Showing 24001 words to 27000 words out of 85263 words
Chapter 9 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt
magani?"
"a-"
waje tayo da ido tunowa da bata son magani da sauri tace "eh na sha momi ta bani magani mai shegen ɗaci"
wani ya mutse fuska tayi kamar da gaske
Qasin yace "tho ci abincin sai kije ki kwanta"
kuka tasa masa
"ni bazan iya ciba Allah ciyo yake sosai"
"owk jeki ki kwanta"
tashi tayi da sauri tana yiwa Siraj ɗageɗage,
har ta kama hanya sai kuma ta dawo ta nunashi da yatsa ta maida baki gefe tace "kai kuma yaro kayi sauri ka cinyeshi duka"
juyawa tayi ta cigaba da tafiyarta tana wani rausaya kamar wata tsohuwar karuwa,
Siraj kai ya girgiza yana dariya,
murmushi Qasin yayi ya bita da kallon har shige.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*24*
*_washe gari..._*
9 da yan mintuna mairo ta nufo downstairs sanye da kayan bachi fuskarta babu annuri,
duk ɗagowa sukayi suna kallonta harta zauna momi nakai wainar kwai tace "maryam lafiyarki kuwa?"
kara ɓata fuska tayi "momi cikina ne yake ciyo sosai tun jiya"
Siraj ne ya gwaleta "dan Allah can ji kanta"
"kai yaro wlh ka kyaleni"
dariya yayi "Allah momi in bata daina cemun yaro ba dukan gwarai zanyi mata"
momi na mika mata cup ɗin tea tace "karma ka soma ka daketa bakai ka fara wasa da itaba"
gwalo mairo tayi mishi "ance yaro yaro yaro yaro yaro yaroooooo"
Usman yace "ba cikinki ke ciyo ba kenan?"
nan ta rike cikin ta langwashe "momi ni ko tea nan bazan iya shaba ciyo yake sosai"
momi tace "wani abun kika cine?"
"a a ni banci komai ba"
Qasin na kurɓa tea yace "bakince kinsha magani ba ko karya kike?"
soshe2 ta shigayi yana son kawarda maganar "uhm momi kinsan kince yaya bazai kara ci miki abinci ba ko jiya yaci kuma yau yana ci"
kallonshi momi tayi "tho yana iya da abunda yafi k'arfin wuta inji kishiyar k'onanna"
dariya yayi yace "Allah momi abinci inba naki ba bana jindaɗinshi"
momi zatayi magana Siraj yace "nidai duk ba wannan ba dan Allah momi karki barta taje ki hanata"
mairo da Qasin suka kalli momi mairo ce ta riga tambaya "minene momi wa za a hana?"
da fork Siraj ya nuna ta "ke mana ke za a hana"
"ina zataje?"
Qasin ya tambaya,
momi badan taso ba ta soma masa bayani "jiya ne bayan fitarka Yarima yazo wai yana son maryam ta rakashi wani taro da za ayi na buɗe wata kungiya ta taimakon yara"
ɓata fuska Qasin yayi ya taɓe baki "tho saboda mie sai ita zata rakashi miye haɗin ta ta kungiyar?"
Siraj ne ya karɓa mishi "wai shine zai kaddamar da abun kuma yana son yaje da yarinya da zatayi jawabi a maimakonsa jifa"
momi tace "tsarin ne yazo da haka dan haka aka tsara komai har ma abunda maryam zata faɗa a rubuce yake"
tsaki Qasin yaja "aikin banza maryam ce kawai yarinya ai yana da kanne mata da maza yaje dasu mana babu inda zata je"
momi tace "yafa riga ya bada abunda zata karanta har kayan da zata saka ya kawo"
tashi Qasin yayi tsaya yana faɗin "tho a mayar masa da kayansa momi dan Allah karki barta taje"
momi bata ce mishi komai ba sai maryam take kallo data ɓata fuska kamar ta fasa kuka,
tana ganin ya fice tace "momi nidai zanje inason nayi jawabi"
Usman da Nura dai kallonta kawai suke basu ce komai ba
kai momi ta ɗaga mata "ai zaki je inma kike kare zan baki takarɗar kiyita bita kamin assabar kin iya"
daɗi sosai mairo taji za a rika Microphone ayi jawabi.
baki sake Siraj yace "momi kina nufin barinta zakiyi taje duk magangganun nan da akayi"
shima banza momi tayi dashi mairo nata watsa masa harara harya kare cin abincin ya fice.
