Showing 69001 words to 72000 words out of 85263 words

Chapter 24 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt

04 Apr 2026

896

ba rabar aiki bace bai hana Qasin fita tun da safe ba,
     Momi ma sha biu na bugawa tasa Mairo tayi wanka saida ta fito sannan itama ta shiga. Koda ta fito Mairo ta ɗanɗasa kwaliyarta ta shirya cikin koriyar atamfa ta cika janbaki a bakinta yayi mata yawur.
   Murmushin jindaɗi Momi tayi daman haka take son ganinta kullum, Hijab Momi ta ɗauko tasa tana faɗin “Karkije ko ina saina dawo kinji na faɗa miki ko?"
  “Eh naji amman karki dade Momi"
  “Bazan daɗe ba danayi gaisuwar zan dawo"
  “Toh Allah ya tsare"
“Amin"
     Har bakin k'ofa Mairo ta rako ta saida ta shiga mota sannan ta dawo parlor.
   Batayi minti 8 da fita ba taji tsayawar mota da sauri ta lek'a ta windo, Qasin ta tsinkaya ya fita daga motarshi ya nufi part ɗin shi.
    Da gudu ta fito ta nufi part ɗin ita. Zauna ta tararda shi yana shan ruwa gora.
  “Yaya sannu da zuwa"
  Saida ya kare mata kallo sannan ya amsa.
  “Yauwa sannu zo nan" Ya mik'a mata hannu.
Ba musu ta mik'a mishi nata hannun ya rik'a ta ya zaunar kusa dashi “Wa yayi miki wannan kwaliyarta?"
  Murmushi tayi “Ni nayi nayi kyau ko?"
   “Sosai ma kamar ba keba"
   Dariyar jindaɗi tayi.
Bakinta ya sakarma ido daga bisani yakai nashi bakin cikin nata.
  Sai da ya tsotse janbakin tas sannan ya yanje bakinshi yana lumshe ido. Tofarda yawu tayi tasa hannu tana goge baki,
“Wai kai Yaya nace ka daina min haka bana so k'azanta nake ji amman kullum sai kayi gashi nan duk ka goge min janbaki"
   Kamar ta rusa kuka tayi maganar tana buga k'afarta a kasa.
    Murmushi yayi “Toh yi hak'uri bari na ɗauko miki janbakin matata ki shafa kina so?"
    “Eh amman babu ruwana in tayi maka faɗa"
   “Ai bata nan ta tafi kasuwa ta siyo abun bak'i zatayi"
   “Toh ɗauko min"
  Tashi yayi rike da gorar ruwan ya nufi ɗakinshi kayan dake jikinshi ya rage ya koma daga shi sai rigar shan iska sannan ya fito ya nufi ɗakin Mansura.

