Showing 42001 words to 45000 words out of 85263 words
Chapter 15 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt
komai ba"
Sai da ya ɗaga mata kai sannan ta kalli Qasin murya k'asa² ta soma magana,
"Daman ranar da muka fita wani guri mukaje gurin buki daga can sai muka shiga mota zamuje wani gurin sai wasu suka cin mana da mota suka tsayar da mu duk fa suna ɗauke da bindigogi manya sun ɗauke wani mutum da sarka sai Yarima yaje yayi magana dasu har ya mari wadda aka ɗauren ya bugar masa baki ni kuma duk naji tsoro kwarai shine yace duk na faɗa sai ya kashe ni shine yace wani ya kawo ni gidan......"
kai Qasin ya girgiza "karya kike Maryam wannan ba shine kaɗai abunda ya faru ba"
rantsuwa ta shiga masa da kuka "wallahi yaya shine abunda ya faru ba karya nake ba kuma ka tambayi Yarima gashi nan"
matsowa yayi kusa da ita ya watsa mata mari da sauri ta nufi gurin Momi dafe da kuncin tana kuka,
Yarima ya kalle shi yace "ina tunani ta faɗa maka komai maye na wani dukanta kuma?"
yana nuna ta da yatsa yace "sai ta faɗamin dalilin zubar wannan jinin data shigo dashi"
"menstruation ne Qasin"
Momi ce ta bashi amsar tana share hawayen da suka zubo a fuskarta,
da sauri Qasin ya kalleta haka ya rik'a jin maganar tana masa yawo a k'wak'walwa nan da nan yaji jikin sa ba k'arfi gumi ya shiga karyo masa
murmushi Yarima yayi ya rik'a wuyan rigar Qasin da hannu biu yana gyara masa kwalar rigar yace " ba haka ake takara ba Qasin da ace kai ɗan siyasa ne da ka faɗi zaɓe dan baka iya siyasa ba i really believed da ace kai lauya ne thom da kaji kunya a gaban kotuna da dama"
sake masa rigar yayi harya juya sai kuma ya juyo ya kalleshi yana tsotsar baki yace "u knw wht my frnd we are all in th sme game bt dffrnt roads wannan karon ka faɗi bt it is a deal btwn us last rubuta Ka aje I wsh yuh a very gud luk nxt time swt drm...."
da wani shu'umin murmushi ya k'arasa maganar ya sara masa sannan ya kalli Momi yace "ki kwana lafiya Momi"
yana kaiwa nan ya nufi k'ofa,
Kiran shi Momi ta shigayi idon ta sai zubar da k'wala suke, yi yayi kamar bai ji taba yayi ficewarsa.
nan Hajiya ta matso kusa da Qasin ta kalli k'wayar idonsa cikin sanyayyiyar murya tace "ko a mafarki ban taɓa tsammanin wannan ranar ba ban taɓa tunanin zaka iya yima ɗan'uwanka abunda kayi masa yanzu ba ina saka layin masu hankali da tunani duk abunda Yusuf yake faɗa a kanka ban taɓa yarda ba sai yau ka chanja rayuwa Qasin dan Yusuf ɗan'uwankane ba abokin gaba ba"
juyowa tayi gurin Momi idonta cike da k'wallah tace "kin ɓata wayonki da kike biyewa ɗanki kuka aikata abunda ban taɓa tunani ba"
dubawa tayi ta ɗauki jakarta harta fice Momi bata ce mata uffan ba sai hawaye take,
darker Qasin ya iya ɗaga kai ya kalli Momi "Momi dan Allah kibar kukan nan wallah-"
bai k'areba ta ɗaga mishi hannu tana hannun Mairo suka nufi upstairs.
