Showing 90001 words to 93000 words out of 150281 words

Chapter 31 - MARTABARMU HAUSA NOVELS LUBNA SUFYAN .txt

23 Nov 2025

3977

shi yana wani irin sauke numfashi. Allah kadai yasan halin da yake ciki tun shekaranjiya, musamman jiya kuma zuwa safiyar yau. Komai karfin hali yake, sanin Bilal na da rai baya nufin hankalin shi ya kwanta tunda bai ga ya motsa ba. Wata natsuwa ce take dawo mishi, ya kai dakika biyar kafin ya bude fuskar shi yana mikewa ya karasa in da Bilal din yake

"Bilal?"

Ya kira cike da alamar tambaya, duk da idanuwan shi a bude suke, yana son ya kara tabbatar da cewa da ya tashin

"Hamma"

Cewar Bilal, wani numfashin Rayyan ya sake fitarwa, da wani yanayi a fuskar shi ya ke kallon Bilal

"Karka sake tsoratani haka, Bilal karka sake tsoratani haka..."

Ya karashe maganar yana sake sauke numfashi, sai da yaga Bilal din ya dan daga mishi kai tukunna ya juya, hanyar kofa ya nufa yana budewa ya fita, hadi da ja musu kofar ya rufe. Anan bakin kofar ya tsugunna yana wani irin mayar da numfashi kamar yayi gudu. Godiya yakewa Allah da duk wani yare da yake fahimta, da zai iya kuka tabbas zaiyi na saukin da ya samu lokaci daya haka. Ya kusa mintina  biyar anan tsugunne kafin ya iya mikewa, kujerar da take ajiye irin na karfen nan ya zauna kan guda daya. Hutawa yakeyi yasan Ayya da Bilal labari zasu fara, yanda kan shi yayi nauyi sosai zai takura.

Yana nan zaune Abbu ya dawo

"Ya mai jikin? Har ya tashi?"

Abbu ya fadi, kai Rayyan ya jinjina mishi, harya karasa ya murza kofar Rayyan yace

"Ya Layla? Abbu ya take?"

Dan juyowa Abbu yayi

"Taji sauki, na barta da Maminta ma, abinci take ci sanda na fito"

Kai Rayyan din ya jinjina zafin da kirjin shi yakeyi yana yin sauki. Da Mami ta biyo Abbu sun dawo zaije wajen Layla. Amman yasan Mami batason shi a kusa da Layla, saboda haka zai jira sai ta tafi, zaiyi wannan hakuri. Wayar shi dai ya zaro daga aljihu yana tura mata sako

"Baki kirani ba da kika ta shi"

Yana shiga tana dawo mishi da amsa

"Sai da su Mami suka zo na tashi Hamma, naji sauki. Ya Hamma Bilal?"

Numfashi ya sauke

"Ya tashi yanzun shima. Allah ya baku lafiya. Ki kula da kanki, zan zo in ganki anjima"

Har yana shirin mayar da wayar aljihun shi yaji sako ya shigo

"Ina son ka Hamma"

Murmushi yayi, abinda ya kwana uku rabon da yaji ko alamun shi, sosai murmushi yayi har hakoran shi suka bayyana, a hankali wani sanyi yake sauka cikin kirjin shi, sake karanta sakon da ya zauna a kwakwalwar shi yayi saboda yana jin muryarta a cikin kan shi inya karanta daga wayar. Ya jima kafin ya iya mayar da wayar aljihun shi, ya kasa daina murmushi. Yanayin da yake ciki bayason ya bar shi, zaiso ace kullum yana cikin yanayin, kafin yayi mata magana tunanin fita ya nemi sigarin da zai sha yakeyi ko zuciyar shi zata kara rage zafi. Amman yanzun yaji baya bukata, dutsen da yake danne da kirjin shi ya daga da kalaman Layla.

Hamma yayi alamar baccin da yanzun yake jin alamun shi, amman bashi da halin kwanciya. Natsuwa ce ya samu shisa ma har baccin ya samu zuwar mishi.

