Showing 33001 words to 36000 words out of 85263 words

Chapter 12 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt

04 Apr 2026

895

maganar da hajiya tazo da ita dan Hajiya ba tada wani farinciki sai na yarima taya zata yarda Qasin ya aureta ga yarima in kuma ta yarda Yarima ya aureta rigima ce ba yar kaɗan,
kai ta dake ta zauna gefen gado _...oh ni mi yasa ban faɗawa hajiya anyiwa maryam miji ba..._ sai yanzu take jin haushin,
_...amman kuma in har taji Qasin ne ai zata iya cewa ya barwa Yarima kuma gashi har na rig na faɗa a kauye Qasin yana sonta yanzu kums si sai su ga ɓayi musu magana biu..._ busarda iskar bakinta tayi ta lumshe ido.

*_© Khadeeja Candy_*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*35*

*_washe gari..._*
_10:47am_ Qasin ya shigo part ďin momi zauna ya tararda ita a dining area,
a kujerar daya saba zama ya zauna yana kallonta "momi ina kwana?"
a hankali ta kalleshi kana ganin fuskarsa kasam tana ďauke da damuwa "lafiya kalau ka tashi?"
"eh momi ke kaďai kike karyawa?"
"a a duk sun karya sun tafi makaranta ne kai ka daina karyawa nan ko?"
ďauke fuska yayi ya ďauko wani zancen "momi ya maganar tafiyar so nake na kaiki sannan na wuce dan yau zan wuni busy"
tea momi ta k'urɓa tace "ai tazo tun jiya"
kallon mamaki yayi mata "nan gidan laifiya dai ko?"
"lafiya kalau wata magana mukayi"
"tame momi?"
"sirrice"
"kamarbya momi nasan duk abunda zai sa Hajiya tazo gidanna ba karami bane dan Allah ki faɗa min minene kodai wani abun aka cene?"
momi bata ce masa komai ba ta tsura masa har tsargu ya tashi dan kanshi ya nufi kofa da tunane²
"Qasin..." murya kasa² momi ta kirashi da sairi ya juyo ya dawo "gani momi"
"ka faɗawa matar maganar aurenka?"
kasa yayi da kansa ya daɗe kamin ya bata amsa "a a momi ina tsoron abunda zai biyo baya ne kinsan ba fahimta zatayi ba"
ajiyar zuciya momi ta saike tace "yayi kyau zaka iya tafiya"
kallonta yayi kamar yace wani abu sai kuma ya juya ya fice,
dafe kai momi tayi tana nemawa kanta mafita sa kusan minti 30 haka sannan ta tashi ta nufi stairs,


