Showing 3001 words to 6000 words out of 150281 words

Chapter 2 - MARTABARMU HAUSA NOVELS LUBNA SUFYAN .txt

23 Nov 2025

3989

taimakeni, Malaminkin nan da yayi miki aiki kije mun wajen shi ko zai taimaka mun akan Ahmadi, dan Allah Khadi, wallahi ya kara auren nan zuciyata bugawa zatayi"

Dariya Khadi tayi har tana saka Maimuna jin haushi

"Ai gara da kika farka, idanuwan ki suka bude... In anyi duniya da Manzo kin kawo kukan ki inda za'a share miki"

Wannan maganganun sun kara karfin amintakar da take tsakanin su. Kudade Maimuna ta baiwa Khadi masu yawan gaske, dan idanuwan ta sun rufe da zafin kishin da bata tunanin addu'ar neman sauki akan shi, ta saki Allah ta komawa yan tsubbun da ta aminta sune kadai maganin matsalar da take fama da ita yanzun. Sai dai wani sabon tashin hankalin ta shiga dan Malamin Khadi ya hango dole sai Maryama ta shigo gidan sannan zata iya nasara a kanta

"Da ayaba akayi mishi wannan mallakar, da ace baki ma farga da wuri ba da yanzun sun shiga tsakanin ki da Ahmadi, dole sai ta shigo gidan za'a san yanda za'a karya sihirin..."

Ya kuma tabbatar mata dole saita kara jajircewa daga ita har yaranta. Kullum cikin boye-boye magunguna take da take bankadawa ma cikinta da yara a matsayin karya tambaya da kuma kaikayi koma kan masheqiya. Wasu da inta jika Ahmadi yagani sai tace mishi maganin shawarane da Gwaggo ta hado mata, wani lokaci harya karba kanshi tsaye yasha shima, tunda ta gano wannan hanyar cewa bokon shi bata rabashi da magungunan gargajiya ba take bashi wasu kanta tsaye da sunan maganin Basir ko shawara ko sanyi.

Kishin da yake cinta ne yasa ta zabi daga musu hankali daga ita harshi ko zai kara saka tai gabala akan shi ya fasa auren nan, amman kullum nuna mata yakeyi asirin da su Maryama sukayi mishi mai karfine dan bazai taba iya fasa aurenta ba. Yanzun ma kallon shi take yanda yake yabonta kamar ita kadai din ta ishe shi, harya karasa cin abincin yanayin hamdala

"Sannun ki da kokari, Allah yai miki albarka"

Ahmadi ya karasa yana mikewa ya tattara kwanukan ya fita dasu dan ya taimaka mata, duk idan ta wuce da turtsetsen ciki haka, koya dawo yaga gidan qwal saiya kara jinjinawa mata, ko a tunani ya hasaso kanshi da cikin jikinta sai ya hango yanda zai wuni shame-shame a kwance, amman ita harda kokarin girki, ko da tana laulayi sai yayi da gaske take kinyin girki, koyane saita lallaba ta dafa mishi abinda zaici. Shisa darajarta a zuciyar shi mai girma ce. Ganin da yayi magriba ta karato ya saka shi daura alwala kafin ya karasa dakin yana fadin

"Bari in fita masallaci...."

Batace mishi kanzil ba, sosai yake kewar hirarrakin su da yanda halin ko in kula din da take nuna mishi yake ci mai tuwo a kwarya. Haka yasa kai ya fice daga gidan. Ko da sukai sallar Magriba nan suka tsaya da wasu cikin unguwa danjin labarin Makka daga sabon Alhajin daya dawo satin daya fita wato Sambo. Da yake Ahmadi ba ma'abocin zaman majalissa bane ba, tunda Alhaji Sambo ya dawo basu hadu ba sai yau, yakan tsaya a lokutta irin haka a gaggaisa dan karamcin mutanen unguwar ba karami bane ba. Haka Alhaji Sambo ya dinga nishadantar dasu da labarai kayatattu yana kwadaita musu zuwa aikin Hajji duk idan halin hakan ya samu.

