Showing 30001 words to 33000 words out of 150281 words
Rayyan daban ne, su Rukayya ma baya magana dasu mai nisan da taji yanayi da Layla din. Yanda ya tsare yarinyar da idanuwa yake yanzun yasa ba zuciyarta ba har kafafuwanta ma rawa taji sunayi.
Tana can tana tsoron Layla karta lashe kurwar Bilal, ashe lallabowa tayi wajen Rayyan, shiru yayi yana kallonta
"Tambayar ka nake kana jina"
Yanda yakan yi duk idan bayason yin magana an saka shi yayi dole shi yayi da fuskar shi yanzun ma
"Ina magana da ita ne Ayya..."
Ya amsa, yana saka kirjinta wani irin lugude, ko ita Rayyan baya tsayawa yayi wata magana da ita. Bilal ma ta kanga yana bin Rayyan din idan yana son magana da shi. Asali yaune rana ta farko tun tasowar shi da taji yace yana magana da wani har ya tsayar dashi dan basu gama ba
"Rayyan..."
Ayya ta kira wannan karin da bayanannen tsoro a muryarta
"Idan nagama zan shigo"
Ya fadi yana dauke idanuwan shi daga kan Ayya. Hannun Layla ya kama yana fisgarta cikin yanayin da yasata binshi dole, suna barin Ayya tsaye ta saki baki cike da mamakin abinda ya faru a gaban idanuwanta. Cike da ta'ajjabin da gaske a gabanta Rayyan ya damki hannun Layla batare da tunanin abinda yayi ba dai-dai bane a tafarkin addini idan bai guji bacin ranta ba, idan ma ji yake dan in aka bibiya ta wani bangaren ya hada jini da Layla, kuma sun taso gida, ai hakan baya nufin ita din muharramar shi ce.
Bayan wannan ma, yaushe Rayyan ya fara magana da Layla, yaushe ya sakata cikin jerin mutanen da yake kulawa, harma kusancin su ya kai na ya damqi hannunta ya jata subar waje kamar akwai zancen sirrin da sukeyi da bayaso ita taji. Rayyan fa, Rayyan dinta da take daukar kafafuwanta, ta karya matsayinta na mahaifiyar shi mai cikakke iko da hakki a kan shi ya taso yazo har inda take ya gaisheta, taje dakin su dan kawai ta saka shi a idanuwanta. Shine yau take ganin kusancin da tayi shekaru tana neman ta samu a tare dashi yana nunawa akan Layla, akan mayyar yarinyar da taki jinin ta wayi gari ko a tunaninta tajita, balle kuma ta saka ta a cikin idanuwan ta
"Bayana kike son gani Maryama... Sakani raba Ahmadi dake bai isa ba? Kassarani kike neman yi shisa kika kawo wannan mayyar..."
Ayya take fadi muryata na rawa, cikin tashin hankali kamar wadda ta samu tabin kwakwalwa. Gabaki daya hankalinta idan yayi dubu kowanne a tashe yake
"Tafdin... Na rantse da Allah ba'a isa ba...ina tunanin wuta a makera ba zanji tashin ta a bayan gari ba"
Duk tsoronta akan Rayyan, duk tunaninta akan halayen shi ta alakantasu ne da abinda tayi kuskure ya sha, sanadin da kawancen su da Khadi bai koma kamar da ba, saboda tayi da ita su koma wajen Malam taqi, sai tama dinke mata, sam ta daina labarta matsalolinta da ita. Gwaggo ce a lokacin kafin rasuwarta, idan ta matsa sai tace mata tana karbo taimako a wajen Malamin Khadi. To dan Rayyan ne ta dinga amso karya tambaya, da yana yaro in ta danne shi tana samu ta dura mishi, daga baya ba zai sha ba, banda abinci sai ruwan leda, ko ya tarya a fanfo, ko zobo ta hada Rayyan baya sha sam.
Bata san ba abinda yasha bane yake dawainiya da shi sai yanzun, bata dauka Maryama na bibiyarta da yaranta ba har yanzun sai yau
"Minna, Neja da Bidda ma ubansu yayi kadan wallahi, balle kuma wata yar banufiya da uwar rikon ta..."