''' * * * '''
kusan isha'i Siraj ya shigo part ďin momi ganin ba kowa parlour yasa kai tsaye ya wuce ďakinta, zaune ya tararda ita ta rafka uban tagumi tana kallon windo,
"lafiya momi?"
a sanyaye ta kalleshi da murmushin karfin hali "lafiya kalau Siraj ka shigo"
yana k'ok'arin zaunawa kusa da ita yace "momi gaskiya ba lafiya ba dan tunda safe naga damuwa a fuskarki akwai abunda yake damunki momi"
batace komai ba ta sauke ajiyar zuciya ganin haka yasa yace "barin kashi a ciki baya maganin yunwa momi babu kuma wadda ya dace ki fafawsa sirrinki irina hankalina bazai taɓa kwanciya ba momi matukar naki bai kwanta ba dan Allah ki faɗamin abunda ƴake damunki"
kallonshi tayi "kona faɗa maka Siraj ba magani zaka mun ba"
"naji nidai dan Allah ki faɗamin momi indai ba so kike nima na shiga damuwa ba"
momi ba dan taso ba ta fayyace masa komai,
Siraj ya daďe yana jinjina al'amarin kamin ya kalleta yace "yanzu momi mi kike gani shine fita?"
"nima ban saniba Siraj ita nake ta nema na kuma kasa samu"
Siraj yace "tho momi ga wata shawara..."
kallonshi momi tayi "ina jinka"
"momi mi zai hana kik'i yarda Qasin ko Yarima ya aureta"
"saboda mi?"
juyo yayi yadda zata fuskanceshi da kyau yace "kinga yanzu in kika bari Qasin ya aureta Yarima zai yita ganin laifinki shida mahaifiyarshi kuma otama zata taga kin mata cin fuska kinki bari Yarima ya aure kika bawa Qasin ya yaje ɗanki kimsan Hajiya bata tada wani Farinciki sai na Yarima tunda shi kaɗai ta haifa zata iya ɓatawala da kowa akansa kinga in kika mata haka ba zata taɓa mantawa dake ba kuma kinga zata ga baki tashi aurawa Qasin ita ba har saida Yarima ya ganeta yace yana so tunda baki riga kin faɗa mata kin nema masa ita ba kuma itama ba ganewa zata yiba sannan kinga shima yaya sai naga kamar bayason maryam sosai kuma kinga yana kaunar matarsa ko auren maryam yayi za suyita samun matsala,
in kuma kika yarda Yarima ya aureta nan ma baki tsira ba dan kinsan yaya bazai taɓa yarda ba kuma nima bazan yarda ki aura masa ita ba dan zai iya musguna mata kodam ganin daga falinmu take kuma kodan muji haushi zai iya yi mata hakan koda yana sonta dan kinsan halin Yarima ishesshen kanshine ko yanzu baki san dalilin da yasa yace sai ita kaɗai yake so ba tunda akwai yan mata da yawa a garinnna kuma suna sonsa dan babu wadda zaice yana so ta kishi kodan dukiyarsa balle ga mulki ga kyau amman ya nace shi sai maryam bakisan abunda yake shiryawa ba kuma kinga duk ya cuceta mudai ba kyalewa zamuyiba kauye kuma dake za suyi kuka dan haka ni abunda nake ganin mafita shine kawai ki bari can kauye ayi mata aurenta duk wadda suka ga damar haɗa shi da ita sai su aura mata"
gyara zama momi tayi tana nazarin kalamansa,
"ka kawo shawara Siraj amman kuma har yanzu da saura in har haka ta faru ita hajiya mi zan ce mata suma kauye dana riga nace Qasin na sonta ya zance musu har yanzu da sauran rina a kaba"
murmushi yayi "no momi kawai ki samu baba ku tattauna sai a warwar zancen auren Qasin ni da kaina zan kaiki kauye in yaso sai kice musu daman bakiyi shawara da Qasin ba kuma yanzu yaji bai amintaba kuma matarsa yar matsiface dan haka kina tsoron abunda zaije ya dawo dan haka a bar zancen aure kawai duk wadda suka dama su aura mata ita kuma hajiya in kika dawo saiki faɗa mata an riga anyiwa maryam miji alkawarine tun tana karama dan haka iyaye sunce bazasu tada ba koda tace ki kaita kauyen karki yarda kikaita dan zata iya zuwa ta rokesu ta nuna musu kuɗin koma shi Yarima da kanshi dan a yarda a aura mishi kuma kinga ko aura mishi ita akayi wahala zata sha dan kinga karamar yarinya ce sannan ba wani tsayawa zai kikayi yana bata hakkinta ba kuma zai iya ganinta tankar kaunarsa koma yarsa da ta masa abu ya daketa koma karki faɗa masu har sai an ɗaura aure, kawai momi wannan shine abunda nafa ya dace kiyi"
murmushin jindaďi momi tayi ta shafa kansa "ka kawo shawara Siraj haka zanyi Allah yayi maka Albarka"
shima murmushin yayi yace "amin momi shikenan damuwa ta wuce ko?"
kai momi ta ɗaga masa ya tashi tsaye yana faɗin "tho muje kici abinci dan nasan bakici abincin dare ba"
"jeka gani na zuwa"
"owk"
juyawa yayi ya fice cike da farinciki.

*_©Khadeeja Candy_*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*36*

A waya Momi ta kira Abbah sukayi magana dan kasa hak'uri tayi ganin ta samu mafita sosai yaso ta bari har ya dawo suje tare amman tak'i dan yadda Hajiya ta matsa mata kullum cikin kiran wayarta take,
ranar alhamis tun da safe Siraj ya fitarda motar da zasu shiga suna karyawa suka kama hanya,