   Kale-kalenta ya kai idonta kan cake ɗin dake gefen kujera.
Ta sauri ta tashi ta nufi gurin daman tun dazu take jin k'anshi.
   D'aya ta fara ɗandanawa da taji yayi mata daɗi sai ta hau cin abinci tana lasar hannu,
  Qasin na fitowa ya hango aikin da take daga can ya katsa mata tsawa “Ke waya kaiki bak'ifa zatayi ta siyo musu cake ɗin shine kika zauna kika ci? Aiko mai rabaki da ita yau sai Allah"
   Ragowar dake hannunta ta aje “Toh ni bana ɗauka naka nabe"
  “Nawa zan aje nan ban bakai miki naki ba bak'i fa tayi ta siyo musu kuma yanzu kar ta iskomu da munje mun tsiy..."
jin tsahawar motarta  yasa yayi shiru.
Da sauri Mairo ta tashi tsaye “Itace ko?"
  “Itace kuma ni babu ruwana ke da ita can"
  Tana tashi ta niyar guduwa Mansura ta turo k'ofar parlor ta shigo.
   Da sauri Qasin ya k'arasa saukowa ya tareta “Kin dawo?"
   Bata amsa mishi ba ta watsama Mairo harara “Mi kikazo nan?"
Duk bata ga aika-aikan da tayi mata ba sai da ta kusa kaiwa kusa da ita.
  “Kan Uba uban wa ya aikeki taɓa min cake?"
   Gabanta Qasin yaci ya rik'ota “Yi hak'uri Mansura bata san naki bane bari na siyo miki wani yanzu"
    Janbakin dake hannun shi ta kalla “Waya ɗauko min jan baki mi zakayi dashi?"
    Matsowa Mairo tayi kusa da ita ta turo bakinta tana nuna mata.
   “Shine ya tsotse min janbakina shine yace bari ya ɗauko min naki na shafa amman na fasa shafawan gida zani"
    Baki Qasin ya saki ya juyo ya kalli Mairo,
“Ke miyasa karya bata miki wahala ne?"
   Sake juyowa yayi ya kalli Mansura “K'arya fa take"
  Uffan ba tace mishi ba ta mika mishi hannu “Bani cake ɗin"
    Yana duk'awa ya ɗauko mata nan ta cire takalmin ta mai tsini ta saita kan Mairo ta k'wala mata shi.
    Wata mahaukaciyar k'ara Mairo ta saki. Jini ya malalo mata daga saman kai,
   K'arasa jefa mat takalmin Mansura tayi tana faɗin “Gobe in kikaga na sake ganin na aje abu ki ɗauka ciki wai har kike faɗamin janbakinki ya tsotse ke tsohuwar karuwa ko?"
    Da gudu Mairo ta bar parlor dafe da kai.
    Jefeta Qasin yayi ya cake ɗin ya wanke mata fuska da mari hudu masu kyau. Da sauri ta dafe kunci tayi baya-baya tana kallonshi “Qasin saboda na fasa mata kai ka mareni"
   K'ara mata na biyar yayi “In bakida hankali sai kiyi shi saboda taci miki cake ɗin banza zaki daketa ki safa mata kai haka aina fada miki duk kika sake sa mata hannu sai na samiki"
    “Lallai Qasin kai butulu ne yaushe aka ɗaura maka Auren da ita da har kake fifitata a kaina? Koda yake halinku ne maza haka kuka gada"
      Cikin kuka take mishi maganar.
  “Ke in banda rashin hankali mi zakiji a jikin Maryam in kika daketa?"
    “Abinda kasan a naji shi zanji mai abin kunya yasa k'aramar yarinya a gaba yana kiss"
    “Toh haramun nayi har abinda yafi kiss sai nayi mata tunda matata ce"
    “Bazan iya zama da kai ba Qasin sun riga sun shiga tsakanin mu yaushe kayi Auren nan amman gashi har ka fara canja min bazan iya zama da kai ba har sai ka zaɓa koni ko ita"
    Tsaki yaja ya fice ya bar mata parlor.

_A ɓangaren Mairo_
Da gudu Mairo ta shigo parlor tana kiran sunan Momi.
   “Lafiya Maryam?"
Jin muryar Yarima yasa ta juyo da fukar jini ta kalleshi. Baya-baya tayi tana cigaba da kukan.
  Da sauri ya rik'ota “Ke Maryam ba wani abin zanyi miki ba miya sameki haka?"
  Cikin kuka ta bashi amsa “Matar Yaya Qasin ce ta fasa min kai"
    Baiyi wata-wata ba yasa hannu ya ɗauketa yana faɗin “Muje na kaiki asibiti"
  Tirjiya ta shiga mishi tana k'ok'arin k'wace kanta.
   Sauketa yayi “Trust me Maryam bazan miki komai ba asibiti zan kaiki"
    Ganin bata da mafita yasa ta kyale shi kodan zogin da take ji yaja hannunta suka fice.

