Showing 27001 words to 30000 words out of 85263 words
Chapter 10 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt
mana hutu"
saida ya sauke ajiyar zuciya sannan yace "zanje Allah ya kaimu"
rawa ta rika masa "yauwa yaya na gode ina sonka sosai"
murmushi kawai ya shafa bayanta,
can ta ɗago "bari naje nayi shirin islamiya kar momi tayi faɗa"
kai ya ɗaga mata ta masa byebye ta nufi cikin gida da sauri.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*28*
Mairo na zaune parlour gaban tv tana buga game Siraj ya shigo,
da far ah ya karaso kusa da ita yana ya zauna,
kallonshi tayi taja tsaki ta matsa nesa dashi tana harararsa.
hannu ya kai ya kashe game ɗin ya ja mata hanci,
tashi tayi tsaye ta ɗauki fillon kujera ta rika buga mishi iyakar karfinta.
rikota yayi ya fisge fillon yayi ya jefar ya shiga kokuwar zaunar da ita,
daker ta zauna koshi dan ya rike mata hannayene haka ta rika kokuwar kuncewa ganin bazata iya bane yasa dole ta hakura ta zauna kurum,
bakinsa ya ɗora daidai kunneta yace
"plz maryam magana nake son muyi dake ta fahimta ba faɗa"
banza tayi masa ta kara turo baki ta ɗauke fuska.
murmushi yayi "haba my sis plz"
"tho ka faɗa mana ai kunne ne yake ji kuma ka sakeni"
sakinta yayi ta zauna daidai tana fuskartarsa "maryam kinga yau aka muku hutu kuma momi tace kauye zata kaiki dan Allah in kukaje karki yarda a baro ki kice ke bazaki zauna ba"
wani kallo tayi masa ta ɗaga baki sama "saboda mie?"
"kinga can ba daɗi kuma ba abinci mai kyau irin wannan ba gurin bachi mai kyau ba daɗi kinsan ai kauye ba daɗine dashi ba"
"nikan inaso a haks zan zauna har hutun mu ya kare inason naga gwaggo da tsoho da kawayena da kowa da kowa"
"oh maryam bazaki gane ba yanxu fa in kikaje can bazaki sake ganinmu ba sai anyi hutu"
tashi tayi tsaye "eh naji nidai ka kyaleni"
kallo ya bita dashi har ta haye stairs tana masa gunguni.
*_6:30pm..._*
momi na zaune ita da Usman,Nura da Mairo Qasin ya shigo da sallama,
da gudu mairo ta rumgumeshi tana murna momi bata kulashi ba Nura da Usman ne suka rika kallonsa har ya zauna,
gefensa Mairo ta zauna tana rike da hannunsa "yaya mi yasa ka daina zuwa nan gurin momi?"
shiru yayi yana kallon fuskar momi data ki ta kalleshi,
nan mairo ta sake jefa masa wata tambayar "kuma yaya ka daina cin abinci nn?"
sai a lokacin ya kalleta yana murmushi yace "aiki ne ya mun yawa bani da time ɗin kaina shiyasa kika daina ganina"
kai ta girgirza tana dariya,
juyawa yayi ya kalli momi "momi an wuni lafiya?"
amsa mishi tayi still bata kalleshi ba "lafiya kalau Qasin ya aiki?"
"Alhamdulillah"
bai sake cewa komai ba in banda wasa da yake da yatsun mairo momi ma ko kallonsa batayi ba barre ta sake ce masa wani abu,
suna haka aka kira sallar magariba haka ya sashi tashi yana kallon momi "bari naje nayi sallah an kira magariba"
sai a lokacin ta kalleshi "ka shirya ranar assabar zamuje kauye"
kai ya ɗaga "owk momi har da mansura"
"a a daga ni sai kai sai maryam zamuje"
"owk Allah ya kaimu"
"amin"
kallon su Usman yayi "ku ba zakuyi sallar bane?"
tashi sukayi ko wane na sosa kai suka nufi kofa, nn ya juyo gurin mairo "kema je kiyi sallah"
"tho"
da sauri ta tashi ta nufi stairs saida ta shige sannan ya maso kusa da momi ya risina hakan yasa momi ta kalleahi cikin sanyayyiyar murya yace "momi fushi kike dani ko?"
"mi zai sa nayi fushi dakai Qasin mi kayi min?"
shiru yayi yana kallonta kamar mai tunanon abunda zaice,
tashi momi tayi "nikan bari na shiga ciki nayi sallah"
bata tsaya jiran mi zai ceba ta nufi stairs saida yaga shigewarta sannan ya tashi ya fice.