Cewar Ayya, bacin rai da tunanin barkatai na maye gurbin tsoronta, tana murna yaronta ya sami gurbin karatu a jami'ar da ake ji da ita a fadin Najeriya, kuma Abbu sai alfahari yake da fannin da zai karanta shine ake neman kassara shi
"Wallahi da sake..."
Ayya ta furta tana samu taja kafafuwanta da sukai mata mugun nauyi tana komawa daki, kanta harya fara sarawa da tashin hankalin da take tunanin ya kunno mata kai.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 14, 2020
08
Da wani yace mishi zai iya shekara daya a wani gari daban, nesa da Bilal, nesa da Layla da bai taba tunanin kewarta zata danne shi haka ba zai karyata. Dare da yawa ya sha farkawa ko shan ruwa da yakan yawan yi ko kuma wani abu daban ya tsinci kan shi da kasa komawa bacci, saboda kawai yana tunanin Layla. Yana tunanin ko tana kewar shi ko batayi, ranar da zai tafi bata neme shi ba sam, yafi mintina talatin a tsaye kofar daki yaki fitowa yana jira ko zata shigo tayi mishi sallama, amman shiru, sai da ya taka ya sameta har bangaren Mami, duk da bai shiga ba a bakin kofa ya tsaya yana kwala mata kira, ko da ta fito sai ya rasa abinda zaice mata.
Lokutta da dama yakan zabi shiru saboda kalaman shi basu da yawa, baisan yanda zai fadi abinda yakeji ba, baisan me ya kamata yace mata ba, shisa ya zabi
"Tafiya zanyi..."
Kai ta dan daga mishi
"Allah ya tsare... Zaka dinga zuwa kaman Hamma Haris?"
Dan daga mata kafadu yayi, yana rasa amsar da ta dace ya bata, abubuwa ne masu tarin yawa a ran shi, ya motsa labban shi kenan ta dago idanuwanta tana saka zuciyar shi dokawa. Ya kasa sabawa da kalar su, kamar yanda ko kan hanya yaga giccin mage sai yayi da gaske ne baya zurawa da gudu. Sanin da wahala ya kara cewa komai ya sata yin murmushi
"Allah ya saukeka lafiya. Banda fada da mutane"
Baisan murmushi ya kwace mishi ba sai da tace
"Inalillahi... Hamma...murmushi kayi ko wani abune ya fadamun a ido"
Kai kawai ya girgiza wannan karin har zuciyar shi da yake ji cike da wani irin duhu a lokutta da dama yaji murmushin
"Kin rainani ko?"
Dariya tayi mai sauti
"Ni na isa"
Numfashi ya sauke mai nauyin gaske, yana kokarin kallon cikin idanuwan ta wannan karin. Ya rasa kalaman da zaiyi amfani da su wajen misalta asalin abinda yake ji. Dakyar ya iya jan kafafuwan shi ya juya yana tafiya. Sanda ya sake waiwayowa sai yaga bata nan. Abin ya mishi wani iri sosai. Yaso ace ta tsaya, yaso ace ta jira shi harya bace mata, amman batayi hakan ba. Bayan tafiyar shi yanayin yana yawan fado mishi a rai, musamman idan yayi kewarta.
A cikin shekara dayan, kusan idan ba karatu bane yayi mishi zafi, duk watan duniya yana hanyar Kano, kawai ya kula da abu dayane a shekarar game da Ayya. Batason yawan zuwan da yakeyi, da ta ganshi zai ga tsoro a cikin idanuwan ta, har magana tayi mishi wani zuwa
"Rayyan ba zaka natsu waje daya ba ko? Taya zaka fahimci karatu kullum kana hanya?"
Cikin idanuwa ya kalleta, yaso ya fahimci dalilin canzawarta lokaci daya amman ya kasa, yawan magana na saka shi ciwon baki wasu lokuttan, kuma idan maganar tai tsayi zaiji ta fara hau mishi kai, shisa baice mata komai ba, har tayi mitar ta gama. Sai da ya mikene tukunna yace
"Zan gaisheki ne daman"
Yana juyawa
"Allah ya shiryeka..."