Da ido ya bisu itama Mairo ta sako masa nata idon har suka shige,
Ajiyar zuciya ya sauke ya lumshe ido iya ɓacin rai ya san Momi tayi shi shi sam bai ɗauka abun haka yake ba kuma gashi har yanzu zuciyarsa tak'i yarda da abunda Mairo ta faɗa dan shi gani yake kamar biye wa ne tayi wata ajiyar zuciyar ya sake saukewa sannan ya buɗe idon ya nufi part ɗinsa jiki ba kwari,
duk wannan abun daya faru a idon Siraj ya faru dan yana tsaye a windon baya yan kallon su baby komai a I donsa sai kwallah dukawa yayi a gurin ya dafe kai,
sululu ya shiga parlor harya zauna bai lura da Mansura ba dan kwata² hankalinsa baya jikin shi "sai yanzu ka dawo ai daman nasan haka zai rik'a faruwa tunda ta dawo"
maganarta ce ta dawo dashi daga dogon tunanin daya tafi kallon ta yayi cike da jin haushi yace "gurin ta naje ko zaka hana ne?"
da sauri ta tashi tsaye "Qasin ni kake faɗawa wannan maganar?"
"an faɗa miki ke wace irin macce ce haka damuwa mijinki bata dameki ba sai kishi tirrr da halinki sai yanzu na soma yarda da wayansu kalamai da Momi take faɗa a kanki ba kida tunani wlh"
idon ta cike da hawaye tace
" *HAKA NAMIJI YAKE* banyi mamakin jin wannan kalmar daga bakinka ba daman nasan Momi ba sona take ba daman nasan-"
tassssssssss ya wanke mata fuska da mari yana nuna ta da yatsa yace "iskancinki ya tsaya kaina karki kuskura saka Momi a ciki dan ba sa'arki bace"
Baya² tayi tana kallon shi wani tsoro ne ya kamata wadda ko faɗa baya son mata yau gashi harda mari juyawa tayi da gudu ta shige ɗaki tana kuka,
faɗawa yayi zaune saman kujera ya lumshe ido "oh ya Rabbi" abunda ya furta kenan yana cizon baki,
'''*** * ** ***'''
cikin wani irin ɓacin Yarima ya isa gida yana sauke Hajiya ko motar bai fito ba ya nufi gidan sa,
cikin yan mintuna ya isa sakamakon gudun da yake ido a rufe yayi parking ya nufi k'ofar parlor da k'arfi ya tura k'ofar ya shiga yana wani irin numfashi da k'arfi.
zaunawa yayi yana murmushi mai cike da jin haushi yana kaɗa kai "lallai Qasin kana wasa ni zaka yima irin wannan siyasar hmmm yanzu ne ko zaka gane wanene ni dan saina aure ta"
wayarka ya ciro ya shiga danna neman number sannan ya danna callin bara daɗe tana ringing ba aka ɗauka "clock ka sameni gida gobe" haka kawai yace ya kashe wayar,
a hankali yaji an kai hannun ana taɓa shi tun daga k'eyar kansa har zuwa kirjinsa k'ara haɗe fuska yayi ya ɗaga idanuwansa sama yana faɗin "don't Zil am not in the mood......"
*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com
*44*
Yi tayi kamar bata jishi ba ta cigaba da shafa shi,
Hannun ta ya fisgo da karfi ya yarfar ya tashi tsaye yace "nace miki am not in the mood bakida hankaline?"
Da sauri ta Kalleshi tsantsar ɓacin rai ta gani a tare dashi "Yarima mi yake damunka waya ɓata maka rai?"
Sama yayi da kansa "Zil miya kawo ki nan?"
"wannan wace irin magana ce ai kasan banada gurin zuwa sai nan wai wane irin ɓacin rai ne ya rufe maka ido haka Yarima Kaga yadda ka koma kuwa?"
Fuskarsa ya shafa yana yak'unar hanci "u are right Ni kaina nasan na chanja na daɗe banga ɓacin rai irin wannan ba ban taɓa sanin inason Maryam ba sai yau kuma kota halin yaya sai na aure ta koda sama da k'asa zasu haɗe"
cikin rashin fahimta tace "ban gane ba Yarima wata kake so ne?"
Murmushi yayi "yes wata kyakkyawar yarinya ce mai k'ananan shekaru kuma yar k'auyen"
Kai ta girgiza "kasan da ni kake faɗawa wannan maganar ko dai wani abun kasha?"
tana kare maganar ya wanke mata fuska da mari biu ya nuna ta da yatsa "karki kuskuren faɗa min kalmar da zata daɗamin ɓacin rai ɓace ki bani guri"
yanayin fuskanta naga ya chanja cikin ɓacin rai tace "babu inda zanje kawai ka fada min aure zaka yi ko me?"
gira ya ɗaga mata "yes aure zanyi tsoronki nake jine"
"tho ni kuma kayi yaya dani?"