'''***'''
koda 12 tayi mairo na zaune ɗaki tana karanta takardar da taji motsi ta ɓoye dan kar Siraj ko Qasin ya shigo ya gani,
haik'an ta ɗauki abun ta rika tarewa a ɗaki duk abunda da bata gane ba ta tambayi momi,
islamiya ce kawai take tasa ta aje idan ta dawo ta cigaba,
a waya Yarima yake kiran momi tabawa mairo yana jin yadda take karantawa dan yasan zuwa gidan ba zai masa daɗiba kuma daman momi tayi dashi akan komai zasuyi ayi a waya karya zo gidan inba weekend ba ranar da zasu tafi,
kullum Qasin da Siraj cikin nanatawa momi suke akan karta barta taje. a fili momi nuna musu take bazata barta ba dan karsu dameta,
mairo har zumuɗi take taga assabar ɗin tayi duk wani ciyo da take ji daina faɗawa momi tayi dan karta hana ta zuwa,
cikin kwana biu mairo ta haddace abunda yake fefar kasancewar ba wani jawabi ne mai yawa ba,
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*25*
*_Saturday morning..._*
_8:24am_ Qasin ya shigo part ɗin momi cikin kananan kaya,
parlour ya tararda su suna karyawa.
momi na ganinshi gabanta ya faɗi a haka ta ɗaure ta amsa gaisuwar da yayi mata "lafiya kalau ya naganka cikin shiri haka?"
yan duba agogon hannunsa yace "wlh meeting ne wai zamuyi da wasu kuma basu faɗa min ba sai jiya da maraice gashi anjima zasu wuce balle nayi cancle ɗinshi"
wani daɗine ya jiyarci zuciyar mairo da momi mairo kasa jurewa tayi saida tayi dariya,
cup ɗin tea momi ta aje mishi "xauna ka karya mana"
ɗaukar tea yayi a tsaye yana sha "bani da time ɗin tsayawa ina Siraj ne?"
"yaje birnin kebbi"
fuskar mamaki yayi birnin kabbi gurin mie?"
"nima ban saniba baba hajara ce ta aiko tana nemansa tun da 7 ya tafi"
iskar bakinsa ya busar "owk maryam tashi ki chanja kaya ki rakani"
da sauri momi ta kalleshi "gurin meeting ɗin zata rakaka?"
"eh momi ban yarda da barinta cikin gidan nan ba"
faɗa momi ta taso masa dashi "tho bazata ba in baka yarda da magana naba sai kayi abunda zakayi nifa na haifeka Qasin ba ni ka haifa ba"
kasa yayi da kansa yana sauke ajiyar zuciya,
duk sai yaji ba daɗi ganin yadda ranta ya bace haka ya juya jiki ba kwari ya fice.
*_9:41am..._*
motar Yarima tayi parking,
ya kusan minti uku ciki motar sannan ya fito ya nufi parlour.
da sallama ya shigo mairo ta amsa masa tana murmushi,
tsaye yayi yana kare mata kallo ganin yadda tayi masa mugun kyau doguwar rigace jikinta golden colour sai ɗan karamin bakin hijab da momi ta saka mata da da jan janbaki sosai tayi kyau,
a hankali ya karaso kusa da ita ya risina ya kai hannu ya taɓa gefen fuskarta yana haɗiye yawu,
murmushi ta sakar masa "ina kwana"
bai amsa mata ba
ya mayar mata da murmushin yana mata wani kallo,
jin an taɓa kofa ya sashi tashi ta sauri ya matsa baya yana kallon momi data nufo downstairs.
"Yarima ka iso?"
"eh momi naga har kin shiryata"
"eh kasan kace mun 9:30 zaka zo"
agogon hannunsa ya kalla "bari muje momi kar muyi african time"
"owk tho Allah ya kiyaye"
hannunta ya rika suka fice tana yiwa momi byebye.
murmushi momi ta bita dashi har ta fice ko kaɗan momi bata son tafiyarta dan dai babu yadda zatayine tunda tana ganin inta hana mairo zuwa bata kyautawa Yarima ba,
'''*************'''
Qasin ne tsaye tsakiyar ɗaki yana kai da kawo kana ganin yanayin fuskarsa kasan ransa a bache yake.
momi ma zaune take saman kujera dafe da kai lokaci lokaci takan kai dubanta gurin agogon dake parlour.
wannan karon *9:21pm* ya nuna hankalinta ne ya kara tashi,
da sauri ta janyo wayar dake hannunta tana kiran number Yarima duk sakamoko ɗaya ake bata kamar ɗazun wayar a kashe,
juyowa Qasin yayi ya kalleta "kinga ni ko momi saida nace miki karki barta taje kika ki yarda da magana na gashi yanxu abunda ake yiwa gudu"
numfashinsa momi ta tara "babu abunda zai samesu insha Allah kawai dai bana son sukai 10 ne"
magana take kamar abun bai dameta ba saɓanin cikin ranta dake cike da tashin hankali,
kai Qasin ya girgiza "hmm ace tun safe mutun ya fita har yanzu babu labarinsa"
da karfi Mairo ta turo kofar parlour ta shigo idonta zurun zurun.
duk juyowa sukayi suna kallonta babu wadda ya iya taɓuka komai harta karaso kusa dasu,
lumshe ido Qasin yayi yana sauke ajiyar zuciya.
da fata momi tayi tana kallon bayanta "ina Yarima?"
