Showing 21001 words to 24000 words out of 85263 words

Chapter 8 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt

04 Apr 2026

887

fuskarsa ya kunbure,
murmishi ta ɗan sakar masa tace "yaya"
shima murmushin yayi mata yaja mata kujera ta zauna a kusa dashi "maryam kin tashi?"
"eh tun ɗazu"
"eh kaima kaci?"
kai ya ɗaga mata yana yana taɓa gurin daya kunɓurar mata "dukan da nayi miki jiya ne?"
taɓa gurin tayi "eh shine yaya karkayi fushi dani"
laptop ɗinsa ya matsar gefe ya kara matso da kujera kusa da ita "ba zanyi fushi dake ba maryam dukan jiya ma rai nane ya bace kiyi hakuri kinji?"

hawaye ne suka zuɓo mata "yaya ni banma ce ya bani kuɗi ba shine ya bani kuma bance ya sani mutarshi ba shine ya sani"
cikin kuka ta karasa maganar,

tausayinta Qasin yaji duk sai yaji ba daɗi hannunsa yasa yana share mata hawayen "ya isa daina kukan haka kinji bazan sake dukanki ba"
ɗagowa tayi ta kalleshi "kayi alk'awari?"
"eh nayi"
saida taja majina tace "malamin mu yace ba kyau saɓa alk'awari"

dariya yayi yace "maryam kwan wayo na yarda amman sai in kin min alkawari nima kin yarda"
"eh minene?"
ido ya tsura mata yayi shiru yana mata murmushi,

ganin haka yasa tace "yaya lafiya?"
ajiyar zuciya ya sauke yace "kalau kesan mi nake so dake?"
"a a saika faɗa"
"so nake karki sake kula Yarima duk abunda ya baki karki sake karɓa"
shiru tayi "koda kuɗi ne yaya"
"eh koma minene"
kai ta ɗaga mishi "tho bazan sake ba"
murmushi yayi ya rumgumeta yana faɗin "yauwa maryam ɗina"

"yaya mi yasa baka shiri da Yarima?"
daidai kunnensa tayi masa tambayar.
ɗagota yayi yana murmushi ya tashi ya rufe laptop ɗin ya mika mata "jeki ki kaimun ɗaki"
tashi tayi tsaye jikinta na rawa ta karɓi laptop ɗin tana kallonsa,
juyawa yayi ya nufi part ɗin momi ya barta nan tsaye.

laptop ɗin ta tsurawa ido tana shafawa maganganun Yarima suka rika mata yawo akai tunawa zuciyarta ta shiga mata zance biu akai akai takan kai duba gurin rijiyar dake gefen gurin sai faman haɗeye yawu take,
dukan da Qasin yayi matane ya faɗo mata rai nan da nan sai tsoro ya shigeta,
da sauri ta juya ta nufi part ɗinshi.

''' ***************** '''
*_6:15pm..._*
Qasin ya shigo part ɗin momi da sallama yana murmushi,
Nura da Usman suka amsa masa Maryam kuma ta tashi da gudu ta tarɓoshi "oyoyo yaya"
shafa kanta yayi "maryam oyoyo bita kikeyi?"
sakinshi tayi tana faɗin "eh kuma yaya iya"
zaunawa yayi yana sauke gajiya "yayi kyau haka nake so ina momi?"
"tana ɗaki bari na kirata"
da gudu ta nufi ɗakin tana kwalawa momi kira,

tare suka fito tana rike da hannun Mairo da murmushi ta zauna tana kallon Qasin "injin anyi nasara?"
dariya yayi yace "anyi momi saidai fa akwai yar matsala"
nan da nan yanayin fuskar momi ya chanja "wace irin matsala kuma?"
"wai sunce zasu min interview gobe bance wadda suka min yau"
"daman abun harda interview akeyi sai kace ɗaukar aiki"
ajiyar zuciya ya sauke "nima abunda yaban mamaki kenan momi kuma kinsan wani abu?"
"a a minene?"
"Yarima ne zai min interview ɗin kuma wai sai nazo da laptop ɗina sunga irin aikin da nayi"

