayya yafi a kirga kan cin zalin Layla da Rayyan yakeyi. Sau biyu ta taba kaiwa Abbu kara, duka lokutta biyun kuma tana shan kunya, dan ko muryar Rayyan din Layla taji da gudu take fita, sai ta dauki ido kawai ta saka musu. Yanzun zata shigo tana kuka shabe-shabe, tana fadar yanda ita da Rayyan sun raba hanya, sai ya aiko kiranta ta ajiye koma meye takeyi ta tafi.
Kamar yanzun da ta ajiye abinci, jikinta har kyarma yakeyi ta fita
"Ki wanke mun"
Ya fadi yana ajiye uniform din a kasa
"Yanzun idan na gama cin abinci"
Kallonta yayi
"Idan ba zaki wanke mun ba ki fadamun, tun dazun bakici abincin ba sai yanzun?"
Kayan ta tattara tana turo labbanta gaba, ta wuce ta koma ciki, tana jin tsakin da Rayyan din yayi. Sai da ya dafe kirjin shi duk da yayi kokarin ganin bai hada idanuwan da ita ba, amman sai da taja zuciyar shi ta doka. Ita kuwa cikin daki ta shiga
"Ni fa zan taimaka in wanke mishi Mami, amman shine wai ba zan gama cin abincina ba, zaiyi fushi ya dauka"
Murmushi kawai Mami tayi tana kallon Layla harta wuce da wankin tana kuma cigaba da mita.
"Allah ya kyautata kaddarar da take tsakanin ku Layla. Allah ya kare maraicin ki"
Shine addu'ar da Mami take bin ta da ita a lokutta irin haka. Har tsoro takeji idan taga sunyi wani abin ita da Rayyan. Ko yara batajin suna cewa Hamma Rayyan ya basu abu, amman wani lokacin zakaga Layla da abu kuma tace shi ya bata. Har kudi a cikin aljihun makarantar shi duk idan ya bata wanki
"Ki mayar mishi da kudin shi"
Mami kance idan ta nuna mata ta tsinta, amman sau biyu ta gwada tana shan maruka, yana fada mata yanda bayaso tana zuwa kusa da shi
"Hamma zai sauke Jujun shi a kaina Mami"
Ta bawa Bilal kuma sau biyu shima ya mayar mishi, saiya Bilal din ya dawo mata dasu yace mata ca yayi ta rike, yana sane yake bari, ba zai bata da hannun shi bane ba. Ba kuma zai bude baki yace ta dauka ba. Shisa har a ranta Mami tana tsoron kaddarar da take tsakanin Layla da Rayyan din. Bata da wanda zata furtawa ne kawai, tunda ita ba wasu kawaye gareta ba, sirrinta yana cikinta, gara ta zanta damuwarta da Haris da ta fadawa wani can. Shikuma yanzun ya sami gurbin karatu a Zaria, duk da yakan yi kokarin zuwa wani lokacin duk karshen wata, idan karatu yayi tsanani kuma sai yakai wata uku ma bata saka shi a idanuwanta ba.
Tana nan zaune, sai da Layla ta gama wankin tukunna ta dawo ta zauna tana daukar abincin
"Har abincina yayi sanyi"
Ta furta cikin yanayin mitarta
"Ki dumama"
Cewar Mami, kai kawai ta girgiza
"Nifa bama na son wanki, Mami kinsan bana son wanki, shine Hamma yake sakani"
Murmushi kawai Mami tayi, indan Layla ce ba gajiya takeyi da mita ba musamman akan Rayyan. Haka ta gama cin abincin tana mitar ta tashi ta wuce kitchen, kwanonin ba yawa garesu ba, ta daifi so ta wanke, sam batason aiki a kanta. Duk da akwai miya da yawa, Mami tace ko taliya sai a kara dafawa, gara tayi wanke-wanken saita fi jin dadin zama tayi kallonta a nutse.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 11, 2020
06
"Abbu...Sannu da zuwa"
Huda da take zaune a cikin falon ta fadi cike da farin cikin ganin shi, idan kaga yanayin autar ta Ayya zaka rantse tayi satika bata ga Abbun ba, a maimakon kwanaki hudu
"Huda"
Cewar Ahmadi yana dorawa da
"Ke kadai? Duk ina kowa? Ina Ayyar ku?"
Da murmushi a fuskar Huda har lokacin tace
"Kowa yana daki, Ayya tana sallar isha'i"
Numfashi Ahmadi ya sauke, a gajiye yake jin shi, ko dan tun da suka isa Abuja bawai sun zauna waje daya bane ba, hidimar da ta kaisu kawai sukeyi
"Ma shaa Allah, Ke kinyi sallar dai ko?"