        Koda Qasin ya shigo bai tararda ita ba duk saida ya bikaca gidan amman babu ta babu labarinta,
    Fitowa yayi ya nufi gurin mai gadinsu yana tambaya shi ko yaga Mairo.
    “Eh ranka ya daɗe naganta a motar Yarima sun fita"
   “What!?" Da k'arfi Qasin ya tambaya
  “Yaushe Yarima ya shigo?"
   “Bai daɗe da shigowa ba sai kuma naga ya fito tare da ita da gudu ma ya fita"
  Kai Qasin ya ɗaga mishi ya nufi part ɗin shi.
     D'akinshi ya nufa yana jin kukan Mansura. bai ta kanta ba ya ɗauko keys ɗin matar shi ya fito.
   Yana kawowa parking space ya tararda Momi ta fito daga mota.
   Yanayin yadda ta ganshi yasa ta tambaya “Lafiya dai?"
  Shiru yayi yana kallonta ya kasa bata amsa, “Qasin da kai nake magana lafiya na ganka haka?"
   Kanshi ya sosa “Momi Maryam ce tayi faɗa da Mansura shine ita kuma ta fasa mata kai kuma nazo yanzu ban ganta ba ance Yarima ya fita da ita shine zan bi bayan shi"
   Momi ta zaro ido “Wa aka fasama kai?"
   “Maryam"
Wani irin Momi tayi kamar ta fasa kuka “Ta mutu ne?"
  “A'a Momi kaɗan fa ne ma aka fasa mata kan"
   Motar Momi ta rufe ta nufi cikin gida idonta da k'wallah.
    Rufa mata baya yayi tana kwantar mata da hankali,
   Saman kujera Momi ta zauna dafe da kai.
  Nan shima ya zauna “Dan Allah Momi ki kwantar da hankalinki bafa wani mugun ciyo bane taji kawai.."
  Hannu ta ɗaga mishi “ɗan Allah ka rufe min baki ka naji da wane da raunin da kukayi mata ko da surutunka"
   Shiru yayi yana shafa kanshi. duk abin duniya ya ishe shi ya rasa da wanne zaiji ɗayan ɓangaren zuciyashi yana gurin Yarima da tafi mishi da Mairo.
nan kuma yasan Momi ba saurara mishi zatayi ba.
   
   ***
    Pharmacy mafi kusa ya nufa da ita k'in yarda tayi a dubata saida Yarima ya rumgume ta.
   Da kuka  akayi treatment ɗinta sannan ya suka bata wasu maganin nika ya sata mota suka ɗauko hanyar gida.
   bataana isa yayi horn kamin a buɗe mishi ya mik'a hannu ya riko hannunta yana sauke ajiyar zuciya
   “Ina sonki Maryam ina sonki"
D'ago kai tayi tana kalloshi har aka buɗe mishi gate ɗin ya kunna kai cikin gidan.
    Bayan yayi parking ya fito ya nufi parlor Momi still yana rik'e da hannunta,

*© KHADEEJA CANDY*
[11/9, 7:00 AM] Khadeeja Candy: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

     *_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

*Vote me on Wattpad* @khadeeja_Candy

*60*

Daga Momi har Qasin tashi sukayi Suna kallonshi. nan Mairo ta shiga k'ok'arin kwace hannunta. Iya k'arfinshi yasa ya rik'e hannun gam. Ko motsin kirki ta gagara yi.
   Cikin wani irin zafin nama Qasin ya k'araso kusa dashi ya ɗaga hannu zai mareshi. Da sauri Yarima yasa ɗayan hannunshi ya rik'e mashi hannu yana mishi wani kallo.
   “Kayi kaɗan kasa wulakantaccen hannunka a fuska ta"
  Damk'e hannu Qasin yayi da k'arfi kamar mai dambe ya kai mishi naushi dai-dai k'ahon zuciya.
  Zaro ido Momi tayi ta ɗora hannu aka “Qasin mi kake k'ok'arin aikatawa haka?"
  Baiyi wata-wata ba ya sake aika mishi wani bugun.
Ba shiri ya saki hannun Mairo ya faɗi durk'ushe dafe da zuciyar. Ture Qasin Momi tayi idonta cike da k'wallah “Wai baka da hankali ne Qasin so kake ka kashe shi fice ka bar parlor nan"
   Hannu Mairo ya fisga sukabar parlor tare.
        
Part ɗin shi ya nuf har lokacin yana rik'e da hannunta.
    Bai sake ta ba sai da ya sata cikin ɗakin shi sannan ya jefar da ita saman kujera ya zaro belt ɗin shi ya hau dukanta.
     Mairo bata san zafin duka ba sai yau tunda Gwaggo bata taɓa sa mata hannu ba kuma bata bari kowa yasa mata.
   Ihu ta dinga yi tana kuka baji ba gani tun tana iya ɗaga murya har muryata ta dakushe.
  Saida yayi mata dakan da shi kanshi ya gamsu ta daku sannan ya jefar da belt ɗin yana faɗin “Daga yau duk kika kuskura kika sake bari wani namiji ya rik'a miki hannu sai na karya ki"
Yana kaiwa nan ya juya ya fice.