lumshe ido momi tayi "oh ni har ka faɗarmun da gaba wannan tho ai ba wani abun ɗaga hankali bane sai kaje da ita ka nuna musu kuma duk abunda suka tambayeka ka basu amsa"
"momi bakiji mi nace ba Yarima fa zai mun"
"tho minene a ciki ai baka kirsa cikin aikinka ko kaɗan bana fargaba akan aikin da za'ayi maka"
"momi tsoron nake kar Yarima yayimin wani abun kinsan halinsa"
"karka taɓa saka wannan a ranka ka yarda da kanka Qasin karka bari damar nan ta wuce ka kaifa kmda kanka ka faɗa min kuɗine masu yawa"
kai ya ɗaga mata yana kallon maryam,

Usman yace "yaya ya akayi Yarima ya zama shine zaiyi maka interview ɗin"
Qasin yace "nima ban saniba amman dai kasan yana hulda da motocin kasashen waje kuma kasan tunda Illustrator ne inajin shiyasa"
"Allah dai ya baka nasara yaya"
duk suka amsa da 'amin'
sun ɗan jima suna fira saida aka kira sallar magriba sannan kowannensu ya tashi momi da maryam kuma suka nufi ɗaki dan sallah.

*_Monday @10:30am..._*
cikin nasara akayiwa Qasin interview duk yadda Yarima yaso ya samu matsala Allah bai yarda ba duk abubuwan da suka bukata saida ya nuna masu Yarima yayi mamaki sosai ganin laptop ɗin,
bayan fitarsa akayiwa mutun 3 duk basuji sun gamsu dasu ba kamar yadda sukaji da Qasin sun daɗe suna ttaunawa kamin su yanke hukunci sosai Yarima yaso a bawa wani ba Qasin ba amman suka ki yarda dan sun lura da gwarewarsa nesa ba kusa ba,

*_2 hours letter..._*
suka aika aka kira Qasin daya shigo suka sake yi masa wasu tambayoyi,
ya amsa musu fiye da yadda suke tunani nan suka kara jindaɗi Yarima suka bawa files ɗin cike da jin haushi ya mika masa,
Qasin na murmushi ya karɓa yayi sign fuskarsa a sake ya mikawaƳYarima files ɗin yana murmushi yace "thank you"
murmushi Yarima wadda bai kai zuci ba "ur welcome Men"
hannu suka rika mikawa Qasin sunna masa congrats,

'''**********************'''
cike da jindaɗi Qasin ya shigo gida kai tsaye part ɗin momi ya nufa tun daga sallamarsa ta gane haka bata masa magana ba saida ya zauna "an daiyi nasara ko?"
dariya yayi ya mika mata jakar dake hannunshi "anyi momi sun bani"
ba karamin daɗi momi taji ba saida ta gama duba laptop ɗin sannan tayi ma Allah godiya "Alhamdulillah Allah mun gode maka haka nake so Alhamdulillah Yarima yaje?"
"eh tare dashi akayi komai shima ya bani files ɗin nasa hannu"

"masha Allah Allah ya tayaka riko"
"amin momi kinga fa ko breakfast banyi ba"
maganar yake yana wani sosa kai,
taɓe baki momi tayi tace "zakaci albakacin wannan ranar zan baka na yau"
murmushi yayi "aiko momi da kin kyauta"
tashi yayi ya nufi dining yana faɗin "yau momi gidan sit ba kowa"
"to ai kasan yau monday wazai zauna nima anjima kaɗan fita zanyi"
"tho bari na daukeki dan nima fitar zanyi"
taahi momi tayi ta nufi upstairs,
"bari na shirya wani abin kamin ka kare"
"owk momi"