Shine kalamanta da yaji kafin ya fice daga dakin. Bai fasa zuwa ba, gajiyar da yayi jiya ita ta hana mishi tafiya gida, da ciwon kai na gaske ya fito daga wajen jarabawar shi ta kare shekarar farko a jami'ar. Amman a daren ya hada kayan shi yana ajiyewa, yaji dadin hakan dan yana dawowa masallaci wanka ya shiga. Lokacin da yaje babu yanda Haris baiyi dashi ba da su zauna tare a gida daya, amman yaki. Shi sun kama gidane anan Layin Kasuwa. Da Rayyan ya tashi sai ya nema a Rufasi.
Gidan nasu daki shidda ne, guda daya Abbu ya biya mishi shi kadai, sanin halin shi. Banda sallama babu wani abu da yake hada shi da wani a cikin gidan, sau dayane da akace wani Emmanuel bashi da lafiya za'aje duba shi ya bisu. Acan ya barosu saboda baisan ya zai zauna ayi hirar da suke tayi da shi ba. Sunayen su ma bai sani ba, Emmanuel din saida yaje asibitin ya gane shi. Lokacin da yaje ya sami da yawansu a gidan, suke fada mishi yanda suke tsara shara da wankin bandaki, idan wannan yayi wannan ma sai yayi.
Sai dai shi baya jira, shiga biyar idan zaiyi a rana, komin wankin da akayiwa bandakin saiya kara wankewa, ya sha jin suna gulmar shi
"Dan sarkin masu tsaftar Rufasi da kewaye"
Daya cikin su ya taba gwada tsokanar shi
"Gaye sarkin tsafta..."
Kallon "Yaushe muka fara wasan nan" Rayyan yayi mishi ya wuce yana barin shi a wajen batare daya samu damar karashe zancen ba, babu wanda ya sake gwada tsokanar shi a cikin su kaf, koya zakayi mishi fara'a fuskar shi bata canzawa, kullum fuskar shi a hade take, ga cikar gashin girar da yake da ita sai yasa ake kara ganin abinda turawa suke kira da "Frown" bayyane a fuskar tashi. Ko a aji an shaida Rayyan, yakan amsa tambaya idan yana cikin yanayin ko kuma wata rana yayiwa Malami. Amman idan ba kai ka fara mishi magana ba, ko kusa da shi ka zauna zaiyi tamkar bai ganka ba.
Na shi miskilancin daban ne, babu wanda zaice ya taba ganin shi yana yawo da wani, shi kadai yake al'amuran shi a cikin makaranta, duk kuwa yanda wasu a aji suke son kulla abota dashi, daga gaisuwa sai kaci sa'a zaka sake fito da magana daga bakin shi. Ko fita zaiyi daga gida wani lokacin a ranshi yake furta
"Allah yasa kar wanda yai mun magana yau. Bansan me yasa mutane basa gajiya da magana ba"
Shisa yau ma yana gama shirin shi tsaf, ya saka wandon jeans, takalmin sneakers ne a kafar shi, sai riga baka da ta amshi farar fatar shi, sai kamshin yakeyi saboda ya yarda da turare, kuma daya fito wanka sai da ya busa sigarin shi. Bilal kance yana warin hayakinta duk idan ya sha, shisa yanzun yafi da ta'ammali da turare, kawai ya tsinci kan shi da kara shinshina jikin shi bayan ya gama shirin, jakar shi daya shirya kaya a ciki ya dauka yana fitowa, mukulli yasa ya kulle dakin, ya saka shi a aljihu kenan kamar daga sama yaji ance
"Rayyan ba dai tafiya ba da sassafen nan, kana kewar gida ne da yawa haka?"
Juyawa yayi yaga wanne mai karfin halinne, ya tsani magana da mutane, yafi tsanar magana da mutanen da baisani ba, idan kana so ka bata mishi rai kayi mishi magana da sassafe haka
"Cikin abubuwan da aka haramta ya kamata ace akwai magana da sassafe"
Ya kan fadima kan shi, kallon gayen yayi, Saminu yaji ana kiran shi, ya rike sunan ne saboda surutun shi, surutun da yasa gayen sam bai mishi ba. Idan yana daki a kwance da daddare muryar shi tafi ta kowa tashi. Lokutta da dama yasha lumshe idanuwan shi ya hasaso ya shiga dakin su Saminu da yake kusa da nashi ya kwada mishi mari.
"Kamar ana korar ka?"