*

Bacci ta sake komawa bayan tayi sallah, babu ciwon kan, sai zazzabi kadan da kuma duniyar da batajin dadin ta. Ta so ta dan watsa ruwa amman batajin karfin jikinta. Sai kuma lokacin Anisa tace zataje ta dawo, sanda ta dawo ta soyo mata kwai ta taho da ruwan zafi da kayan shayi data kullo su a ledoji. Sai kofi da cokali. Layla ta san tana da lakca shisa ta matsa mata ta tafi

"Baki ga naji sauki ba, kinga an fara test, ana iya yin wani babu tsammani, kuma idan akwai wani abin zan kira wayar ki ai"

Bataso tafiya ba

"Dan Allah ki tafi, ni bacci ma zan koma"

Sai da ta ga Layla din ta juya kwanciya da yake tun wajen karfe hudu da aka cire mata ruwan daya kare sai suka barta ta huta. Tafiya Anisa tayi don tayi shirin tafiya aji. Lokacin ne wayarta ta soma ruri, ganin Abbu a rubuce yasa cikinta hautsinawa, sabon zazzabi na dirar mata, amman idan taci gaba dakin daukar kiran su hankalin su zai tashi fiye da yanda tasan ya tashi. Batayi magana da Bilal ba, amman idan yaji zabinta na barin komai daya faru a tsakanin su tasan zai amince. Ta san boye komai shine saukin su, in ma sunce zasu fada ta ina zasu fara?

Kuma jiya Rayyan yace yana son ta, shi ya saukar da zazzabinta ya rage ciwon kan da takeji, ya rage kusan rabin damuwarta, shi ya bata kwarin gwiwar daga wayar Abbu har tana amsa sallamar shi

"Layla... Ya jikin naki?"

Numfashi ta sauke, kenan sun san bata da lafiya, tana da tabbacin Rayyan ne ya fada musu

"Da sauki Abbu, ina Mami?"

Ta tambaya

"Gata nan tana jinki, yanzun zamu karaso ma, muna Zaria"

Mikewa zaune tayi wata irin zufa na karyo mata, kanta take kallo tana neman alamun da zasu iya nunawa Mami wani abu ya faru da kuma yanda zatayi ta boye

"Hello..."

Abbu ya fadi jin tayi shiru

"Sai kun karaso Abbu"

Tayi maganar tana mamakin yanda akayi muryarta bata rawa. Sauke wayar tayi daga kunnenta, tabbas idan bata saita nutsuwarta ba Mami zata gane akwai wani abu, karyar da zatayi take nema amman gabaki daya kanta ya kulle, tana nan zaune tana tunani sai ganin su tayi sun shigo. Wani kukane yake neman taso mata da ta hango Mami, saboda a tsayin rayuwarta Mami ce komai nata, duk da Abbu ya zame mata mahaifin da ta rasa, Mami daban take, ko da tana cikin damuwar da bata taka kara ta karya ba haka takan shige jikin Mami tana mata sangarta, Mamin kuma zata biyeta ta lallasheta a wasu lokuttan in ta kula da gaske akwai damuwa a tattare da ita.

Yanzun ma kasa daurewa tayi, suna karasowa ta zagaya hannuwanta tana rike Mami, hawaye masu dumi na zubo mata, numfashi sosai Mami ta sauke tana samun natsuwa da taga Layla din, dagota tayi daga jikinta tana zama gefen gadon

"Menene na kukan kuma? Ai gamu mun zo"

Mami ta fadi muryarta na rawa, har cikin ranta take godewa Allah da yasa babu abinda ya sami yarinyarta. Jikinta ta taba tanajin da zazzabi

"Kin ci abinci?"

Kai Layla ta girgiza tana share hawayen da yake fuskarta

"Gashi Anisa ta kawomun shayi"

Abbu ta kalla

"Abbu"

Murmushi yayi

"Sai yanzun kika ganni?"

Dariyar karfin hali Layla tayi, amman tanajin yanda wani abu yake budewa a cikin kirjinta. A lokutta da dama na rayuwarta ta saka kafa tayi fatali da duk wata tarbiya da suke dorata a kai, saboda tana ganin a kasan kaunar su akwai rashin wayewa, akwai dogon bambancin da take gani tsakanin yanda sukayi tasu rayuwar a baya da kuma yanda rayuwa take tafiya yanzun.

"Babu wani abu zamani Jabir, duniya bata canzawa, mutanen cikinta ne kawai suke canzawa, bambancin yanda mukayi tamu rayuwar da yanda ku kukeyin taku yanzun shine zabi..."