"ai nasha faɗa miki Zil bazan taɓa iya aure ki ba maybe bazaki yarda ba har sai kinga matata a cikin gidan nan"
kwalla ne suka cika mata ido cikin muryar tausayi tace "amman ka ɓata min rayuwa Yarima ka raba ni da karatuna kasa na watsarda samarina"
murmusawa yayi ya taso yazo daf da ita ya ɗora hannayensa saman kafaɗarta yace "kina da matsala Zil mi yasa kike ɗora min wayannan laifukan koda yaushe ni ban lalata miki rayuwa ba kuɗine suka ja hanalinki kikaga zaki iya kum gwargwado na kyautata miki tunda na baki mota na kai ki makka na mallaka miki gida na cia miki account ɗin ki and what else do you need?"
Hannunsa ta rika hawaye nabin fuskanta tace "duk abunda ka zana yanzu ba sune a gabana ba aurenka nake so shine cikar burina"
Kai ya girgiza ya janye hannunsa "am so sorry Zil dear bazan iya yi miki wannan ba"
Cikin ɗaga murya tace "ba a haifi matar da zaka aura ba Yarima ba ayika dan ko wace mace ba sai ni kuskure ne kasa son wata a ciki zuciyar ka matukar ina raye"
Fashewa yayi da wata mahaukaciyar dariya yasa kafarsa ya kaɗe mata kafafu ta faɗi da karfi sai da kashinta ya amsa (yayi kara) sannan ya sake kai mata wani mugun shuri ba shiri ta saki ihu ya nuna ta da yatsa yace "ba'a faɗa min irin wannan maganar be careful next time ɓace min da gani"
da sauri tayi baya² ta shige ɗaki da kuka,
shi kuma ya zauna saman kujera yana cikama bakinsa iska
bai bar parlor ba sai kusan 3 dare bayan y gama sake² ya nufi bedroom,
zaune ya tararda Zil babu abunda take sai kuka tana rike da kunkurota kamar mai shirin haihuwa, yana kallonta yaja tsaki ya shiga toilet ya watsa ruwa ya fito
yana cikin saka kayan bachi yace "baci zanyi malama ko kiyi shiru koki fita kije gidan ubanki" ba shiri ta hade bakinta ta matse haka rage hasken wutar ɗakin yayi kwanciyarsa ya barta zaune.
*WASHE GARI..........*
8:34am Qasin ya shigo part ɗin Momi bai iya yin sallama ba saboda bugun gaban daya sami kansa dashi har ya isa dining room,
Nura da Usman suna zaune suna karyawa Momi kuma ta tisa abincin a gaba tana kallon wani guri
Mairo ce ta Kalleshi tace "yaya ina kwana?" da murmushi ya amsa mata "lafiya kalau Maryam an tashi lafiya?"
Kaita ɗaga mishi ta na dariya nan suma suka shiga gaida shi bayan ya amsa ya kalli Momi yace "Momi an tashi lafiya?"
ba tare data ɗago ba ta amsa mishi "lafiya kalau"
cikin sanyi jiki yace "dan Allah Momi kiyi hak'uri wallahi banyi-"
kasa k'arasa maganar yayi sakamakon ɗagowar da tayi ta ɗaga mishi hannu "karka kuskura fitar da kalma ko ɗaya daga bakin ka matuk'ar ni zaka furtawa ita kawai ka fita kabar parlor nan"
Nan da nan yanayinsa ya kara chanjawa bugun zuciyarsa ya karu kamar ya fasa kuka yace "dan Allah Momi karkiya fushi dani dan adam ne ni ajizi wallahi banyi hakan dan na ɓata miki rai ba dan Allah ki gafarce ni"
Momi fuska a ɗaure tace "bana fushi da kai tun har na iya amsa s
gaisuwarka kawai dai ka ɓace min da gani nace"
tsayar da cin abinci Usman yayi ya kalli ta yace "Momi lafiya?"