*_K'auye..._*
ajiyar zuciya Gwaggo ta sauke tace "wannan magana ai kamar anyi sara akan gaɓa ne"
Momi tayi mata kallon rashin fahimta "mi kike nufi wani abun ne?"
Gwaggo tace "akan maganar nan ne wai Halilu yanzu ya fito wai sonta yake bai tashi magana ba saida yaga anyi wannan maganar kiji mun rainin hankali"
Momi ta rik'e baki "yanzu Halilun ne yace haka?"
Gwaggo tace "ai kuma baki san wani abun haushi ba wlh tsoho yayi tsaye shi sai Halilu zai aurawa"
"amman tsoho yaji da Qasin ne ake son haɗa auren?"
"wlh yaji kinsan matsalar da aka samu? ya rigani zuwa yayi magana dan ni a yadda na yanke sai an ɗan kwana biu kusan zata koma sannan nsyi maganar kinga koma minene amsar in kukaje sai kuji aiko yana jin haka sai kawai yaje ya faɗawa tsoho wai shi sonta yake ni kuma da naji haka sai naje nima nace ga abunda kike ce aiko tsoho k'in yarda yayi ya dinga ganin laifi yace nice nake son juyarda abun haka ai da kunso shi zaku samu kuyiwa magana ba niba wai shi daman yana son ya haɗasu amman yana tsoho amman yanzu tunda har haka ta faru shikena ta kwana gidan sauki shi Halilu zai bawa babu yadda banyi ba amman yayi tsaye shi lallai sai Halilu balle nasan ya kwashi k'arya da gaskiya ya faɗa masa"
Momi tace "tho injin ita Maryam ɗin tana sonshi?"
"uhmmm aifa kinji inda matsalar take nan itakan tayi tsaye wlh bata sonshi yanxu haka in kikayi mata maganar kuka zatayi"
"dank'ari aiko akwai matsala tho ba'a faɗawa tsoho bata soba?"
"hmm ai sai kiyi abunda tsoho yake nema ai shine ya tsaya kai da fata wai ko bata so sai anyi shi daman ya yanke shawarar aurarda ita dan ya gaji da tsegunmi mutane"
Momi tace "amman kuma Gwaggo ai naga kamar shi Halilun bashi da wata matsala"
"aiko shine da matsa nifa na rik'ashi tun yana k'arami yanzu haka ganin da kike masa baya noma tho ɗsn k'auye in baiyi noma ba mi zaiyi sannan babu sana'ah babu aikin fari babu ma bak'i in kinmai magana yace shi karatu zai bazai iya rayuwar k'auye ba kuma karatun nan bai wani yi zurfi ba balle ace aiki kuma ance aikin nan fa ko a can birni wahala yake tho ina wani abun k'aurai tunda babu abun ci da mata"
Momi ta jinjina kai zatayi magana taji an rumgumeta da karfi,
dariya tayi jin Mairo ce tace "tun ɗazu mukazo ban ganki kiba kina can gurin yawo ko?"
dariya Mairo tayi ta k'ara rumgume Momi "a'a Momi tunda kukazo naga Siraj yaje dani yawo sai yanzu muka dawo Momi nayi mesage ɗinki"
"missed ake cewa yar boko"
Gwaggo tayi dariya tace "haka muke da ita abu kaɗan sai turanci ita yar boko"
Momi ta juyo da ita ta zauna daidai "ina kukaje yawo wato kings shigowa amman da kiks gs Siraj sai kiks shareni ko?"
"a'a Momi yawo fa mukaje da mota ko'ina sai kallonmu ake"
ta karasa maganar tana wani marmarɗen ido,
Gwaggo tace "kin samu abunda kikeso ko kiyiwa mutane kuri tho ina kika baroshi ko ya sake fitane?"
"a'a waya yake yi yanzu zai shigo"
kallon Momi tayi "Momi kinci abinci?"
da murmushi Momi tace "a'a Gwaggo ki bata bamu ba amarya"