"yana can basan inda yake ba sawa yayi a kawoni"
magana take muryarta na rawa kana gani kasan tsoro take ji sai waiga bayanta take,
juyowa Qasin yayi da ita "maryam mi yasa kuka daɗe?"
shiru tayi tana haɗiyar yawu "ba ba babu komai"
tsawa Qasin ya katsa mata yana girgiza ta "faɗamin min gaskiya tun safe ku fita sai yanzu ki dawo kice mun babu komai faɗa min miya faru?"
matsawa tayi ta rike momi tana kuka "yace duk na faɗa sai ya kasheni"
sanyi jikin Qasin yayi momi kuma tsigar jikinta ta tashi,
a hankali momi ta rika zata zaunarda ita kin zama mairo tayi ta ɗan ɗaga rigarta cike da tsoro tace "momi kayana duk ya ɓata dubi jini na min zuba"
da sauri Qasin da Momi suka kalli jinin dake bin k'afarta.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*26*
waje Qasin yayi da ido cikin rawar murya yace "maryam..-"
da sauri ta kalleshi itama idon nata a tsaye.
zai rikata momi tayi saurin rika hannunta "muje ciki"
janta momi tayi suka nufi stairs jikinta babu karfin,
Qasin ma haka yake kallonsu jiki ba kwari har suka shige sannan ya faɗin zaune yana kallon gurin da jinin ya zuba,
sai kusan 10 da wani abu ya tashi ya nufi part ɗinshi tafiya yake kafafunsa na masa nauyi zuciyarsa sai bugawa take da karfi,
baiyi sallama ba ya shigo parlour.
har ya zauna bai lura da mansura dake zaune saman kujera ba
dafe kanshi yayi ya kulle idonsa gam yana cizon baki,
jin an dafashi yasashi ɗago kai ya kalleta.
tashi hankalinta yayi yanayin yadda taga idonsa yayi ja tasan ba lafiya ba,
tana shafa gefen fuskarsa tace "Qasin lafiya na ganka haka?"
janye mata hannun yayi "babu komai jeki kwanta"
"kamar ya naje na kwanta bayan kai hankalinka ba-"
cikin tsawa ya tari numfashinta "nace miki kije ki kwanta babu komai"
tashi tayi tana masa wani kallo kamin ta juya ta nufi ɗaki,
dafe kai yayi ya sake rumtse idon abunda ya faru ɗazu ne ya rika dawo masa,
jin yayi bashi da natsuwa yaji wani irin abu ya tsaya masa a zuciya da sauri ya tashi ya nufi firij yana buɗewa ya ɗauki gorar ruwa ya kafa a baki,
kaɗan yasha ya ɗire ta saman firij ɗin yana maida numfashin,
ya daɗe tsaye a gurin sannan ya juya ya nufi kofa.
part ɗin momi ya sake nufowa yadda yabar parlour haka ya tarardashi kai tsaye upstairs ya nufa,
tun kamin ya karasa hawa yayi tsaye jin shinshikar kukan momi wani abu yaji ya tsikareshi tun daga ɗan yatsan kafarsa har tsakiyar kansa karfen stairs ɗin ya rike da karfi ya matse hannunsa ciki yana dantsar hakora,
jin bazai iya jure tsayinba yasashi zaunawa a gurin,
lumashe ido yayi saida yaji abunda ke zuciyarsa ya ɗan kwanta sannan ya tashi ya nufi ɗakin momi,
a hankali yakai hannu ya tura kofar ɗakin.
tsaye yayi yana kallon mairo dake saman gado kwance tana bachi kamar gawa.