"babu ruwan ka kuma karka kuskura sa min baki a magana kaima inka kare ka tashi ka fice"
k'asa yayi da kansa shida Nura suna mamakin abunda yasa ran Momi ya ɓace haka,
tsaye Qasin yayi yana kallonta kamar ba dashi take maganar ba sai son yake yayi magana kuma ya kasa
ganin haka yasa Momi ta tashi ta bar mishi parlor,
Jinginawa yayi da ginin dake gurin ya dafe kai yana cizon baki ya daɗe a haka sannan shima ya juya ya fice,
Nura da Usman ma suna ganin ya fita suka tashi suma suka fice aka bar Mairo ita kaɗai sai cin abincin ta take tana yan wake²,
baifi 5 minutes da fitar su ba Siraj ya shigo fuskarsa babu yabo ba fallasa sallamar ma ciki² yayi ta Mairo ta amsa masa ta kaɗa kai "taf lallai ma kai wannan yaron sai yanzu kaga damar tashi har kowa ya gama breakfast? Kayi olo ma dan abincin ya k'are"
Murmushi ya ɗan yi "aini ba abinci zan ci ba"
gyara zama tayi "saboda me?"
shiru ya ɗanyi sannan yace "a zumi nakeyi"
taɓe baki tayi "thom kun zama ɗaya kai da Momi kenan"
"itama a zumin take ne?" ya tambaya saida ta girgiza kai sannan ta bashi amsa "a a bata dai ci abinci ba"
"miyasa?"
"Nima ban sani ba kila bata da lafiya dan tun jiya kuka take ko bachi bata yi ba"
da a sauri ya nufi upstairs jikinshi na rawa ya tura k'ofar ɗakin Momi,
da sallama ya shiga ta amsa masa da muryar kuka "wa'alaikassalam"
kusa da ita ya zauna yana faɗin" Momi kuka kike yi ne?"
bata iya ce masa a'a tunda yaga hawaye a idonta kawai sai kawarda fuska,
Hannun ta ya rik'a "dan Allah Momi kibar kukan nan Maryam tace tun jiya take kukan nan"
hannu tasa ta share hawayen tana faɗin "dole inyi kuka Siraj jiya Qasin a gaban Hajiya ya aibanta Yarima ɗan ta kwara ɗaya ɗan da tafi kowa sonsa ban taba ganin bacin ranta ba irin na na jiya wani abu bai taa haɗa ni da itaba sai jiya kuma nasan zata rika ɗaukar na hana ma ɗanta Maryam da nasan rikonta haka zai zamar min daban ɗauko ta ba tun farko"
Ajiyar zuciya Siraj ya sauke yace "har gobe Momi bazan basa faɗa miki ba Yarima bai dace da Maryam ba dan ba mutumin kwarai bane taya za a ɗauki karamar yarinya kamar Maryam a aura masa kada ki sake ɓata ranki akan wannan hukuncen da kika yi dan ni banga wata matsala ba"
Momi tace "akwai matsala Siraj dan yanzu ganin suke na hana Yarima auren Maryam na aura mata wani"
tashi yayi tsaye ya kalleta yace "Momi kina son Yarima sosai da badan wani abuba da nace kinfi sonshi sama da mu da muke yayanki"
Lumshe ido tayi ta sauke ajiyat zuciya shi kuma yasa hannayensa aljihu ya fice,
''' *** *** *** '''
duk inda yabi gaishe shi ake cikin girmamawa har ya isa parlor Hajiya zaune ya tararda ita tana cin apple wata baiwa na matsa mata kafafu Hajiya na ganinshi ta janye kafafun nata tayi mata alama data ta fice cikin sauri ta tashi ta gaida Yarima ta fice,
Karasowa yayi kusa da ita ya zauna ya ɗauki apple ɗin ya kai baki ganin bai yi mata magana ba yasa ta kalleshi yadda taga fuskarsa a ɗaure tasan akwai wata a kasa saida ta ɗanyi gyaran murya sannan tace "ɓacin ran jiya ne ko kuma na yau dn nasan Mai martaba yayi maka magana?"
ba tare da ya kalleta ba yace "saboda mi Mai martaba zaisa min baki a neman aure?"