*_washe gari..._*
tun 7am Qasin ya shigo part ɗin momi ya tare a parlour murna gurin mairo ba a magana haka ya sake jikinshi kamar ba shiba momi dai sai kallonshi take.
tare sukayi breakfast sai kusan 10am ya koma part ɗinsa bai daɗe ba ya fito cikin shiri ya yabar gidan.
da dare ma nan ya ci abinci ya rika jan momi da fira tun tana shareshi har ta gaji ta sake jiki, saida dare ya raba sannan yayi mata sallama ya nufi part ɗinshi,
haka Qasin ya rikayi duk wani bachin rai dake ransa dannesa yayi ya barshi a ranshi saidai duk lokacin daya kalli mairo sai yaji ba daɗi,
da sallama ya shigo kaya nuki nuki a hannunsa banci wa yanda Siraj da Usman suka riko,
gaban momi suka ɗire kayan nn da nn mairo ta shiga budewa "momi kayan waye?"
ɗan kwalin dake kanta Siraj ya cire yaja mata gashi saida tayi uhu,
da sauri Qasin ya kalleshi "kai mi yasa kake son mata keta haka ne?"
mairo ta watsa masa harara "mugune shi mai katon kai ai gobe ba zaka gannin ba"
murmushi yayi ya kalli momi yace "dan Allah momi karki baro ta"
shafa kanta momi tayi "a a can zan barota sai taga gari sannan a dawo da ita"
gwalo tayi masa tana masa rawar kai,
dariya Qasin yayi yace "gobe mirna gurin Gwaggo ba a magana"
momi tace "lallaikan an kwana biu ba a ga mairo ba"
rufe baki Siraj yayi "momi mairo kike ce fa"
"eh ai haka suke ce mata can kauye"
aiko nan ya hau kiran suna nata yana fashewa da dariya tun bata kulaba har ta soma tsarguwa ta tsuke baki "tho sai miye dan kace Mairo ai sunane haka ake kirana"
gwalo yayi mata "ai ba mairo yake ba mero yar kauye"
fashewa duk sukayi da dariya haka yasa ta haɗe fuska kamar ta fasa ta turo baki,
nn Qasin ya sake fashewa da wata dariyar yace "Siraj shi yasa ta raina ka ka cika mata shinshigi da yawa"
"ba shinshigi bane Allah mero ne sunan"
da fata momi tayi "ke kyalesu tashi kije ki kwanta kinsan gobe sammako zamuyi"
tasgi tayi kamar ta fasa kuka ta nufi daki.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*29*
*_washe gari..._*
koda 8am tayi mairo tayi shirin tafiya kasa yin breakfast tayi saboda murna ruwan tea kawai tasha ta tare saman kujera tana kallon su momi dake karyawa,
can taja tsaki ta kalli agogon dake hannunta "mts momi duk kun ɓata min lokaci har 9tayi"
juyowa Siraj yayi ya kalleta "eyye yar kauye an waye yanzu kin iya agogo ko mero?"
kawarda fuska tayi ta masa banza momi ta tashi tana faɗin "bari naje na shirya muje na kaiki gurin Gwaggo ki huta da matsalar Siraj"
kallonta Siraj yayi "momi dan Allah karki baro mana Maryam wlh miss ɗinta zamuyi"
kallonta kawai Qasin yayi ya kara kurɓa tea dake gabansa ya tashi ya fice,
mairo ta kalli momi "nidai kije ki shirya momi kar ki daɗe"
Usman yayi dariya yace "yau Maryam har gudun mu akayi ne dan zakije kauye"
Siraj kamar mai tsira ya hau tsokanarta "kaji fa wai kauye babu ma daɗin faɗin"
taɓe baki mairo tayi ta kalli momi "momi kije dan Allah ki shirya muje"
stairs momi ta nufa tana faɗin "tho yar gidan Gwaggo"
itama tashi tayi tana rufawa momi baya tana hararar Siraj,
*✧*
sha ɗaya da yan mintuna suka kama hanya,
mairo na front-seat Qasin na driving momi kuma a gidan baya surutu kan mairo shi tasawa gaba inta ɗauko wannan ya ɗauko wannan momi dai saurarenta kawai take inta kai gana dariya ba ta tamata saɓanin Qasin da fuskarsa take haɗe hankalinsa ma a wani gurin yake,
hannu Mairo takai ta taɓoshi da sauri ya kalleta "ya maryam mi kikace ne?"
murmushi tayi masa "bance komai ba naga dai kayi shirune baka magana kuma ka ɓata fuska"
sakin fuskar yayi "ina tunanin wani business nawa ne"
"tho ka ka daina haɗe fuska"
murmushi yayi yace "na daina Auntie"
dariya tayi ta kwanta tana kallon t-t,
motocin dake wucewa ta rika lisafawa har bachi ya ɗauketa.