Kiran sallar Isha'i ya tarwatsa taron nasu, inda ana idarwa kai tsaye Ahmadi gida ya wuce, yana shiga soron ya mayar da gidan ya rufe sanin ba bako zasu karayi ba, inma sunyin a kwankwasa yaje ya bude. Jin shirun gidan ya tabbatar mishi da yaran sunyi bacci, da ya shiga daki kuwa Maimuna kadai ya samu, yasan harta kaisu dakin da suke kwana ta kwantar, baisan kuka takeyi ba saida ya zauna gefenta

"Subhanallahi.... Maimuna? Lafiya? Me ya faru? Ko jikinne?"

Ahmadi yake tambaya hankali a tashe yana riko hannunta, kai take girgiza ma duk tambayoyin shi alamar a'a kafin tace

"Me yasa ba zaka rayu dani kadai ba? Me kakw tunanin Maryama zata iya baka wanda ni ba zan iya ba? Ka fadamun dan Allah kagani, Wallahi Ahmadi zan maka komai. Karka tonamun asiri ka hadani da wata...."

Kallonta yake yanda kwanaki basu wuce sittin ba suka rage a daura auren shi da Maryama, har a sujjadar shi addu'ar kwanciyar hankali da dangana yakewa Maimuna saboda kishinta ya fara bashi tsoro, sake rike hannunta yayi, cikin taushin murya ya fara magana

"Da wanne yare zan fahimtar dake ba zan kara aure bane dan in wulakantaki? Maimuna baki yarda da kalar kulawar da nake miki bane ba? Shin a duk rana bana nuna miki yanda kike da muhimmanci a wajena? Ba zai canza ba dan na kara aure"

Wasu hawayen ne suka kara zubo mata saboda yaki fahimtar tsoronta, yaki gane ba soyayyar shi bace bata yarda da ita ba, soyayyar ce batason rabawa da kowa, tsoro take kar auren nashi ya zama sanadin da za'a rabata dashi gabaki daya

"In dai ba wahayin auren nan akayi maka ba dan girman Allah, dan datajar Ma'aiki da iyayen mu kayi hakuri"

Hannunta ya saki, duk hakurin da yake a kanta ya fara gajiyawa, tanayi kamar bata taba ganin an kara aure ba, kiriri kiriri take nuna kamar haramci yake son aikatawa ba abinda musulunci ya yarje mishi ba

"Maimuna kinga gara ki kwantar da hankalinki ko zamu samu zaman lafiya tunda auren nan ba fasawa zanyi ba"

Hawayenta ta share tana saka idanuwanta cikin nashi

"Tunda an shanyeka daman ya zaka iya fasa aure?"

Rai a bace yake kallon ta shima

"Wacce irin maganace wannan? Ba zaki daina baiwa sh Gwaggo damar darsa miki wasu zantuka marassa kan gado a rai ba ko?"

Kada kai Maimuna tayi cikin zafin rai

"Babu wasu maganganu da ake darsa mun a rai sai gaskiya. Yanzun daga ina kake tunda ka fita? Adalcinne kake son gwadawa bayan tun safe ka fice daga gidan nan, dan lokacin naka da zan samu ma tun kafin ka aurota sai ka raba mana tare"

Kai Ahmadi ya dafe yana rasa ta inda zai fara shawo kan wannan al'amarin

"Idan nace miki ba wajen Maryama naje ba zaki yarda?"

Yanda take kallon shi ya sakashi dorawa da

"Tunda nai maganar kara aure kike neman laifina a duk wani abu da zanyi, karyatani kike ko gaskiyata na fada miki. Halayen nan babu inda zasu kaiki Maimuna, karki rage kimarki a idanuwana wallahi"

Yanda ya karasa maganar yasa wani abu tsinkewa a cikinta, da gaske an asirce mata Ahmadi, in har da bakin shi yake furta hango raguwar kimarta a idanuwan shi an asirce shi

"Ashe kimata zata iya raguwa a idanuwan ka? Kaga dalilina na gudun aurenka ko? Kaga abinsa suke sa kana fadamun tun kafin ta shigo, wanne irin wulakanci zan gani kenan nan gaba?"