Saminu ya sake fadi yana washe ma Rayyan din hakora kamar ya san shi. Hannu Rayyan ya mika mishi sunayin sallama, yanajin wani yarr a jikin shi saboda hannun Saminun da yake da lema alamun ya taba ruwa, kilan ma baki ya kuskure ya sakada yatsu a ciki yana wankowa. Yatsina fuska Rayyan yayi cike da kyama, yana da bala'in tsantsani, shisa ko a cikin makarantar bako ina yake cin abinci ba, yafi son soyayye kuma, ko ya siyi lemo da biskit yafi mishi natsuwa, akan ya siyi abu yaci zuciyar shi taita tashi a banza da wofi.
Yanzun ma raba Saminu yayi yana ficewa daga gidan. Nufin shi ya fita harya samu acaba da zai kaishi tasha, sai ya tsinci kan shi da takawa yana cigaba da tafiya, kafin wani lokaci ya gan shi kofar gidan su Haris, bayason yaji kamar bai kyauta ba, duk da yanda kasan cuta haka yake avoiding din Haris a cikin makaranta, yana iya hango shi daga nesa ya sake hanya. Duk da Haris din yaki fushi, har aji yakan same shi idan ya kwana biyu bai ganshi ba, wata rana kuma har gidan yakan je da yar kular shi ya kai mishi abinci
"Ni na dafa, duk me zan kawo maka ni na dafa..."
Haris din ya fadi ranar farko daya kawo mishi abinci, baici ba saida ya tafi, ya kuma ji dadin wake da shinkafar da miyar kifi. Dan ya kwana biyu baici abinci ba a lokacin, to kusan saiya zamana idan yaci abinci ba soyayyen abu ba, to Haris ne ya kawo mishi, ko nashi rishon mai amfani da kalanzir dana wuta bai taba kunnawa ba. Ba ruwan zafi yake wanka dashi ba komin sanyin da akeyi kuwa, ba kuma girki ya iya ba balle ya dafa. Jiyan Haris ya same shi har aji yayi mishi fatan nasara da cewa
"Naga yau zaku gama jarabawa... Nikam sai ranar laraba in shaa Allah"
Baisan ya akayi bakin shi yayi nauyin cewa Haris zai tafi gida ba yau, daya huta yanzun. Gashi tsaye a kofar gidan yana tunanin shiga, bama shigar bace ke mishi wahala, abinda zai fada din ne tashin hankalin shi. Yana nan tsaye yayi sa'a Haris ya fito, da mamaki yake kallon Rayyan, dan bai tsammace shi ba, bayan sun gaisa ne yake fadin
"Sai kayi tsaye a bakin kofa? Da ban fito ba fa? Ka shigo"
Kai Rayyan ya girgiza
"Zan tafi gida ne, shine na biyo"
Murmushi Haris yayi, yaji dadin biyowar kuwa. Dan mutane kanyi mamaki idan yace musu Rayyan din kanin shine, duk da akwai yanayi na kamanni da zai nuna cewa akwai alaka ta jini a tsakanin su, amman halayyarsu tayi hannun riga
"Ka kyauta daka biyo, nagode da zumunci. Allah ya tsare hanya. Nima in shaa Allah ranar laraba dana fito daga exam zan taho gida"
Kai kawai Rayyan din ya daga mishi yana juyawa. Jakar shi ya sakewa kafada saboda ta daman ta gaji, anan ya rataya tun fitowar shi. Daga gidan su Haris din kai tsaye titi ya fita yana samun mashin zuwa tasha. Kamar ya runtsa idanuwan shi ya bude su ya ganshi a gida haka yake ji, idan ba kwakwalwar shi ce take mishi karya ba, kamar zumudin zuwa gida yaji yanayi.
*
Sam tunda Rayyan ya dawo hankalin ta yaki kwanciya. Baccin kirki ma bata samu tayi, gashi hutun yayi mata tsayi, daya tafi makaranta sai taji hankalinta ya kwanta sosai. Ko babu wani abu Rayyan din yayi nisa da gidan, yayi nisa da Mami da Layla. Bikin Zubaida ma da za'ayi nan da wata biyu bai tsaya mata a rai kamar yanda take so taga Rayyan ya koma makaranta ba. Gashi yanzun yafi da yin nesa da ita, jiya badon Rukayya ba sai girkin da ta dora ya babbake, yanata qauri, sam a hanci ma bataji ba, tazo jikin window din dakin ta daga ciki ta labe tana leke.