Mami ta taba cewa Jabir sanda yake mata maganar cewa zamanin su da kuma na yanzun daban ne, sun jima suna dariya bayan Mami din ta tashi, a ganinsu ba zata taba fahimta ba, ashe sune basu fahimceta ba, akwai tarin ma'anoni a kalamanta, ko kan maganar kaya da take yawan yiwa Layla din, ta dauki shekaru tana mata fada da nasiha a kai sai yanzun take kallon abin da kalar idanuwan da Mami ta ke taso ta duba. Abubuwa da damane suke ta mata yawo. A cikin abinda ya faru a kwanakin nan biyu ta daina kokarin gane ya akayi abinda ya faru ya faru, saboda bata da wannan amsar, ta dai san babu tirsasawa a al'amarin saboda rudanin da take ciki shi Bilal yake ciki.

Abu biyu zuwa ukku ta sani a yanzun, kafafuwanta ta dauka taje gidan su Bilal, da ta tura taga basa nan zata iya juyawa kamar yanda Rayyan ya taba balbaleta da fadan shi harda rankwashi da ta kai musu abinci taga basa nan ta zauna tana jiran su. Yana shiga ya ganta ya rankwasheta yana kama hannunta, dakyar ya bari ta saka takalma

"Idan kika ga bama nan karki kara zama, baki da hankali ke kam sam ko? Baki san maza bane kawai a gidan? Karki kara zuwa ki zauna idan ni ko Bilal bama nan, dakin tura dakin ki juya ki tafi gida, kina jina?"

Harya rakata bai daina fada ba, da tabi maganar shi, tunda ko suna nan din baya bari ta zauna. Tana shiga zai mike, shisa ta daina sallamar masu abin hawa. Ko a ranar dan tana tsammamin zata same sune, shisa ta sallami mai napep din. Tunda tana son taga tafiyar Rayyan din in yaso ita da Bilal sai su koma makaranta. Amman da ta juya da taga basa nan, da ta janyo dakin ta juya, sai ta zabi ta shiga ciki harta zauna. Idan Mami taji tana da yakinin tambayar farko da zatayi mata shine

"Me kikaje yi gidan su Rayyan?"

Kuma bata da amsar wannan tambayar, uzurin duk da zata bayar a cikin kanta ma bamai karbuwa bane ba. Akwai abubuwa da yawa da ta fahimta yanzun, abubuwan da take dauka a matsayin takura da batasan kariya bane a wajenta. Tun jiya take daukar alkawurra kala-kala, ciki harda sauraren duk wani abu sa Mami zata fadi da kuma yin aiki da shi, dan taga alama maganganun na da karfin kareta daga abubuwa da dama. Da ta saurare su da bata zo inda take yanzun ba, amman tana jin kamar lokaci bai kure mata ba. Ganin Mami din ya sa duk ta kara jin karfin ta ya karasa karewa.

Ita ta taimaka mata taje bandaki ta kara kuskure bakinta suka dawo, likita ne ya shigo yin round da yake dakin su hudune a ciki, akwai dai yar tazara tsakanin wani gadon zuwa wani, kuma akwai wasu gadajen da babu kowa, su Abbu fita sukayi sai da aka gama sannan suka dawo.

"Wai idan naci abinci sai a kara sakamun ruwa yace, zan kara kwana sannan su sallameni"

Kai Mami ta jinjina mata, tana daukar kofin da yake cikin kwandon da Anisa ta kawo. Shayin ta hada mata tana dauko yar kular ta bude mata wainar kwan, ta fara cine Abbu yace

"Bari in koma wajen su Bilal in kara ganin ya nashi jikin tun da ita ta samu"

Kai Mami ta jinjina

"Kayi mishi sannu"

Dubu sha biyar ya kirga ya bata yana barin biyar a jikin shi, karba tayi hadi da yin godiya, ita da Layla suna mishi addu'a da bada sakon yiwa Bilal din sannu da jiki. Daurewa Layla tayi ta shanye shayin tas, wainar kwance ta kasa cinyewa, karfin hali takeyi kar Mami ta fahimci wani abu, hira sukeyi a hankali, har akazo aka kara mayar ma da Layla ruwan, da yake an saka allurai a ciki, baccine ya dauketa. Mami na nan zaune Anisa ta dawo, gaisawa sukayi ta wuce da fadin zata dora girki