kujera yaja ya zauna ya hau cin abincin har wani sauri yake yana lumshe ido raban da yaci abinci mai daɗi haka har ya manta kullum cikin siyen takeaway yake gashi abinci inba na momi ba baya jindaɗinshi,

kusan plate biu yaci yasha zoɓon da momi ta haɗa ya tashi yana hamdallah,
part ɗinsa ya nufa bai daɗe ba ya fito ya sake nufo part ɗin momi bayan ya ɗan watsa ruwa ya chanja kaya, zaune ya tararda ita tana jiranshi,
"momi har kin shirya?"
"eh so nake nayi saurin dawowa kar maryam ta dawo gidan ba kowa"
agogon hannunsa ya duba "gashi ko sun kisa dan 12 ta kusa"
tashi momi tayi ya ɗaukar mata jekar dake gabanta suka fice.

*_2:34pm..._*
Mairo ta shigo gida kamar ta fasa kuka ta nufo parlour dan tun gate maigadi ya faɗa mata momi bata nan,
jefa tayi da jakarta tsakiyar parlour ta nufi upstairs,
tana shiga ta cire uniform ɗinta ta ɗauki tawul ta ɗaura ta shiga bathroom wanka tayi tare da alwala sannan ta fito sai wani tureturen baki take tana matsar kwallah,
wadurof ta nufa tana buɗewa taji an kira amsawa tayi duk da bata san mai kiran ba ta rufe wadurof ɗin da sauri ta nufi kofa.

candynovels.wordpress.com

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*22*

da sauri ta sauko stairs tana rabon ido dan bata ga kowa ba har ta nufi kofa taji an rikota,
juyowa tayi da sauri suka haɗa ido da Yarima sosai ta razana ganin fuskarsa a haɗe gashi batayi tsamaninsa,
kokuwa ta shigayi dàshi tana son kwace kanta jikinta har wani rawa yake.
iya karfinsa yayi wurgi da ita saman kujera cikin jar fuska yace "mi yasa kika karya alkawarin?"
tashi tayi zaune tana kuka tace "yi hakuri dan Allah karka dakeni"
risinawa ya shafa gefen fuskarta "baki son na dake ki miyasa kika ki aikata abunda na saki? mi yasa maryam?"
shiru tayi tana kallonsa hawaye na mata zuba.
hannu yasa yana share mata wayarsa tayi ringing,
saida ta kusan katsewa sannan ya ɗauka banji mi akace masa ba saidai naji nace "Gret mun faɗi sai dai mu tari gaba... owk sai na ganka"
yana aje wayar ya tashi tsaye yana tafiya bayabaya fuskarsa ɗauki ke da murmushi saida ya kai kofa sannan ya juya ya fice,

ajiyar zuciya ta sauke ta kawanta saman kujera dafe da zuciya.
ta kusan minti 20 a haka sannan ta tashi ta nufi ɗaki,
cikin kankanen lokacin tayi shirin islamiya ta ɗauki littafanta ta nufo downstairs.

cike da tsoro ta sauko sai leke2 take har ta samu ta fita parlour,
har ta isa harabar gidan bata daina jin tsoro tana kisan isa gate motarsu momi ta kunno kai,
Qasin nayin parking mairo ta nufi momi ta rumgumeta idonta cike da hawaye.
murmushi momi tayi ta rumgumeta "maryam kin dawo?"
kamar tayi kuka tace "eh momi ki daina fita kina barina"
"tho na daina maryam jeki islamiyar karkiyi latti"
kin ɗagowa tayi saida taji an ja mata kunne sannan ta juyo da fuskar ta kalli Qasin,
murmushi ya sakar mata ya buɗe mata mota "shiga na kaiki"
ba musu ta shiga bayan ya rufe ya shiga mazaunin direba yayi ribas suka juya momi kuma ta nufi cikin gida.