nan da nan Mairo ta ɓata fuska kamar ta fasa kuka "Momi bana so ki daina"
Momi ta dafata "ai dole kiso kedai tashi ki ɗauko mana abincin"
matsawa tayi gefen ta takure kanta ta haɗe rai, Siraj na shigowa ta rushe da kuka.
da sauri ya karaso kusa da ita "lafiya mi akayi mata"
Momi tace "wai dan nace mata amarya shine take kuka"
"kamar ya auren za'ayi mata ne?"
"eh Halilu za'a aura mata wai ita kuma bata sonshi"
murmushi yayi ya shiga tallaɓata yana bata hak'uri, daker ya samu tayi shiru ta tashi ta nufi ɗaki,
gurinsu Momi ya nufo yana faɗin "wai yanxu daga yin magana har anjuyarda abun zuwa ga Halilu?"
kamin ya zauna Momi tace "a'a daman rigimar da aketayi kenan wai shi sonta yake...................."
nan Momi ta labarta masa komai,
Sosai Siraj yayi mamaki ya kalli Gwaggo yace "mi yasa bakison auren Gwaggo? Halilu bashida hallin k'waraine hala?"
Gwaggo tace "a' wlh yana dashi nina rik'ashi tun yana k'arami gaskiya bashi da wani mugun hali"
Siraj yace "tho mi yasa bakison ya auri Maryam ni aganina ba wani abu bane kinga shima ai ɗan'uwane kuma duk duniya bana ganin akwai wadda ya dace ya aureta sama da shi kefa kika reneshi Gwaggo ya tashi a hannunki yanzu dan yace yana son Maryam in kikak'i baki ganin xai iya shiga damuwa? ni aganina koda ahi baiyi magana ba kema ya kamata ki haɗasu ballantana har yayi gaskiya Gwaggo in kikak'i goya masa baya baki masa adalciba kuma kin nuna masa ke bake kka hafeshi ba"
shiru Gwaggo tayi tana nazarin maganar.
"amman fa Sirajo ita Mairo bata sonshi fa"
"karma ki kawo wannan Gwaggo Maryam k'aramar yarinyace bata san soba ko a birni ksmar Maryam za'a iya aura mata wadda akaga dama balle k'auye kune kuke k'ara sa tana cewa bata sonshi kawai kibar ma wannan zancen inta girma gidansa a babu zance k'i"
dariya Gwaggo tayi "kuma fa haka ne Sirajo da maganar ka Allah dai ya zaɓa mana abunda yafi zama alkhari"
duk sukace 'amin'
Siraj yace "amman dai Gwaggo ba zaku raba ta da karantunta ba ko?"
Gwaggo ta leme baki "karatu kan ai yasha kashi tunda in an mata aure ai tarewa zatayi kaga ko babu zancen karatu"
"amman gaskiya Gwaggo ku barta tayi makarantar ta koda anyi auren ne inta k'are sai ta cigaba da zamanta na aure"
ido Gwaggo ta nuna masa "kaga nawa ni yanzu kuma fa ako auren akayi nan zatayi ta zama dan bashida gurin ajeta sai yayi gina"
shiru Siraj yayi ya nuce kai bai sake magana ba,
can Momi tace "wai ins wadda taje ɗauko mana abinci?"
Gwaggo tace "aifa sai kiyi bafa zata ɗauko ba da nan fushine take dake"
Momi tayi dariya "in banda abinki Maryam daga faɗar gaskiya sai cibi ya zama k'ari"
Gwaggo ta tashi ta nufi ɗaki tana faɗin "bari na ɗauko miki indai wannan ce saiki shekara"
tashi Siraj yayi "ni bari naje bakin kasuwa kamin ki k'are cin abinci"
"kai ba zaka ciba?"
"kai Momi kinsan ni kan bazan iya cin abincin nan ba bari dai naje can ko zan samu abunda zanci"
kai Momi ta ɗaga mishi ya saka hannayensa aljihu ya fice.