Take maganar tana wani irin kuka da yakeji har ranshi shisa ya mike saboda bayason biye mata, bayason bata mata rai fiye da yanda yake a bace ko dan cikin jikinta. Kuma da a karo na farko ya zanta sirrin gidan shi da babban abokin shi Nasiru saboda tsoron kalar kishin Maimuna daya gani shawara ya bashi mai kyau, kalaman Nasiru sun zauna mishi sosai

"Su mata ba'a biye musu, hakuri ake da halin su saboda wasu lokuttan kamar yara haka suke da karancin tunani. Laifine kayi mata da kara aure dole kuma tayi kishi, na kula shi kishin nan ya bambanta a tsakanin mata, kowacce da kalar nata. Kayi hakuri da duk wannan tashin hankalin da takeyi, da anyi auren zata hakura. Gani take kamar intaci gaba da daga maka hankali zaka hakura ka fasa. Kai dai karka biyeta, in ranka ya baci kabar mata gidan saika huce ka koma gudun biyewa zugar shaidan"

Aikam shawarar Nasiru ta mishi amfani wajen kaucewa rikicin rashin dalili da Maimuna kan takale shi da shi. Yanzun ma dakin yaran yaje yana samun tabarma ya shimfida kusa da yar katifar su da suke bacci a kai ya kwanta. Yasan halin Maimunar shi, duk fadan da zasuyi bata iya bacci ba'a kusa dashi ba, da almatsutsan kishin nata sun sauka da kanta zata zo ta neme shi. Dan haka ya lumshe idanuwan shi yana musu addu'ar tabbatar alkhairi a wannan auren da zaiyi da kuma zaman lafiya bayan yin shi.

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:05 PM - 111: Nov 1, 2020

2

May 1985, Kano.

Da gaskiyar iyaye da kance kukan yaro yafi komai daga hankali, har kasan ranta take jin kukan Rayyan, a gaggauce ta karasa wankan, sabonta ne sai ta saka hijabi idan ta daura zani sannan take fitowa daga wanka, kamar yanda takan shiga da ita. Amman yanzun kam haka ta fito, hijabin ma a bandakin ta baro ta. Ganin ta lallaba Rayyan din yayi bacci shisa ta lallaba tadan watsa ruwan ta fito, ashe ba nisa baccin yayi ba. Tana daga labulen gabanta nayin wata irin mummunar faduwa ganin Maryama data mika hannu tana shirin daukar Rayyan

"Me kike kokarin shafa mishi?"

Ta furta tana karasawa da sauri ta hankade Maryama da take tsaye. Sallar la'asar ta idar, tana zaune tana jan casbi kamar yanda takan wuni tanayi, ko karanta wani littafin da take tunanin zai amfani rayuwarta tunda ta shigo gidan. Da yake da ta gama firamare tayi makarantar kwana har aji uku, da maganar auren su da Ahmadi a kanta ma ta karasa aji ukkun. Bata tsammaci tarbar kwarai a wajen Maimuna ba, amman tayi mamakin kalar kiyayyar da take nuna mata kamar itace mace ta farko data fara shiga gidan aure a matsayin mace ta biyu. Ba zata manta ranar da aka shiga da ita dakin Maimuna watanni ukku da suka shige dan karrama Maimuna a matsayinta na uwargida kamar yanda tsarin al'ada yake.

Sam bata ga fuskar Maimuna ba tunda kanta a rufe yake kasancewarta amarya. Kalaman Iya Asabe da take fadin

"Wanda duk yake a dakin nan yasan halin da kike ciki, dan kishiyar nan anyi mana, wasun mu fiye da daya. Sai anyi hakuri, ko da babu tsira mai nisa tsakanin ki da Maryama kanwa ce a wajenki a gidan aure. Saboda haka ga amanar ta..."

Iya Asabe bata karasa maganarta ba Maimunar ta katse ta da fadin

"Iya ki takaita kalamanki, indai amanar Maryama ce ban dauka ba, karku doramun nauyin da ba zan sauke ba..."

Daga inda Maryama take zaune tana jin salallamin da duk wanda yake cikin dakin yakeyi cike da mamaki

"Inda amana ba zaku rako Maryama dakina ba wallahi, ba zaku dauketa ku liqawa Ahmadi ba..."

Ba zata manta yanda taji takun tafiya ana barin dakin daya baya daya ba. Har Iya ta kamata suka fice saboda yanda Maimuna sam taki sauraren nasihar da Iya taso tayi mata, tana barinta da furta

"Allah ya saukaka"

Kafin su fita daga dakin. Maimuna bata canza kalamanta ba ko bayan da Ahmadi ya hadasu da sunan yi musu nasiha

"Ka dauki matarka ku fitar mun daga daki Ahmadi, ku fita ba sai kun haskamun yanda zaku kasance da juna tsayin daren yau ba, wallahi hakurina yana gab da karewa..."