      Saida yayi kusan minti 30 da fita sannan ta samu ta rarrafa ta fito.
    Tana kawowa parlor Momi ta zube k'asa ta rushe da sabon kuka. Da sauri Momi ta k'arasa ta rik'o “Inna lillahi wainna ilaihi raji'un dukanki yayi Maryam?"
   Kai ta ɗaga mata tana wani irin kuka. Dak'er Momi ta lallaɓata tayi shiru sannan taja hannunta tana matsifa suka shiga ɗakinta.
   Sai da Momi ta shiga ta haɗa mata ruwan ɗumi sannan ta shigar da ita bathroom ɗin ta gasa mata jiki. Bayan ta k'are ta sake haɗa mata wasu ruwan wankan ta fito.
     Mairo wanka take tana kuka har tayi ta gama. Koda ta fito ta tararda doguwar rigar atamfa aje saman gado. D'auka tayi ta saka ta hau tsakiyar gadon ta kwanta tana sauraren ciyonkai da ya kawo mata ziyara.

***
    Bayan Sallar Isha'i Qasin ya shigo side ɗin Momi k'asa-k'asa ta amsa mishi sallamar da yayi muryarta na ɗauke da damuwa.
Kusa da ita ya zauna tana kallonta tare da sauke ajiyar zuciya,
    “Momi kiyi hak'uri Zuciyata ce ta rufe shiyasa"
Kallonshi Momi tayi “Amman kuma dan zuciyarka ta rufe saika aikata abinda in badan Allah ya gyara ba da zai iya kaimu ga dana sani? Daker Yarima yabar parlor, saboda mugun Bugun da kayi mishi duk kuma haka bai maka ba sai da kasa Maryam gaba ka dinga dukanta kamar an aiko ka"
      “Momi Yarima dai ko kashe shi nayi inada hujja tunda shi ya kawo kanshi har cikin gidan nan ya kuma ɗaukar min mata ya fita da ita Maryam kuma inba duka nayi mata ba ba zata samu  natsuwa ba"
    Kai Momi ta girgiza “Ko kaɗan Qasin duka baya gyara sai dai ya ɓata faɗa ya kamata kayi mata ba duka ba bazan yarda ba,
   Ba kuma zansa muku ido ba kai ka daketa matar ka ta daketa ba jaka bace dan haka karka sake sa mata hannu"
    Bak'ar ledar dake gefen hannun shi ya mik'a mata yana faɗin “Naji Momi ayi hak'uri bazan sake ba ga wannan maganin a bata tasha"
  Saida Momi ta sauke ajiyar zuciya sannan ta k'arɓi ledar tana faɗin “Ka turo min Mansura zanyi magana da ita"
    “Bata nan Momi nima koda na dawo ban tararda itaba daman da zan fita naga tana haɗa kayan ta"
    “Fushi tayi kenan akan wani dalili?"
  Kafaɗunsa ya ɗaga “Oho mata nidai bazan je bikonta yanzun ba tunda bani nace taje ba kuma ba wani abin akayi mata ba"
     Taɓe baki Momi tayi “Toh Allah ya kyauta"
Saida ya amsa da “Amin" sannan ya tashi ya nufi dining.
   Momi kuma ta nufi ɗakinta.

        Zaune Momi ta tararda Mairo tana cin kankanar dake gabanta da ɗai-ɗai. Ruwan goran dake gabanta Momi ta ɗauka ta k'ara zubawa a kofi sannan ta kankare maganin ta mik'a mata.
   “K'arɓi kisha jikinki zai ɗanyi sauki kamin gobe"
   Ba musu ta karɓa ta sha. ta cigaba da cin kankanar.
   A hankali Momi ta shafa kanta “Maryam dan Allah ki rik'a jin magana kinji in nace kiyi abu ki rik'ayi ki ɗinga karatun ta natsu
Kinga har makaranta nayi maganar zan saki amman sai naga natsuwarki tukuna"
   Da sauri ta kalli Momi “Na daina Momi ina son makarantan ina ne? Bazan sake ba"
   Murmushi Momi tayi “Toh sai dai naga natsuwarki tukuna dan karatu natsuwa yake so balle ba subject ɗaya za'ayi muku ba kinga za'a koya Miki yadda zaki iya saka tufafi, da tafiya, da iya magana, da dafa abinci, da zaman gidan Aure, da rubuta da karantawa,
   Har sana o'i duk ciki za'a koya muku kuma kuɗi da yawa ake kashe dan haka nafi son sai kin natsu dan bana son kuɗina suje a banza"
    Shiru Mairo tayi kamar mai tunani.
   Momi ta cigaba
       “Makarantar ba nisa nan ne gurin Abdullahi Fodio Road sunan makarantar gyara da kanki nima a radio naji ta na ɗauki number malamar na kirata mukayi magana kuma Fitar da nayi ɗazun gurin gaisuwa ma saida na biya naga makarantar,
  Dan Allah ki natsu kinji ki daina duk wani abu da kikasan baya da kyau"
   Kai kawai ta ɗaga mata taja fillo ta kwanta Momi taja zane ta rufe mata jiki tana faɗin “Ina tafar dai kinyi sallar I'sha ko?"
  Nan ma kai ta ɗaga tasa hannu a baki.