Ba karya kunnuwanta sukayi mata ba, tabbas taji muryar Rayyan din yana kiran Layla. Shisa ta labe ko zata ga fitowar ta, taga alama idan ba jan ido ta nuna akayi karamin tashin hankalin da aka kwana biyu ba'ayi irin shi a gidan ba, to Layla ba zata kyale mata yaro ba
"Shegiya mayya mai zubin yan ruwa. Yarinya baki tafasa ba kina kauri. Wai yar yarinyar nan harta san ta kashewa maza murya. Kai ni Maimuna naga ikon Allah"
Ta furta ita kadai, dan sambatu shine abokinta tun da Rayyan din ya dawo, kusan kullum zaka ganta manne jikin window, tun yaran na magana har sun kyaleta. Huda takan aika idan bata makaranta tace taje ta dubo mata idan Rayyan yana nan, ko ta saka mata ido idan ta gansu da Layla tazo ta gaya mata, abinka da kuruciya randa ta gansu kuwa tun a gaban shi tace
"Ayya tace dana ganka da Adda Layla inje in fada mata"
Da gudunta kuwa ta karasa har dakin Ayya din, inda ko mintina biyu bata hada da shiga ba Rayyan din ya rufa mata baya, tana cikin rattafowa Ayya zance, sai da ya kamo hannunta ya juyo da ita sannan ya wanketa da maruka har biyu
"Karyaki zanyi idan kika sake dibo gulmata kika kawo, kina jina, karyaki zanyi wallahi"
Yake fadi yana girgiza Huda da take wani irin gigitaccen kuka da ba ita kadai ta rude ba, har Ayya da ta fisgeta, babu wanda Rayyan bai daka ba a gidan, daga Khalifa da sam baya shiga sabgar shi sai kuwa tace Huda, ita kadai ma take ganin yana dan yiwa fara'a wasu lokuttan. Amman ranar saboda ta kawo zancen Layla shisa yake shirin kurmantata
"Ni zaka daka Rayyan, ba ita zaka daka ba. Ka dakeni saika nuna mun ka girma kafi karfina. Tunda ni na sakata..."
Ayya take fadi tanajin zuciyarta na wani irin zafi
"Ayya..."
Rayyan ya kira ranshi a bala'in bace, saboda gani yake shi akayiwa laifi, sam bayason gulma, yaga alama kuma Ayya da kanta take so ta koyawa Huda
"Dan ubanka nace ni zaka daka, akan waccen shegiyar yarinyar ne kake neman nakasa kanwarka, kake kuma tsareni da ido"
Kai yasa yana ficewa daga dakin yabarta. Ranar yanda taga dare haka taga rana, washegari sai da tayi wa Bilal zancen
"Wai meye tsakanin Layla da Rayyan? Yarinyar nan duk sai ta lashe muku kurwa ko?"
Da yake kansu a hade yake, dariyar shi ya dinga mata, cikin salo ya canza maganar. Sai ta hakura ta kyale shi, to yanzun Huda da take sakawa ta gano mata me yake faruwa tsoron Rayyan takeyi, ko ta aiketa idanuwanta zasu tara hawaye
"Hamma zai karyani Ayya... Allah zai dakeni"
Dole ta kyaleta, sauran yaran ma babu wanda zaije tasani, idan ma sunje din dawowa zasuyi suce mata basu ga komai ba. Mami ta jima tana sakata kwanan zaune, yanzun kuma ta kawo mata alaqaqai tana sakata tuna satin amarcin Mami din da kalar bakin cikin data hadiya.
"Wallahi Maryama ke ba alkhairi bace a rayuwata"
Ta fadi rannnan da takaici ya qumeta, harda kwallarta. Yanzun kam lissafinta yazo karshe, tunda dai gobe Rayyan din zai tarkata ya koma makaranta, itama ko na kwana talatin ne kafin fitina ta dawo dashi zata samu ta maida hankalinta kan maganar bikin Zubaida. Idan san samune ma Rayyan din yai zaman shi har sai lokacin bikin tukunna. Addu'ar da takeyi baji bagani