ɓachin ransa dake ransa ya karu saurin ɗauke idonsa yayi ya mayar gurin momi dake zaune kusa da ita hana sharar kwallah,
cikin dakisasshiyar murya yace "momi kuka kikeyi?"
ba tare data kalleshi ba ta girgiza masa kai alamar a'a,
kai ya ɗaga "itama naji kukanta ɗazu"
sai a lokacin momi tayi gyaran murya tace "eh ina tambayar tane ko yayi mata wanin abun ne shine nace zan daketa inbata faɗa ba shine take yiwa kuka"
saida ya ɗanyi jimmm sannan yace "mi tace momi?"
ita shirun ta ɗanyi kamin ta bashi amsa "ina jin menstruation ne Qasin dan banga wata alama data nuna yayi mata wani abun ba kuma ita bata faɗa ba"
sai a lokacin ta kalleshi
murmushi yayi "yes momi menstruation ne saida safe"
bai tsaya jiran mi zata ce ba yayi baya baya yaja mata kofa daman can bai karasa shiga cikin ɗakin ba,
cikin wani yanayi ya nufo downstairs yana tafe hawaye na masa zuba har sauko.
saman kujera ya zauna saida yaji hawayen sun tsaya masa sannan ya tashi a kasale ya nufi part ɗinshi,
*_washe gari..._*
Mairo na zaune saman gado tana wasa da kafafunta Qasin ya turo kofa ya shigo fuskarsa ɗauke da murmushi,
tana ɗago kai suka haɗa ido murmushin da ta gani a fuskarsa ya hanata jin tsoronsa tun kamin ya karaso tace "yaya ina kwana?"
saida ya risina kisa da ita sannan ya amsa mata murya kasakasa "lafiya kalau kin tashi lafiya?"
"lafiya kalau"
"ina momi?"
"tana kicin"
hannayenta ya riko "faɗa min maryam mi Yarima yayi miki?"
"ni bai min komai ba yaya"
shiru yayi ya soke kai
can ya ɗago kai ya kalleta "jinin dake miki zuba har yanzu yanayi ko ya daina?"
"a'a ya daina koda na tashi da safe bai min zuba ba"
da sauri ya lumshe ido bugun zuciyarsa ya karu.
"ba abunda kake zargi bane Qasin jikina bai bani haka ba kuma na bincike ta banga haka ba"
momi ce take maganar lokacin da ta karaso kusa dashi.
sakin hannunayen nata yayi suka tashi tsaye tare shida Mairo,
wani irin faɗuwa gabansa yayi lokacin da ya juyo suka haɗa ido da mansura dake tsaye bakin kofa rike da kofar ɗakin.
cikin rashin ta karasa shigowa tana faɗin "miya faru da maryam?"
da sauri momi ta tari numfashinta "babu abunda ya faru da ita gimuwa ne tayi da kuma ciyon kai"
karasowa tayi kusa da mairo "gimuwa a ina?"
nan mairo ta soma mata bayana "a a jiya ne da-"
tassssss Qasin ya wanke mata fuska da mari saida ta faɗi tun bata kai ko ina a zancen ba,
da sauri mansura ta kalleshi "Qasin mi-"
marin itama ya watsa mata saida tayi baya ta dafe kunci.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
_dedicated this page to maama Hajiya Zainab Kano kakar yan biu 🙈 LOL_
*27*
da sauri momi ta riko Qasin da fuskarsa ke ɗauke da bachin rai tace "mi yake damunka Qasin mi suka maka?"
kallon kawai ya rikayi ba tare daya amsa mata ba,
sun minti 10 haka ɗakin tsit sai shehsekar kukan Mairo ke tashi.
mansura ce tayi karfin halin sake yin magana "momi mi yake damunsa ne tun jiya na kasa gane kansa?"
nan momi ta saki Qasin ta matsa kisa da mansura "abunda ya kawo ki kenan? daman nasan baki taɓa leko part ɗina ba sai a wata bukatar kanki ta taso"
kasa tayi da kanta har alokacin tana dafe da kuncinta hawaye na mata zuba,
"indai har abunda ya kawo ki kenan tho ki juya ki barmin ɗakinki ai mijinki ne kinfini sanin hanyoyin da zakibi ki fahimcin abunda yake damunsa"
kamar *HAWAINIYA* ta soma tafiya kanta a kasa har ta fice,
juyawa momi tayi ta nufi mairo ta tashe'ta tana share mata hawaye cikin sanyayyeyar murya momi ta soma magana da Qasin ba tare data kalleshi ba "bana son kowa yasan da maganar nan Qasin koda Siraj ne"
nan ma baice komai ba ya kaɗa kai ya fice,
mairo sai taga ya fice sannan ta kalli momi cikin muryar kuka tace "momi minayi masa?"
"baki masa komai ba maryam"
"amman momi ya mareni haka da zafi"
murmushi momi tayi "baya son idan manya na magana yara su saka baki"
shiru mairo tayi tana shafa gurin,
momi ta kwanto ta ita jikinta "maryam"
cikiciki ta amsa "na'am"
"duk wadda ya tambayeki mi akayi miki kice komai karki kuskura kice Yarima yace in kika faɗa sai ya kasheki ko kice ranar jini yayi miki zuba kinji?"