tukin yake yana kallonta ita kuma kanta na kasa sai murza yatsunta take tana haɗiyar yawu,
A'hankali ya rage gudun da yake ganin haka yasa ta ɗago ta kalleshi suna haɗa ido yace "mi yake damunki maryam?"
shiru ta ɗanyi sannan tace "babu komai"
Qasin yace "kinsan ba kyau karya ko?"
kai ta ɗaga mishi
"tho faɗa min miya ke damunki?"
"nace maka babu komai"
"Yarima yazo?"
batace masa komai ba har yayi parking daidai gate ɗin makarantar saida ta buɗe motar zata fita sannan tace "eh yazo"
da sauri ta rufo motar ta nufi cikin makarantar,

saida ya daina hangota sannan yayima motar key da sakesake ya iso gida yana tuna yadda mairo ta rumgume momi,
har ya nufi part ɗinshi wani tunanin ya dawo dashi gurin maigadi ya soma masa tambayoyi bayan sun gaisa "Sadiqu bayan fitarmu waya shigo?"
"babu wadda ya shigo inba Yarima ba"
"ya jima nan?"
"a'a bai jimaba ya fita"
kai Qasin ya ɗaga mishi "owk na goɗe"
ya juyo ya nufi part ɗin momi,
da sallama ya shigo saidai bai samu mai amsa masa ba dan babu kowa parlour.
guri ya samu ya zauna yana sauke ajiyar zuciya sai kallon parlour yake ta ko ina kamar wani bako,
ya daɗe haka sannan ya tashi ya nufi part ɗinshi.

*_washe gari..._*
*7am* Qasin ya shigo part ɗin momi,
momi na kicin tana aiki taji shigowar mutum hakan yasa ta nufo parlour,
Qasin na ganinta yace "an tashi lafiya momi?"
"lafiya kalau"
"masha Allah maryam tqa tashi?"
da ɗan mamaki momi tace "eh tana ciki shirin makaranta take yi lafiya dai"
murmushi yayi ya nufi stairs "lafiya kalau momi abu zan bata"

a hankali ya tura kofar ya shiga tana zaune tana saka safa tana ganinshi ta saki murmushi "yaya ina kwana?"
"lafiya kalau maryam kin tashi lafiya?"
"lafiya kalau"
zaunawa yayi kusa da ita yana faɗin "shirin makaranta kikeyi?"
"eh"
"yayi kyau"
kafarta ɗaya rika yana saka mata safar "maryam jiya da Yarima yazo mi yayi miki?"
ɓata fuska tayi "nidai ba nace maka bai min komai ba bai min komai ba"
"tho miya yace miki?"
"nidai baice komai ba kawai yace gurin momi yazo kuma bata nan harda kuɗi ya bani amman ban karɓa ba sai yayi tafiyarsa"
tana maganar tana wani ɓalɓal da ido karya gano karya take.
daɗi Qasin yaji sosai da kanshi ya saka mata jikar makarantar yana murmushi yace "yauwa maryam daɗina dake jin magana kin kyauta da baki karɓi kuɗin nan ba"
rufe ido tayi ta fashe da dariya da gudu tabar ɗakin,

'''***********************'''
tafiya yake yana shewa (fito) hannayennsa na lakkame a bayansa.
duk gurin da yabi sai sun gaisheshi jiki na rawa amman ko kulasu ba yayi bare ya amsa gaisuwar sai wani rangashi yake har ya iso maidaidaicin parlour,

guri ya samu ya zauna bayan ya gaisheta ya ɗora kafa ɗaya saman ɗaya yana wani lumshe ido,
tsakin da yaji tayi ne ya sashi ɗago kai ya kalleta yana kalkatar dariya "haushi nake baki ko hajiya?"
taɓe baki tayi "Yusuf na gaji da maka magana na gaji da saka maka ido haba Yusuf sai kace wani yaro karami kullum ayita faɗar abu ɗaya ana maimai tawa"