"saboda bata dace da kaiba haba Yusuf koda basu wulakanta kaba ai kaima kasan bai dace ka auri wannan yarinyar ba ga yayan manyan mutane masu aji masu kyau wasu m har sun nuna suna sonka amman ka kai kank gunda za a wulakanta ka karama da ba ayi auren ba dan Mai martaba ya nuna baya so kamar yadda nima bana goyon baya"
kallonta yayi yana murmushi yace "nima zuciya tace take so ba ni ba kuma aure sai anyi shi no matter what dan haka kuso abunda ɗan ku yake so kawai"
fuskantar a haɗe ta kalleshi "saboda baka da zuciya ko shiyasa har yanzun kake son ta ina mamaki ka Yusuf kwata² ka chanja wai mi ka gani a jikin yarinyar nan ne.....?"
kamin ya bata amsa wayarsa tayi ringing ciro ta yayi ya danna picking ya kara a kunne,
banji mi akace masa ba murmushi kawai naga yayi yace "good job an samoshi kenan.........bani minti biyar"
da kallo Hajiya ta bishi har ya tashi tsaye sannan tace "waya kira ka a waya mi kake kokarin aikatawa?"
kallonta yayi fuskarsa ɗauke da far'ah ya rika hannunta yace "babu komai Ummi na ɗan ki ba zai aikata wani mummunan abu ba just trust him okey?"
bai jira cewarta ba ya sakarma hannun nata kiss ya fice yana murmushi.
*_©KHADEEJA CANDY_*
[11:27PM, 3/17/2017] Khadeeja Candy: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com
*45*
Haka Momi ta share kwana da kwanaki bata kula Qasin iyakarta dashi gaisuwa babu hanyar da bai biba na ganin ta dawo normal amman abun yaci tura dole tasa ya hakura ya kyaleta,
Wata ranar Asabar Momi na zaune parlor tana tunane² Siraj ya shigo guri ya samu kusa da ita ya zauna kasan carpet cike da ladabi ya kalleta yace "Momi wai miyasa yasa ba zaki ɗaga ma ya Qasin kafa ba Momi wadda fa kike abun nan danshi baima san kinayi ba dan me zaki rika fushi da ɗanki akan ɗan wata Momi"
Ajiyar zuciya Momi ta sauke irin nasu na manya sannan ta ɗan gyara zamata tace "bana daga cikin iyayen da suke fushi da y'ay'ayensu dan fushi iyaye yana tare da fushi Allah ko kaɗan ni bana fushi da Qasin kawai dai inason nuna masa kuskuren daya aikata babbane gaba karya sake aikata shi kuma wani gefen ma bana ganin laifinsa laifin kaina nake gani dana ɗauko Maryam riko har Yarima ya ganta ya nuna yana so kuma na hana shi ita wannan abun shine ya tsaya min a rai shiyasa yanxu na yanke shawarar ma yarda ita gurin Gwaggonta kusa da mijinta"
kallon rashin fahimta Siraj yayi mata "kina nufi ki ma yarda Maryam kauye kenan?"
"haka nake nufi kuma hakan shine kwanciyar hankali"
Amsar Da Momi ta bashi kenan a takaice
"amman Momi naga ai abunda na faru ya riga ya faru kuma kin riga kince yarinyar nan karatu zatayi mijinta yayi Na'am itama tana so Gwaggo ta amince dan me kuma yanzu zaki ce ki maida ta itama ai ba zata jidadi ba"
Motsa baki Momi tayi "ma yarda ita ya zama dole a gareni kodan suma na sama musu sukuni"
"ki sama musu sukuni su suwa?" Siraj ya tambaya
Momi saida ta nisa sannan tace "satin daya wuce Gwaggo ta kirani a wayar haruna tace mun wasu daga birni zunzo neman auren Maryam an faɗa musu tana da miji shine suka samu halilu sukace zasu bashi kuɗi mai yawa ya sake ta shi kuma ya k'i Aminta babu irin rarrashin da basu yi masa ba yak'i sun jera kwana da kwanaki suna zuwa har suka ce masa matukar bai rabu da itaba komai zai iya faruwa dashi"
keɓe baki Siraj yayi "ba kowa sai Yarima dan babu wadda zai aikata haka sai shi dan sheɗan kaɗa masa ganga yake yana rawa"
Momi tace "hakan yasa nake son maida ta kusa da mijin ta kar wani abun ya shiga kuma adawo ana ganin lafin juna"
"babu wani ganin laifi Momi kawai ki barta tayi karantunta shi kuma darasi yake son a koya masa"
kai Momi ta girgiza "a'a bana