"tho momi"
"koda fa can ne kauye karki faɗawa kowa kinji?"
"tho bazan faɗa ba"
"yauwa Maryam ɗina yar albarka tashi muje muyi breakfast"
"tho"
da sauri ta tashi momi ta rika hannunta suka fice,
parlour suka tararda Qasin zaune saman tree-setter rike da cup din tea.
da kallo ya bisu yana kurɓa tea a hankali har suka zauna sannan ya tashi ya nufi kofa,
"yaya yau ba dakai za ah karya ba?"
Siraj ne yake masa maganar yana kokarin saka T-shirt ɗin dake hannunsa ya nufi dining.
kai kawai ya ɗaga masa ya fice,
haɗe gira yayi ya kalli momi "lafiyarsa kuwa?"
momi tace "lafiyarsa kalau saidai ko in wani gurin aka taɓoshi"
kafaɗunsa ya ɗaga alamar bai damu ba yaja kujera ya zauna yana tsokanar mairo,
"miya kunbura miki fuska haka yar kauye?"
turo baki tayi ta kalli momi "momi kingan shi ko?"
kai momi ta girgiza "oh Siraj dan Allah ka rabu da ita bana son fitinar nan dan Allah"
murmushi yayi ya noce kansa ya soma cin abincin.
lokaci lokacin ya kan ɗago dasun haɗa iɗo da mairo yayi mata gwalo ita kuma ta murguɗa masa baki,
daga ita har momi ba suyi wani cin abincin kirkiba suka tashi daman ita Siraj ya tsangwameta
*_2:55pm..._*
Qasin ya shigo part ɗin momi saida ya karewa kujerun parlour kallo sannan ya kalli momi dake tsaye dining yace "Yarima yazo?"
kallon mamaki momi tayi masa "Yarima? mi zaya maka?"
jijiyar kansa ce ta tashi jin yayi kamar ya ɓalɓalowa momi masifa amman ba dama dan mahaifiya ce. dole tasa ya tausasa harshensa "magana nake son miyi dashi momi na ɗauka ta shigo ne"
"tho bai zoba kuma in har akan maryam ne karka kuskura masa magana kaji na faɗa maka"
kallon rashin fahimta yayi mata "momi karfa ayi masa magana kikace"
kallonshi tayi ido cikin ido "eh nima mahaifiyarta ce ina tunanin ko ni kaɗai nayi magana dashi ya isa"
wani murmushin ban haushi Qasin yayi ya juya ya fice,
Gardem ya nufa yana tafe yana tunanin hali irin na momi,
wakewaken Mairo ne suka ɗago da hankalinsa yakai gareta
tana zaune karkarshin bushiyar mangoro rike da gwallon gwaiba tana ci,
sai a lokacin ya soma jin tausayinta nn d nn idansa suka cika da kwallah wata irin tsanar Yarima yaji ta taso masa a ɗayan ɓangaren kuma yana son ganin laifin momi,
ya daɗe yana kallonta zuciyarsa sai wani tunani take kawo masa saida ya fisgi kansa sannan ya samu karasa kusa da ita,
da sauri ta tashi tsaye ta jefarda gwaibar tana masa kallon tsoro.
risinowa yayi ya ɗan sakar mata murmushi "maryam..."
da sauri ta amsa "na'am yaya"
hannu yakai ya shafa gefen fuskarta kamin ya jata jikinshi ya rumgume,
_'ya lalata miki rayuwa Maryam ya cutar dani yayi miki taɓon ds zakiyi bakinciki nan gaba amman zan nuna masa kuskurensa sai yayi nadamar abunda ya aikata'_
a zuciyarsa yake wannan maganar yana cige da lips.
kalamanta ne suka dawo dashi daga tunanin da yake,
"wlh yaya kaci arziki yanzu na daina fitsara na shiryu da baka isa ka mareni na kyale kaba"
hannu yasa ya ciro handkerchief ya share hawaye da suka zubo masa ya ɗago yana murmushi yace "da gaske?"
"Allah wlh kai hmm"
gefen fuskarta ya lakata "ashe ke matsifaffiya'ce ko?"
dariya tayi ta rufe ido "a'a ni mai lafiya ce"
dariyar yayi shima "mai lafiya ai sunan wani ne"
wannan karon rumfumeshi tayi tana dariyar
"yaya zaka bimu kauye?"
"yaushe zaku je?"
"da anyi hutu ranar juma ah za ayi