Washe gari Mairo a ɗaki tayi breakfast su Momi ne kawai sukayi a dining room.
   Nan na Momi take tabartawa Qasin maganar makarantar. Bai yi unk'urin hana taba duk da wani ɓangare na zuciyarshi baya so fatan alheri kawai yayi mata ya tashi ya fice.

    Wasan ɓoya Mairo ta dinga yi da Qasin sam bata yarda ya ganta duk gun da tasan zai iya ganin ta daina zama.
Sai da Momi tayi mta faɗa sannan gaisuwa ta dinga shiga tsakanin su kuma daga gaisuwar bata wuce ba data gaisheshi ya amsa zata tashi ta bashi guri,
    Hakan kuma sai ya soma damuwar Qasin ganin bata sakewa dashi.

   Saida Momi ta tabbatar da taji sauki sosai sannan ta ɗauke ta da kanta ta kaita makaranta akayi mata komai da ake buk'ata. Daman suna da school bus ga mai buk'ata. Kuɗin bus ɗin Momi ta biya wadda za'a rik'a zuwa ɗaukarta kullum da k'arfe 10am a dawo da ita 5pm.
     Maida hankali tayi sosai gurin karatun gashi Momi kullum cikin jaddadamata take kar tasa tayi hasarar kuɗinta
    Wata irin natsuwa ce ta sauko mata tunda ta fara zuwa makarantar kwata-kwata ta cire wasa gefe ta aje ta tattara hankalinta gurin ɗaya ta kama karantunta
  
       A makarantar darussa aka dingayi musu kala-kala tun Mairo na ganin abinda kamar lalata tarbiyane yana bata haushi har ta daina sannu-sannu abin ya fara shiga ranta.

*****
      Ranar wata Jumma'a da misalin karfe goma sha ɗaya na dare Qasin ya shigo parlor Momi.
    Mairo na ganin shi tayi saurin tashi daman ita ka ɗai ce parlor ta gaishe shi bayan ya amsa ta aje remote ɗin dae hannunta ta juya da niyar tafiya.
   Da sauri ya riko hannunta “Ina zaki Maryam?"
   Ba tare data juyo ba ta amsa mishi “D'aki kwantawa zanyi"
     “Baki tashi yin bachi ba sai da kika ganin wai miyasa kike wahalar da nine Maryam bayan kuma kin kore min mata"
   Sai a lokacin ta kalleshi “Nikan ban korar maka mata ba ita dai taga dama tayi tafiyar ta"
   “Amman dai ai saboda ke ta tafi ko?"
  “Amman kuma ni bance ta tafi ba ganin damarta ne"
    Wani dogon numfashi yaja “Fine tunda kin iya jayayya"
   B'ata fuska ta ɗanyi “Ni ba jayayya nake ba ai jayayya ba kyau kawai ina faɗan gaskiya ne"
    Taɓe baki yayi yaja hannunta. Saida suka kai bakin k'ofa sannan ta fisge hannun ganin zai fita da ita “Ina zamu?"
   “Part ɗina mana"
“Na maka mi?"
“In mukaje zaki gani"
Yana sake rik'a hanunta ta fisge.
  D'aure fuska yayi “Kinsan bana son musu ko ba dai canye ki zanyi ba ba kuma dukanki zanyi"
  Shiru tayi ta ɗanyi k'asa da kanta.
Bai bari ta tsaya tunani ba ya sake jan hanunnata a karo na uku suka nufi Part ɗin.
  
       Sama  gadon shi ya zaunar da ita.
Ita kuma gaban sai faɗuwa yake bedside drawer ya buɗe ya ɗauko wani dan karamin box Red color ya ya kalleta yace “Rumtse idonki"
   “Kamin mi?"
“Ai dai bazan cutar dake ba ko Please close your eyes"
   Rumtse idon tayi gam

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login