'''*************'''
tsayawar da motar tayi da karfine yasa ta farka a figice tana rabon ido,
rana ne zagaye dasu sai tsalle suke suna ambatar mairo.
da sauri ta fita motar tana uhu suka shiga rumgumar juna ita dasu suna tsalle² ta gina wasu matan aure suka rika lekenta,
tuni momi da Qasin suka kunna kai cikin gidan,
ita kan saida suka gama ɓata mata kaya da kasa sannan ta shiga cikin gidan. da gudun ta karasa ta rumgume Gwaggo dake zaune saman tabarma tare dasu momi, idon Gwaggo cike da hawaye ta soma ture mairo "ni ɗagani ai guduwa kikayi kika barni"
kara rumgume tayi "Gwaggo ni ba guduwa nayi ba ai daman nace miki zan dawo kuma ba gashi na dawo ba ni babu inda zanje"
momi tayi murmushi tace "haba aiko duk kika kori mairo baki mata adalci ba dan kullum zancenki take ita dai Gwaggo ta dai"
Qasin yace "Gwaggo yar matsifa ke kullum matsifarki karuwa take ba raguwa ba"
nn Gwggo ta dawo kansa "eh ai daman kaine ka hure mata kunne tunda kazo taki ta samu matsuwa sai ta biku"
dariya yayi "tho Gwaggo ba gata yanxu mun dawo da ita ba da nan fa da can duk ɗaya ne tunda duk abu ɗaya ne"
momi ta karɓa masa "duɓe ta ki gani na gyare miki ita ta zama yar zamani"
gaban Gwaggo mairo ta dawo tana jujjuyawa kamin ta fashe da dariya ta faɗa jikinta ta rumgumeta,
*_two hours letter..._*
"kingani ko Gwaggo mairo ta sami lafiya ai daman nasan cikin biu sai anyi ɗaya kodai a maidota dan mugun halinta ko kuma ta chanja hali"
Halilu ne ke maganar yana kai lomomin shinkafs da wake bakinsa,
taɓe bag Gwaggo tayi "ai daman ba wani mugun haline da ita ba kaine dai ka bi ka matsa mata"
halilu yayi dariya yace "Allah Gwaggo in zaki faɗi gaskiya kema kinsan mairo ta chanja jifa har take bari yaran na su taɓa ta inda ne ai basu isaba ballan tana ma ta dawo daga birni"
"gaskiya kan ya gashi yanzu har girma maryam tayi kuma tayi hankali"
maganar momi take tana kallon fuskar Gwaggo,
Gwaggo ta taɓe baki "ai dole tun Allah kaɗai yasan hawalar da kuke gwada mata ai duk abunda zai sa mairo ta zama haka ba karamin abu bane"
Halilu ya tashi yana faɗin "Gwaggo ai ba zasu dai yi mata abunda kike nufi ba"
momi tace "ai muna zuwa duk wani abu da tasan bana Gwarai bane zubarwa tayi kuma muka saka ta a makaranta"
juyowa Halilu yayi da far'ah "harda makaranta kuka saka ta momi gaske dai ta kara chanja wa tayi kyau yanzu"
dariya momi tayi "kaji Halilu shi boko har sawa yake mutun yayi kyau?"
"Allah kuwa momi kinga ai yanzu ta natsu kuma ta waye ba kamar daba daman burina kenan naga mairo a makaranta kuma cikin rayuwar jindaɗi"
harara Gwaggo ta watsa masa "kuma can da kake dukanta?"
"yau ai saboda bata jin maganane shiyasa kuma kinga dan ta dainane ake mata haka"
"hmm tho chanjawa tayi ne ai babu irin dukan da bata a hannunka ba"
dariya yayi ya aje kwanon dake hannunsa "ai ba zaki gane ba Gwaggo ni dai bari naje Qasin na jirana mu zaga gari"
momi ta kalleshi "kar kuyi nisa halilu yanzu zamu je gidan tsoho mu koma gida dan ba daɗewa zamuyi ba"
"tho momi bari na faɗa masa"
hannunsa ya ɗauraye bayan yasha ruwa ya kurkure baki ya fice.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*30*
momi ta kalli Gwaggo tace "wai halilu ya daina karantun da yaje ne"
"wane karatu?"