Kai ta jinjina mishi
"Tun dazun ma... Hamma Bilal ne daya shigo sai yace inje inyi"
Wannan karin Ahmadi ne yayi murmushi
"Madallah da Hamma Bilal...bari inzo kafin ta idar"
Ya karasa maganar yana ficewa daga dakin. Kan shi tsaye bangaren Maryama ya nufa, ita da Jabir ya samu zaune a falon suna cin abinci. Jabir suna gaisawa ya dauki filet din shi yana ficewa
"Sannu da dawowa...kayi zuru-zuru"
Maryama tai maganar cike da kulawa, yar dariya Ahmadi yayi
"Yanzun nan? Ko dan ba zama mukayi waje daya ba, kinsan ni da nayi zirga-zirga sai fuskata ta nuna"
Murmushi tayi
"Hutu ne yai maka yawa"
Ta karasa maganar da sigar tsokana tana mikewa, tana jin dariyar da yakeyi. Ruwa taje ta kawo mishi, bata ma gwada mishi tayin abinci ba tunda girkin Maimuna ne, tasan ko yana so ba zai taba ci ba. Wani lokacin ita kadai takan yi tunanin ko duka maza haka suke da adalci irin Ahmadi, sosai yake duk wani kokarin shi na ganin yayi adalci a tsakanin ta da Maimunar
"Ya kuke? Fatan dai kowa lafiyar shi kalau... Na shiga in duba yaran a daku nan su dana shigo, ina jin basu dawo daga sallar isha'i ba"
Kallon shi takeyi
"Anya kuwa? An idar da sallah, sai dai ko in sun tsaya wajen abokai ana hira. Duka lafiyar su kalau. Alhamdulillah"
Kai ya jinjina
"Alhamdulillah, ina Layla?"
Murmushin ta Maryama ta fadada
"Fushi take mun dan na mata fada kan saka kananun kaya"
Dariya yayi
"Layla manya... Yaran ne basajin magana, ni da ina yaro abinda za ayi mun magana ma bana farawa, idan akayi sau daya kam bazan bari a maimaita ba..."
Numfashi Maryama ta sauke, zata ce duk wani abu da ta saka Layla tanayi, bangaren aiki kuwa in ba tana makarantar boko ko ta islamiyya ba cokali bata bari ta daga. Girki tun tana koya mata har yanzun babu wani abu da bata iya girkawa ba. Tana da rigima, sosai tana da rikici, amman idan ba tabata kayi ba babu ruwanta da kai, ga fadanta baya rabuwa da wuri saboda mita da take da ita, kusan Maryama zatace duka yaranta sun biyo sanyin hali irin nata, kau da kai da sanin ya kamata irin na baban su. Jabir ne ma bashi da hakuri idan ka tabo shi.
Sai Layla tayi wani abin sannan take tuna cewa ba daga jikinta yarinyar ta fito ba. Matsalar da suka cika samu da Layla bai wuce yanda a rayuwarta take bala'in son kananun kaya ba, idan zata wuni da dogon wando da yar riga yafi mata dadi, gara ma ranakun asabar da Ahmadi ya ware yana zama a gida. Shine zaka ga tana yini yawo da hijabi, kamar duk gidan shi kadai ne take jin nauyi ko shakka kar yai mata magana. Amman da yan shekarunta ko atamfa ce skirt din sai tace a sha mata shi, ga kirar jiki da Allah yayi mata, wasu lokuttan Maryama kan jinjina kalar jikin da Layla take da shi, shisa take tsoron shigar da takeyi.
Bataso, amman da duk rana da take kokarin ganin ta rabata da kananun kaya, da ta daina sai mata, kudinta duk idan ta tara akwai gidan su Farida, nan cikin unguwa, islamiyyar su daya da Layla din, kuma ajin su daya, sana'ar gwanjo mahaifin Farida yakeyi, dila-dila yake kawowa daga kwatano, hakan yasa matar kan bude itama tana siyarwa cikin gida. Sai dai Maryama taga Layla ta shigo da abinta, duk yawancin kudadenta yanzun a can suke karewa, kuma sukan mata saukin kayan saboda sanayya. Idan ma tayi mata fada sosai, kwana biyu tana saka atamfa haka zakaga dakyar take motsawa saboda matsewar siket din da yake jikinta.
Zatayi karya idan tace abin baya damun ta, sai ta tuna zancen da mutane kanyi na cewar
"Dan riko wahalar sha'ani gare shi"
Wasu ma sukan ce
"Maraya akwai wahalar riko"
Duka biyun take gani akan Layla wasu lokuttan, amman duk wani abu da zaifi karfinta da addu'a take hada shi, Laylar ma addu'a takeyi mata, saboda girma take karayi, halittarta ta 'ya mace na kara fitowa, shisa yanzun Maryama ta numfasa kawai tana fadin
"Allah dai ya shirya mana, yaran yanzun magana har sai bakin ka yayi tsini"
Mikewa Ahmadi yayi
"Amin thumma amin. Abinda yafi tsini kam bakin ka zaiyi. Idan sun shigo nasan zangan su..."
Ya fadi yana dorawa da yi mata sallama, daman lafiyarta da ta yaran ya shiga dubawa kamar yanda ya saba ko aiki ya dawo, balle kuma tafiyar kwanaki hudu. Yayi kewar su ba kadan ba. Yana fita dakin Maimuna ya wuce, inda ya sameta ta fito falon tana zaune, yanayin fuskarta yake kallo, girma bai hana shi gane rigimar da take shimfide a kan fuskar ba
"Uwargidan Ahmadi..."