rufe baki yayi kamar wani mai jin hamma "sorry hajiya komai ya kusa zuwa karshe na samu wadda nake so jira kawai nake ta karasa girma"
kallon rashin fahimta Haiyar tayi mishi "ban gane ba?"
murmushi yayi "na samu wadda nake so saidai karamace amman idona na kanta data girma zan ɗauke abunta"
maganar yake yana wani ɗaga hannu sama yana taɓe baki kamar wadda yasha wani abu,
kai Hajiya ta girgiza "Yusuf lafiyarka kuwa ban sanka da wannan halin ba"
dariya yayi yace "nayi miki kama da yan shaye2 ko kinfi kowa sanin bana shaye2"
"tho mi yasaka cikin wannan halin?"
"tsabar bakin ciki ne kawai"
"bakinciki kamar ya?"
kafaɗunsa ya ɗaga ya tashi tsaye yana faɗin "barshi kawai hajiya kona faɗa miki bashi da rana"
cikin rashin jindaɗi tace "Allah ya sauwake"
dariya yayi yace "amin bari naje ciki"
kofa ya nufa yana saida ya kusa fita sai kuma ya juyo ya kalleta yace "wlh hajiya bana shaye2 kuma ba wani abun na shaba karki saka wannan a ranki kinji dai na rantse wannan abun da nake tsabar bakincikine da kuma yunwa"
a jiyar zuciya ta sauke iya Tabbacci tana dashi akan Yarima baya shaye2 ko babu komai yakan yi mata irin haka wani lokacin saidai ba kamar na yau ba.
a kasale ta kalleshi tace "na yarda dakai Yusuf baka taɓa aikata irin wannan amman mi yasa ka bakinciki haka?"
yana rike da kofa yace "wani abin na sawa gaba kuma ban cima masara ba shiya ɓata min rai har na kasa cin abinci tun jiya amman karki damu yanzu zan koma daidai dan na hari gaba"
"Allah ya yaye maka ko minene Yusuf na yarda da kai"
murmushi ya sakar mata "good mother"
saida ta masa murmushin sannan ya fice.

*©Khadeeja Candy*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*23*

yanzu hankalin mairo a kwance yake dan ta daina ganin Yarima ba tada wata matsala inba ta jarabawar da suke ba dan momi bata barinta ta zauna data dawo gida kullum ciki karatu take banda wadda ake mata a makaranta da kuma wanda Siraj yake tisa mata Qasin ma wani lokacin yakan mata,

'''*********'''
yau Mairo da far'ah ta tashi ita ta da shi kowa na gidan tare suka shiga kicin da momi aikin komai tare sukayi,
bayan sun kare ta shiga jerawa a dining tana wakewake momi na zuba mata abinci a kula tace "maryam yau far'ah me kike haka?"
fashewa tayi da dariya "oh momi kin manta yau muke kare jarabawa shikenan sai hutu"
momi ta rufe kular tana faɗin "o na ganoki shiyasa kika tashi tun safe haka tho Allah yasa a kara muku wata har 8"
da fuskar zolaya momibta karasa maganar
mairo ta marairaice fuskar "Allahumma a'a Allah karka amsa momi wlh bana son haka"
dariya momi tayi tace "tho na daina amman dai kinsan ta ɗaya zaki ɗauko mana ko?"
dariya tayi ta rufe ido "momi dan kinga ban iya ba ko?"
"a a kin iya maryam Allah dai ya bada sa ah"
"amin momi kin san kince in an mana hutu zaki kaini gurin Gwaggo ko?"
"eh anyi haka tho bari a muku hutun"
rumgume momi tayi cike da jindaɗi kamin ta sake ta ta ɗauki kular makarantar ta fice dan tuni motar makarantar ta iso,

*_2:37pm..._*
ta shigo gida uniform ɗinta duk ya bace da k'asa tafarta ma babu kyau gani,
tafiya ta rikayi laɓalaɓa har ta isa kofar parlour ta shiga leke.
cikin rashin sa'ah ta hango momi zaune ita da Siraj da sauri ta koma baya,
can kuma ta sake lekowa momi kamar wadda aka tsikara ta waigo suka haɗa ido.
"lafiya maryam kike laɓe?"
kara laɓewa tayi ta yadda fuskarta kawai ake gani tace "momi uniform ɗina duk yara sun lalashi"
"kamar ya? shigo mana"
"kasa suka samin kuma nidai banma yi qasan kasa ba sune suka samin"
"tho shigo"
"bazaki dakeni ba?"
"eh shigo"
daker ta shigo parlour tana wani kakkaɓen2 muna furci.