"Kina ta shan hidima, idan akwai waje me kyau ki siyo kawai Anisa"

Mami ta fadi tana bata dubu uku, tasan duk tsadar abincin dai nasu su uku ba zai wuce dubu dai-dai ba. Karba Anisa tayi dan kuwa da gasken a gajiye take jinta. Saida tayi sallar azahar sannan ta dawo, tana kawo musu nasu sallama ta kara yiwa Mami saboda tana da wata lakca har karfe hudu. Har tana saka Mami yin tunanin ya za'ayi yara ba zasuyi rashin lafiya ba da wannan zirga-zirgar da sukeyi. Ga shi saika dawo daga daukar darasi zaka fara neman abinda zakaci

"Kullum daman sai kun dawo sannan kuyi girki?"

Ta tambayi Layla cike da damuwa bayan ta tashi, dariya Layla tayi

"Muna ci a cikin makaranta, mun mafi yin abincin dare dai, ko da safe mu girka kafin mu fita idan babu lakcar safe"

Numfashi Mami ta sauke, babu wani abu a karatu nesa da gida banda wahala a nata ganin, saboda idan a gidane zakaje ka koma kuma ka sami abinci a girke, shisa duk in suka dawo sai taga sunyi zuru-zuru. Ayita maganar wahalar karatu ce, nan kuwa harda kujuba kujuba da rashin samun abinci akan lokaci

"Kinga da kinyi zamanki BUK kikaqi"

Murmushin Layla tayi mai ciwo, saboda a karo na farko maganganun Mami din sun zauna mata, da ta zauna a BUK din abin nan da bai faru ba, saboda ina taga Bilal din ma in ba hutu ya dawo ba? Batason tsaurara tunani a kai har mami ta fahimci akwai wani abu

"Kai Mami, baki ga su Hamma ba har sun gama, sauran fa sati uku a fara jarabawa...da an dawo an karayin wata nima aji uku zan shiga"

Kallonta Mami tayi

"Babu in shaa Allah kamar kece da rayuwar"

Dan murmushi ta sakeyi

"In shaa Allah"

Ta fadi tana saka Mami fadin

"Hmm..."

Kawai saboda ganin Layla ya nutsar da ita, amman akwai wani yanayi da zuciyarta take ciki wanda ta kasa fahimtar shi, watakila yana da alaka da kalar rashin tarbiyar da ta dinga cin karo da shi tunda ta shigo makarantar, yarane kala-kala, wasu matan kallo daya zakayi musu daga fuskar su ka gane yaran hausawa ne kuma musulmi, amman shigarsu tayi hannun riga da wannan, ga shi sai rike juna suke da maza kamar hakan bakomai bane ba, ga gungun dalibai duk an jera an taho tare anata hada kafadu da sunan za'a tafi aji. Addu'ar duk da tazo bakinta yinta takeyi, bataje jami'a ba, tana jin labari kala-kala da yake tattare da jami'a dai.

Amman taga yaran da suka shiga cikinta suka fita kalau, yaran da suka tsallaka kasar ketare sukayo karatun su batare da tarbiyar su ta sami tangarda ba, hakan baya nufin kowa ma zai kasance a haka, idan babu rashin ji kacokan na yaro, akwai mugayen abokai da tasirinsu mai girma ne. Illar jami'a zatayi dai-dai da rashin illarta idan ma illar batayi rinjaye ba kenan.

"Allah ya shirya mana, Allah ya tsare mana"

Shine abinda taita furtawa sanda suke hanya. Kusan har karfe shidda suna garin Zaria. Sosai Mami taso tafiya da Layla, amman taqi

"Nafa ji sauki Mami, kuma mun kusa fara jarabawa mu dawo gida hutu gabaki daya"

Abbu kuma ya goya mata baya da fadin

"Nan da kwana biyu sai mu kara dawowa mu kara duba su"

Zuciyar Mami ta kasa nutsuwa, Ayya ma dakyar Abbu ya rabota da asibitin bayan sunje daukarta. Can ma suka sami Aisha da wata kawarta sun zo duba Bilal din sunyo abinci sun kawo. Abbu najin labarin Aisha a wajen Ayya, amman yaune ya fara ganinta, yarinya ba dai kunya ba, dan dakyar ta gaishe da su, ko sallama batayi ma su Bilal ba suka fice suka tafi. Sai da suka jira ta karbi lambobin abokan Bilal din, tana tunawa Mami da cewa itama zata saka Layla ta tura mata lambar Anisa. Haka suka bar garin Zaria da rashin nutsuwa daban da wanda suka shigo garin da shi.