Kallon shi tayi tana kauda kai, tunda ta fito daga daki Huda ta fada mata ya shigo ya fita take kallon agogo, mintina sha ukun sai take ganin su kamar awanni sha ukku dan tasan yana wajen Maryama ne. Wani irin tuquqin kishi da shekaru basuyi komai wajen rage mata ba take jin yana taso mata
"Magana fa nake yi..."
Sake kallon shi tayi
"Ai na dauka a can zaka kwana"
Yanayin yanda tayi maganar ne yasa shi dariya
"Hmm..."
Ta furta, ba yau ya saba mayar da ita mahaukaciya ba daman
"Yi hakuri... Na shigo kina sallah, shine nace bari inje mu gaisa kafin ki idar"
Cike da rigima take kallon shi
"Ko dawafi nakeyi ai kasan na idar tun dazun dai. Sai kayi zaman ka kunata labari, kuma tunda girkina ne, kwana hudu bangan ka ba, ya kamata ace ka bari na fara sakaka a idanuwana tukunna kaje duk inda zakaje"
Murmushi Ahmadi yakeyi, zuwa yanzun indai rikicinta ya saba da shi
"Ba za'a kara ba Uwargida. Kiyi hakuri..."
Numfashi ta sauke
"An dawo lafiya?"
Ta fadi ciki-ciki har lokacin, sai da ya tabbatar ya jata da hira ta daina amsa shi dai-dai tukunna ya mike
"Da kaci abinci dai sai kayi wankan"
Kai ya girgiza mata
"Bari dai in watsa ruwan, kafin in fito kin hadamun abincin..."
Ahmadi ya karasa maganar yana soma tafiya. Mikewa tayi itama, so yayi ya wuce bangaren shi, amman yana son ganin su Rayyan, haka kawai ya kasa hakura, musamman da yasan in ba a hanya ya hadu da Rayyan din ba, ba zaije yayi mishi sannu da zuwa ba. Kowa zaije amman banda shi, yaso ya tambayi lafiyar yaran daya bayan daya, amman yana gudun jin ance Rayyan din yayi wani abu bayan tafiyar shi, Allah ne shaida da shi yake kwana a ran shi, da shi yake kuma tashi. Ko waya tayi kara sai gaban shi ya fadi, sai yayi zaton ko Rayyan ne ya dauko wata maganar da yayi nisa da gida.
Akan Rayyan ne yasan cewa zai yiwu ka haifi da ka dinga jin zuciyarka na rawa duk sanda zaka gan shi, yanzun da yake nufar dakin su Rayyan din sai yaga kamar yayi mishi nisa.
"Oh Allah..."
Ahmadi ya furta jin yanda zuciyar shi ke rawa
"Allah idan jarabta ce ka kadarta mu ta fado akan Rayyan, Allah ka bani karfin zuciyar daukar ta. Allah na yafe mishi duk wani laifi daya taba mun, wanda na tuna da wanda na manta. Rabbi ka shiryamun yarona, Kai ka bani amanar shi, kai ka sakamun kaunar shi, Allah karka sa ya zama rauni na"
Shine addu'ar da ya tsinci kan shi da yi, duk da ya kasa samun natsuwa, musamman daya tinkari dakin yaji wani irin wari da tashin hankali bai barshi fahimtar ko na meye ba farat daya, sai da ya kara kusantar dakin sannan ya gane warin sigari ne, badan cutarwar da takeyi ba, cutarwar da yagani da idanuwan shi akan abokin aikin su da bature ne dan kasar amurka, haka da wahala ka ganshi batare da sigari ba, kullum cikin buka ma cikin shi hayaqi yake, lokaci daya ya fara wani irin tari daya kwantar da shi, kafin ace kansar huhu ce tayi mishi muguwar illa a sanadin taba.
Ko sanda sukaje asibiti duba shi kafin a mayar da shi kasar shi inda ya mutu a can, yanda yake kokawa da numfashin shi Ahmadi zaiso duk wani mashayin sigari ace yana dakin asibitin dan yaga tashin hankali da illar da sigari takeyi ko zai yarda ya daina cutar da kan shi. Shi ko warin ma idan yaji sai zuciyar shi ta dinga tashi, tana daya daga cikin abubuwan da yaki jini
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..."
Ya furta a fili yana kasa kwankwasa kofar dakin jin warin sigarin da zuciyar shi taki taya kwakwalwar shi karyata cewa ba daga cikin dakin su Rayyan warin sigarin yake kara fitowa ba. Wani irin bacin raine da yake shirin danne firgicin da yake ciki ya saka shi tura dakin batare da sallama ba, haske ne gauraye da dakin saboda akwai wutar lantarki. Rayyan na zaune akan kujera ya dora hannayen shi kan teburin da yake gaban shi, Bilal na tsaye, inda ya juyo saboda turo kofar da su duka suka ji anyi
"Abbu..."
Bilal ya kira da