"ba nasan da yana zuwa can sokoto gurin karatu ba"
Gwaggo ta taɓe baki "karatu kan ai yasha kashi tunda babu kuɗin karasawa"
"ayyah haba nijan kasan yana karatu a da digiri yake ne ko mie?"
"karki tambayeni ni sanin nayi yadda abun yake ne can dai su suka sani"
dariya momi tayi tana gyara ɗaurin ɗan kwalinta,
abincin dake gaban momi Gwaggo ta kalla tace "kema bazaki ci abincin ba ko Qasin ma yace ba zai ciba ku yan birni baza kuci na kauye ba"
"a a aini kinfi kowa sanin ba haka nake ba tun kamin mu baro gida saida muka ci abinci kuma ni bama abincin ne a gaba na ba"
"ko a siyo miki wani abun ne kici?"
"a'a ai inason shinkafa da wake ni wata magana nake son muyi dake Gwaggo"
kara juyowa Gwaggo tayi tana fuskarta "wace magana ce hauwa?"
"cewa nayi wai mi zai hana ayi haɗin gida"
"haɗin gida kamar ya kiɓfito kiyi magana tunda ba kunyata kike jiba kuma ba bakuwarki nake ba"
dariya momi tayi ta matso kusa da Gwaggo "ina nufi auren gida a haɗa Maryam da Qasin"
faɗaɗa fuskar Gwaggo tayi da far'ah "masha Allahu hauwa kin kawo magana daman abunda aketa magana kena a gari wai mun bayarda mairo can birni dan kwaɗayi mamakon muyi mata aure ai kara lalacewa zatayi magagganu kalakala babu daɗin ji
shekaran jiya fa tsoho yake cewa shidai cewa zaiyi a maido da mairo ya huta har nace nidai ba zanyi magana ba indai ba garin kukazo"
dariya momi ta girgiza kai "ai koda man munce fushine kikeyi"
"ai babu yadda halilu bai yiba kan yaje ya ganota na hana amman gaskiya naji daɗin maganar nan kin kawo shawara tho amman kunyi magana da Alhaji?"
"da haɗin bakinsa nake wannan maganar saida muka tattauna komai dashi kuma ya aminci shi da kanshi yace in nazo nayi miki magana ke kuma kiyiwa tsoho magana kinga duk yadda kukayi in muka dawo sai muji"
"tho insha Allah haka za'ayi abu mai sauki"
sosai momi ta jidaɗi dan batayi zaton zata samu goyon bayan Gwaggo ba,
abincin taja ta fara ci suna fira da Gwaggo, daf da zata kare Qasin ya shigo tare halilu.
zaunawa yayi kusa da ita yana kallon agogon hannunasa yace "momi tashi muje gurin tsoho so nake muje gida da wuri mansura tace nayi baki"
banza momi ta masa saida ta gama cin abincin sannan ta tashi suka nufi gidan tsoho,
''' * * * '''
sai bayan la'asar suka dawo gidan Gwaggo har lokacin mairo bata dawo gida ba,
sosai momi taso ta ganin mairo kamin su wuce.
amman ba dama dan halilu yayi nemanta har ya gaji baiga inda ta shiga ba, haka yasa dole momi tayiwa Gwaggo sallama. godiya Gwaggo tayi ta musu ita da halilu suna ɗsgs musu hannu har suka daina hango su,
sannan suka koma cikin gida.
kuɗi halilu ya ciro aljigunsa ya mikawa Gwaggo "ga naki kason"
da far'ah ta karɓa "yayi ɗan albarka abun ya samu"
yana dariya yace "Qasin ne ya bani ɗazun da muka fita"
zaunawa Gwaggo tayi tana faɗin "ai yaron nan yana da albarka wlh shiyasa ni na jidaɗi sosai da haɗin auren na da za'ayi shida mairo"
faɗuwa gaban halilu yayi nn da nn yanayin fuskarsa ya chanja tsigar jikinshi ta tashi a kasali ya kalli Gwaggo yace "aure za a haɗa mairo da Qasin?"