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 17, 2020

22

"Shiru-shiru halina ne Bilal, shisa naka yake mun yawa a kwanakin nan"

Rayyan ya fada mishi, yasan baiyi maganar dan yana jiran amsa ba, ya fadane kawai saboda abinda yake ran shine. In da ya tsammaci amsa ne Bilal din bashi da abin cewa, shiru-shirun da yakeyi ba zabi bane ba, dole ce ta saka mishi. Ya kanji mutane sunyi maganar tsoro, sunyi maganar kwana cikin firgici, yanzun ya gane ma'anonin kalaman su, baccin kirki baya samu sosai. A tsorace yake al'amuran shi, ko kallon shi yaga Rayyan ya cikayi sai yaga kamar yana zargin akwai abu mai girma da yake boye mishi, kamar yana so ya gane cewa yaci amanar shine.

Sanda duk zaiyi waya da Abbu sai zuciyar shi ta doka, muryar Abbu yanzun batayi mishi komai sai kara gigita mishi lissafi. Hirar su da Abbu batayin tsayi, saboda a kagauce yake daya sauke wayar kafin ya fadi abinda baiyi niyya ba. Yana fadama kan shi maganar da Malamai da yawa sukayi a kaine na boye zunubi irin wannan, saboda bayayin komai sai yada rikici da haifar da shakku a zukatan mutane, in dai har ranka zaka tuba saboda Allah, zaka kiyaye sharuddan tuban, to kayi shiru shine mafi alkhairi, Allah ya sirranta zunubinka ne saboda dalilai da dama. Har wa'azin ya lalubo ya saka a wayar shi ko zai saukaka mishi jin nauyin amanar daya ha'inta da yakeyi.

Kwanan shi biyu a asibiti aka sallame shi, duk yanda Rayyan yayi mishi maganar ya huta kafin ya koma makaranta sai ya kasa. In ya zauna baya komai sai tunani, zuwa makarantar na rage mishi tunani, yakan yi kokari sosai wajen mayar da hankalin shi kan lissafin da akeyi. Sai da aka hada sati daya a hakan, kafin ya dauki wayar shi yaga shigowar saqo, ya dauka Aisha ce, dan itace comfort din shi a wannan lokacin, har tausayin damuwar da yakan gani a cikin idanuwanta yakeyi, damuwar da yake da yakinin shine silarta

"Nawan wani abu na damun ka, nasan zaka fada mun inda zaka iya. Amman bana so wallahi, ko menene yake damun ka yana mun ciwo a zuciyata saboda bansan me ya kamata inyi in taimaka maka ba"

Murmushi ya iya yi mata, duk wani abu da zatayi domin shi tana comforting din shine, a lokaci daya kuma tana saka shi jin yanda da duk dakika bai kyauta mata ba itama. Kamar yaci amanar duk tarin kaunar da takeyi mishi. Shisa yake ta wasa da wayar a hannun shi, bai bude ba, jiya ya kasa zuwa ya ganta, ta kira shi da daddare bai daga ba, kuma baibi kiran ba da safiyar ranar, sai ya dauka itace tayi mishi sakon a lokacin, ya fi mintina goma yana tararrabin budewa, sai daya duba yaga sunan Layla sannan wani abu ya tsirga mishi. Tun da akayi abin bai yarda ya sakata a idanuwan shi ba, baisan ta inda zai fara ba.

Jikin shi na rawa ya bude

"Bansan me zance ba Hamma, bansan me zan fada maka ba, har raina ina so in dora laifin komai a kanka ko zan samu sauki, amman na kasa, saboda kana daya daga cikin mazan da suke a rayuwata da nake da tabbacin ba zasu taba cutar dani ba. Har yanzun ina cikin rudani, ban san ko abinda zan fada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login