ɓata fuska Siraj yayi "yanzu maryam da girmanki zakiyi wasan kasa haka?"
harara ta watsa masa "ina ruwanka nida momi nake magana bada yara kananuba"
dariya Siraj yayi momi kuma tayi murmushi hakan yasa ts ɗan saki jiki ta matso kusa da momi "momi ni yarane suka ɓata uniform ɗin harda kular suka fasa marfin kawai suka barmin"
sai a lokacin momi ta lura da murfin kular dake hannunta,
Siraj yace "karya kike kedai kika fasa da kanki ai nasan halinki"
kamin mairo tayi magana momi ta tari numfashinsa "tho ai babu komai sai a siya mata wata aini tunda tana karatu komai zan iya yimata"
gwalu tayiwa Suraj tana daddalomai ido "yaee an bashi red card"
shikan inbanda dariya babu abunda yake ganin abun nata ba mai karewa bane yasa momi ta riko tace "kyaleshi haka jeki wanka kiyi sallah sai muci abinci"
saida ta kara masa gwalon sannan ta nufi stairs.

da dare mairo na zaune parlour ita da Qasin suna game Siraj ya shigo,
aiko daman neman tsokana yake haka yasha mur yace "ke tashi muje kiyi karatu"
juyowa tayi ta kalleshi tayi mai fari da ido "kai dan Allah ja can yaro ba sauran karatu mun kare jarabawa hune kawai zayi mana yaro"
dariyace ta suɓucewa Siraj Qasin ya kalleta yace "Siraj ɗin ne yaro?"
"eh yaro ne man baka ga ka girme shiba"
"tho ai shekara kaɗan na bashi"
"eh duk da haka dai yaro ne"
maganar take tana wani war da ido tana jujjuya baki,
fashewa Qasin yayi da dariya Siraj ma da dariyar ya nufi dining.

game ɗin Qasin ya kashe ya rika hannunta "tashi muje muci abinci"
ɓata fuska tayi ta taɓe baki "yaya bamu gama game ɗin ba fa kuma momi bata zoba barre muci abincin"
hancinta ya lakkata "momi yau ba nan zata ci abinci ba kisan abbah yana nan g(me kuma gobe zamuyi tunda ba makaranta tashi muje"
tashi tayi yana rike da hannunta suka nufo dining saida yaja mata kujera ta zauna sannan shima ya zauna ya soma zuba mata abincin"
Siraj dai kallonsu kawai yakeyana cin abincinsa yana murmushi saida suka fara cin abincin sannan yace "yaya kasan momi tace ka daina ci mata abinci fa"
harara Qasin ya watsa mishi "tho momi ka gani nan ne"
rufe baki mairo tayi tana dariya "lahh yaya Allah sai na faɗa mata"
dariya Siraj yayi Qasin ya haɗe fuska
"kaga bana son iskancin nan fa Siraj ina ruwanka"
Siraj yace "gaskiya ce ai ace mutum da matarsa amman kullum sai yazo gurin momi yaci abinci"
banza Qasin yayi mishi ya cigaba da cin abincinshi,
Mairo kan dariya kawai take tana kallon Qasin.

can ta dafe ciki ta koma kuka kamar ba ita ba "na bani cikina ciyo yake"
duk suka kalleta Qasin yace "ciki kodan kinyi dariya ne?"
"a a tun safe yake min ciyo kuma sosai"
Siraj yace "kinsha

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login