Maimunar ta karasa maganar da rawar Murya alamar kukan da take kokarin tarbewa. Ita kam zatace firgicin da ta tsinci kanta ya girmi wanda kowacce mace take tare dashi a darenta na farko. Daga ranar kuwa har yau babu wata magana ta arziqi data hadata da Maimuna, banda mugayen kallo da takan watsa mata duk idan ta wuce, tana jin labaran kishi, amman na Maimuna daban ne, ga yan uwanta da taga alama wajen zaman jegon Rayyan suna tayata.

Ba tsoron biye rigimar da Maimuna takan takaleta da ita a duk rana takeyi ba, kalaman Ahmadi ne suke tausarta

"Da bana sonki ba zan aureki ba Maryama, kamar yanda kauna ce tasani auren Maimuna kema haka. Idan ina da mutunci a idanuwanki zaki tayani kaucewa rigima da Maimuna, dan Allah ki kauda kai daga lamurranta, ki tayani wanzar da zaman lafiya a tsakanin ku gwargwadon iyawarki"

Tun kafin zama karkashin inuwar aure ya hadata da Ahmadi ta tabbatar da nagartar shi. Ta dauka tasan soyayya a iya tsayin lokacin da suka dauka kafin auren su, sai yanzun take ganin banbanci. Yanda Ahmadi yake kula da ita, yake gudun duk wani abu da zai sosa ranta ya kara daga daraja da matsayin shi a zuciyarta. Saboda shi zata cigaba da kauda kai daga halayen Maimuna har Allah ya fahimtar da ita cewa su dukansu zaman aure sukeyi, kuma ita da niyyar mutu ka raba ta shigo gidan, babu inda zata tafi.

Shisa take kokarin ganin bata shiga harkarta ba, bata taba ganin gidan da keda kishiyoyi kowa na abincinta daban ba tun tasowarta sai a nasu gidan. Ta dafa sau biyu, ba zatace ga abinda ya faru ba, Ahmadi ya ce mata kowa abincin shi zai dinga dafawa, abin har yanzun wani iri yakeyi mata. Ga yaran Maimuna da shiga rai, musamman Zubaida, ko dan Ahmadi har ranta take jin yaran. Kiri-kiri Maimuna ta hana mata rabarsu, ko inda take basa zuwa, buta wannan idan tata ce basa tabawa, in ta dan samu sunje kusa da ita to Ahmadi ya dawo gidan, kuma ranar itace da girki, shima kome zata basu kai suke girgiza mata a tsorace.

Yau ma kukan Rayyan da take tajine yai mata tsaye, taso ta share, amman taji shigar Maimuna bandaki, kuma tasan sauran yaran suna makaranta. Tunanin ko an dora shi a samane ya fado shisa yake wannan gigitaccen kukan yasata tashi ta shiga bangaren Maimuna din, komin yanda basa ga miciji yaron baisan me duniyar take ciki ba balle zafin kishi irin na mahaifiyar shi. Tana shiga taga kuwa wajen mitsilniya yaja zanin shimfidar ya nade fuskar shi da shi, samu tayi ta cire mishi, ta gyara ne zata dauke shi taji shigowar Maimuna, bangazar da tayi mata da babu bango a kusa zata iya faduwa. Rayyan din Maimuna ta dauka tana saka shi a jikinta hadi da jijjiga yaron

"Kashe mun shi zakiyi Maryama? Meya kawoki dakina?"

Kalaman Maimunan taji har ranta, sun mata zafi matuka

"Wacce irin magana ce wannan? Kukan shi naji yayi yawa, kuma naji kamar kin shiga bayi shisa nazo in duba"

Cike da rashin yarda Maimuna take kallonta, Gwaggo Bare tayi mata kashedi karta bar Maryama na rabar mata yara, kafin ta shafa musu abinda in rayuwar su bata salwanta ba za'a sabauta su. Yanda tayi nasarar mallake Ahmadi ba zata bari tayi nasara a kanta ba sam. Karfi da yaji jituwa ta musu karanci tsakaninta da Ahmadi, laifinta yake gani yanzun a duk wata karamar magana da zasuyi. Ranar da aka daura mishi aure da Maryama ne rana mafi muni da tashin hankali a rayuwarta. Ba zata manta bayan fitar su shi da Maryama daga dakin yanda ta dafe cikinta tanajin kamar zai fito duniya ranar saboda yasan kalar tashin hankalin da take ciki.