"eh abunda muka tattins da hauwa kenan kuma alhaji ne ya aikota yace a faɗawa tsoho kuma ni wlh nafi kowa farinciki wannan abun da za ayi ksgs ms mun huta da tsegumin mutane-"
da karfi halilu ya haɗeye yawu duk sai yaji maganar ta cika masa kunne, ya juya jiki ba gwari ya nufi kofa, kallo Gwaggo ts bishi dashi baki sake har ya fice,
tsaki taja ta taɓe baki "ai daman kai bason mairo kake ba kafison ka rika gwada mata azaba kamar haihuwarta"
'''***************'''
cikin dare su momi suka shiga sokoto _Rahama Restaurant_ momi tasa Qasin ya biya sukayo takeaway sannan suka iso gida,
Qasin nayin parking ya nufi part ɗinsa, momi ma a gajiye ta nufi nata part ɗin,
*_washe gari..._*
sai kusan 10 momi ta kare haɗa breakfast saboda gajiyan tafiyar jiya gashi kuma mairo maitaimaka mata bata nan,
Nura ne ya taimaka mata gurin jera abincin a dining, Usman yayi dariya "ayyoh Allah momi har nayi miss ɗin mairo"
momi na shirin zaunawa tace "ai nice nayi miss ɗinta yanzu haka ita nake tunani aikin nan duk sai naga yayi min wata kala"
Qasin yayi murmushi "ai momi ko ita sai tayi miss ɗinki balle ma can da nan ai ba ɗaya ba"
Siraj ya kalli momi "Allah momi da ba dan wani abu ba dasai nace Allah ya kara ai saida nace karki barota kika ki ɗaukar shawara ta"
"ai dole na barota wata nawa bata ga gida ba sai yanzu bamabfa shi kaɗai ya kaini ba"
Siraj yace "tho miya kaiki momi?"
tana buɗe marfin filas tace "auren maryam naje nemawa Qasin..."
kamar daga ssma sukaji maganar da sauri Qasin ya tashi tsaye yana kallonta
Usman da Nura ma duk ita suke kallo Siraj baisan lokacin daya saki tea cup ɗin dake hannunshi ba.
*©Khadeeja Candy*
[11/9, 6:54 AM] Khadeeja Candy: candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*31*
"aure fa kika ce momi?"
Siraj ne yake maganar yana mata wani kallon rashin fahimta,
murmushi momi tayi "aure mana miye abun tada hankali a ciki?"
Qasin da tun ɗaxu ya kasa fahimtar ta yace "kamar ya momi nifa naji kin anbata?"
ɗago kai momi tayi ta kalleshi "eh kai na nemawa inason ka auri Maryam ne"
a hankali ya zauna yana kallonta "saboda mi momi nifa ban fahimta ba?"
"bari mu gama cin abinci sai muyi magana"
juyawa tayi gurin Siraj "zauna mana Siraj"
zaunawa yayi yana kallon wainar kwan dake gabansa momi ta sake haɗa masa wani tea ta mika masa,
Qasin kasa cin komai yayi shidai moni kawai yake kallo zuciyarsa cike da tambayoyi,
Siraj ma cin abinci kawai ba dan yana jidaɗinsa ba
wayarsa nayin ringing kamar mai jira yayi sauri tashi tsaye ya ciro ta a jihu ya kara a kunne ya fice,
momi saida ta kare cin abincin tsaf sannan ta tashi ta nufi stairs ko minti uku ba tayi ba Qasin ya rufa mata baya,
gefen gado ya samu ya zauna yana kallon momi dake tsaye gaban madubi yace "momi kefa nake saurare nama kasa fahimtar abun kike nufi?"
zaman kujerar mirrow momi ta zauna "kasan me nake nufi Qasin auren maryam nake so kayi"
"saboda mie momi?"
"saboda inason ka kara aure"
"ban gane na kara aure ba mansura fa momi?"
"mansura ba mata bace Qasin so nake ka auri matar da zaka san kayi aure kasan waye kai"
kai ya girgiza "momi ni ban shirya kara aure yanzu ba haba momi ni bazan iya zama da mata sama da ɗaya ba"
leme baki momi tayi
"soboda mi baka san macce hudu Allah ya halitta maka aure ba?"
"na sani momi amman gaskiya ni ban shirya kara aure yanzu ba"
momi tace "ban fahimceka ba Qasin baza iya ba kamar ya?"
shiru yayi ya maida dubansa wani gurin fuskarsa ɗauke da damuwa,
ido momi ta tsura masa tana jiran amsar da zai bata.
ganin bashida niyar magana yasa tace "ina saurarenka faɗamin dalilinka?"
juyowa yayi ya kalleta "momi da wane ido zan kalli mansura bama zata fahimta ba momi inma gwadanine kike dan Allah ki daina"
"mansura..." momi ta faɗa "itace ta faɗo maka a rai ko baka kada wata matsala