*_©Khadeeja Candy_*

candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*

*37*

kai tsaye Siraj bakin kasuwa ya nufa daman ɗazu da suka wuce ya hango gurinda Halilu yake zaune,
Halilu na hangoshi ya ɓata fuska aransa yana _babu wani magiya da zaka mun na barma ku ita wlh boko dai nima nayi dan haka baka fini wayeba_,
Siraj ya k'arasowa kusa dashi yayi masa sallama tare da mik'a masa hannu, ciki² ya karɓa ya juyarda fuska,
murmushi Siraj yayi ya zauna saman teburin da yake zaune yana faɗin "kai kaɗai kake zaune?"
"eh ina hutawane"
Siraj ya kalleshi "Halilu ka saki jikinka dani bana nufin cutarda kai ko cilas taka yin abunda baka tashi ba ni shawara nazo na baka kuma inason kayi nazari ka ɗauki shawarar karka kalleni a matsayen ɗan'uwan Qasin inason ka kalleni a matsayin ɗan'uwanka"
juyowa Halilu yayi ya kalleshi "wace shawarace?"
dafashi Siraj yayi yace "naji ance ka fito kana son Maryam ita kuma bata sonka kuma kaga yayana ma yana sonta banci shi kuma akwai wadda yake sonta can birni sannan naji ance baka kada sana'ah ba kama da gurin ajeta tho kuma yanzu naji tana zance sai ta bimu birni tho abunda nake so da kai shine kayi sauri ka matsa a ɗaura muku aure koda baka da gurin ajeta ɗin dan in kayi sake tho rasata zakayi kaga in ka aureta koda tace sai taje birrin kana iya kyaleta taje tayi karatunta amman fa da aurenka kaga kamin ta k'are kai kuma ka samu aiki kayi gidan ajeta ni zan iya taimaka maka ka cigaba da karatunka amman karka yarda wani sati yayi ba'a ɗaura maka aure da ita ba"
ido Halilu ya tsurawa Siraj yana son tantance abunda yake faɗa,
_ta yaya zai yi masa wannan shawarar bayan shi ɗan'uwan Qasin ne miyasa yake son shi ya aureta sama da Qasin can wata zuciyar tace amman kuma fa gaskiya ya faɗa min tunda banida gurin ajeta balle abun ciyarda ita kuma nasan yanzu Mairo bazata yarda ta zauna k'auyen nan ba tunda nama ji ta fara zancen sai ta bisu kuma gashi har yace zai taimaka min na k'arasa karatuna inhar da gaske yake kuma fa inna aureta na huta koda taje can birrin wani ya ganta yana so na dai riga na aureta......_
dafashi da Siraj yayi yasashi dawowa daga duniyar tunanin daya tafi,
Siraj yace "ka yarda da shawarata Halilu shine kawai mafita a gareka"
ajiyar zuciyar Halilu ya sauke yace "maganganunka abun dubawa ne Siraj saidai na kasa ganewa taya zaka goya mun baya na auri Mairo bayan yayanka ma yana sonta?"
murmushi Siraj yayi yace "shiyasa tun farko nace karka ɗaukeni a'matsayen ɗan'uwan Siraj ka ɗaukeni a'matsayin ɗan'uwanka Halilu bana nufi cuta a gareka nayi haka ne saboda shi Qasin yana da mata sannan kuma zuwan da Maryam tayi birni ne ya ganta yace yana so saɓanin kai da tun tana k'arama kake sonta ko ɗazu na faɗawa Gwaggo babu wadda ya dace da Maryam irinka,
Halilu nifa bance dole ka ɗauki shawarta ba kawai in tayi maka shikenan in kuma batayi maka ba duk ɗaya ne"
ya karasa maganar tare da tashi tsaye. Hannu halilu ya mik'a masa "na gode sosai Siraj zanyi tunani a kai"
"nima na gode da bani lokacinka da kayi Allah ya shige mana gaba"
nan sukayi sallama Siraj ya nufo gida,

''' * * * '''
bakin k'ofa ya tararda Mairo zaune rik'e da ɗan karenta tana zane a k'asa,
da murmushi ya fito motar ya nufota, saida ya kusa kawowa kusa da ita sannan ta ɗago ta kalleshi ta wani turo baki wai ita gamai fushi,
sai da ya zauna kusa da ita sannan yace "fushin mi kike Maryam?"
"wai Momi ce tace bazata je dani birni ba"
"tho ai hutunku bai k'areba kuma kinga aure za'ayi miki babu ma zancen komawa birni gaba ɗaya rayuwarki ta dawo nan kenan"
da sauri ta kalleshi "ni wlh ba zan zauna ba kuma ni bana son aure wlh bana son halilu"
da kuka ta k'arasa maganar,
saida Siraj ya duba yaga babu mai kallonsu sannan yace "in baki shawara?"
kai ta ɗaga mishi
yace "karki yarda a aura miki Halilu kinga ɗan k'auyene kuma duk wani abun daɗi da kikasan kinaci da kin aureshi kin daina cinsa kenan kuma kings babu ke babu karatu babu zuwa birni nan zakiyi ta zama kina daka da zuwa daji kina ɗebo kara shikenan kinyi bankwana da jindaɗi muma ba zaki sake ganinmu ba har Momi"
k'ara fashewa tayi da kuka da sauri ya rufe mata baki yana kallon k'ofa "shinnnnn kar sujiki kina son na baki wata shawara?"
nan ma kan ta ɗaga yace "koda an ɗaura miki aure da Halilu karki yarda ki zauna kice ke gurin mu kikeso kiyi ta musu kuka kice kesai an barki kinyi karatu in kikayi haka nasan za'a iya barinki ki bimu amman inba haka ba shikenan ba zaki k'ara jindaɗi ba kinji"
cikin muryar kuka tace "tho Gwaggo zanyiwa ko tsoho?"
"dukansu har Halilu kice indai yana sonki yabarki kije kiyi ta musu kuka kina murje² in kikaga sunk'i yarda sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login