Kwanciya tayi a kasa tana sakin wani irin gunjin kuka zuciyarta kamar zata fado, a haka Ahmadi ya shigo dakin yana kamata

"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un... Maimuna me kikeyi haka? Dan Allah ki rufamun asiri, kinga bake kadai bace ba... Kiyi hakuri, kiyi hakuri kisawa ranki salama, inda nasan kishinki yakai haka wallahi dana hakura da auren nan... Oh Allah na"

Yake fadin yana sake riketa a jikin shi ganin yanda numfashinta har sama-sama yake saboda kuka

"Wata zaka raba, Ahmadi wata zata dandani soyayyarka yau, dan Allah karkaje, karka hada mun jikinka da nata, karka cakuda kaunata data wata, Ahmadi mutuwa zanyi Allah idan nasan a wajen wata zaka kwana"

Maimuna take maganar kamar bata cikin hayyacinta. Har yau ba zatace ga yanda akayi ya sulalace yabar dakin ba, bama zata tuna ko ta runtsa ko bata runtsa ba, a satin farkon nan ta wahala. Tayi mamaki da mata suke kiran nakuda tafi komai ciwo a sha'ani na rayuwa. Zata zabi haihuwa goma a jere indai za'a koma baya a goge Maryama daga rayuwar Ahmadi, ko haihuwar Zubaida data kwana hudu cikin matsananciyar nakuda kamar ba zatai rai ba bai kai mata zafin ciwon da takeji a zuciyarta duk idan Ahmadi ya kasance a dakin Maryama ba.

A kwanakin bakwai bata tsaya tasan me suke ci shida Maryama ba, dan batai mishi karyaba washegari daya shigo mata daki kamar bai hada shimfida da wata ba

"Idan abin kari kake jira zaku wuni da yunwa daga kai har ita, wallahi zan zabi mutuwa akan in dafa abincin da Maryama zataci"

Da suka kwana bakwai ma ta karbi girki ko lafiyar kirki bata da ita, tana ganin Maryama da salo dan ta zuba mata wani abu tace zatayi girkin. Su Zubaida gidan Yaya Ayuba ta turasu sukaci abinci, itama daga can din aka kawo mata, washegari da taga ta shiga ta dafa tazo tayi mata maganar da ko amsa bata iya bata ba, Ahmadi na dawowa ya shiga dakinta da ya duba karfin jikinta tace mishi

"Ba zan iyacin abinda duk ya fito daga hannun matarka ba, yarana ma ba zasuci ba ballantana a barbada mana abinda aka baka aka mallake ka"

Yanda yake kallonta rai a bace bai ko girgizata ba

"Maimuna yaushe ne zakiyi sanyi akan maganar Maryama? Da kika taso gidanku abinci kikaga an raba? Me yasa nine zan fara wannan al'adar dan kawai kin dauki zafin kishi kin saka a ranki"

Batasan ko yanda ya nuna dan Yayya tayi hakurin zama da kishiya itama ya zame mata dole tayi wannan bane a fakaice ya taba zuciyarta, ko kuma maganganun da yake mata a fadace saboda Maryama sune suka tunzurata ba, amman bataso hawayen da suka zubo mata ba

"Ni dai na fada maka, kai za'ayiwa asarar abinci saboda wallahi ni ba zanci ba..."

Runtsa idanuwan shi Ahmadi yayi yana bude su a kanta

"Idan akayi hakan shikenan? Idan kowa ya dafa abincin shi yayi miki?"

Kai ta daga mishi, bai sake furta wani abu ba yasa kai ya fice daga dakin. Idan fushi yayi ma shiya jiyo. Ita kama tasan ba zataci duk wani abu da zai fito daga bangaren Maryama ba, su Khalifa ma daki ta sakasu taja kunnen su akan Maryaman ganin yanda take wani jansu a jiki. Dan Zubaida ma ca tayi mata Dodo Maryama take zama da dare, idan ta karbi abin hannunta zata zo ta cinyeta tana bacci. Yaran kuwa har ransu suka dauki hudubar mahaifiyar tasu

"Bana so, karki sake shigomun daki, idan siqewa kikaji yanayi bance ki taimaka mishi ba....idan burgeni kike sonyi Maryama dan girman Allah ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login