Showing 57001 words to 60000 words out of 85263 words

Chapter 20 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt

04 Apr 2026

906

cikin wani hali abin tausayawa gaskiya kayi abu mai kyau kuma ina goyon bayanka ɗari bisa ɗari"
Daɗi sosai Qasin yaji ɗago kai yayi ya kalli Abbah "Nima Abbah tausayi take bani sosai hakan yasa na yanke shawarar aurenta n dawo da ita kodan zaman da take son yi tare damu"
"Gaskiya ne naji daɗin wannan shawarar da kayi Allah ya taimaka"
"Amin. amman fa Abbah kai nake so ka nema min Auren"
Ya faɗa yana ɗan sosa kai.
Abbah yayi dariya "Toh In'sha Allahu zan samu lokaci kamin naje Abuja saina je can k'auyen"
Godiya sosai Qasin yayi mishi sannan ya tashi ya fice.

Goma da mintuna ya kare shirin shi tsaf na fita office. laptop ɗinshi ya ɗauka tare keys ya nufi parking space.
"Yaya" Gudu Nura ya k'araso gurin yana faɗin "Yaya Momi na kiran ka"
Faɗuwa gabanshi yayi ajiyar zuciya ya sauke "je kace gani nan tafe"
Kai ya ɗaga mishi "Okey" ya juya ya bar gurin.
Saida ya buɗe Motar ya saka laptop ɗinshi sannan ya rufe ya nufi part ɗinta.
Bai tararda ita parlor ba hakan yasa ya nufi up stairs.
"Gani nan Qasin"
Juyowa yayi ya kalli dining inda yaji muryar Momi tare da nufar gurin.
Kujerar dake facing ɗin nata yaja ya zauna "Momi gani Nura yace kina nema na"
Shiru tayi har na wani lokacin sannan ta kalleshi ta soma magana "Qasin dan nace bazan nema maka auren Maryam ba shine kaje ka samu Abbah ka da maganar ?"
Ajiyar zuciya ya sauke "Momi toh naga babu yadda zanyi ne tunda babu wadda ya dace ya nema min auren nan sai ku ke kuma kince bazaki nema min ba baki ma bani goyon baya ba"
"Saboda mi zan goya maka baya Qasin kayi abin da gaba ba zamu jidaɗin shi ba"
"Saboda mi zai zamo abin rashin jindaɗi aciki ba cutar da ita zanyi ba Momi kuma naga kema fa kinason nayi nima kaina ina buk'atar auren nan toh minene abin rashin jindaɗi aciki"
"Qasin abunda nake son ka gane shine. Duk auren da akayi babu so toh yana da wahala auren ya ɗore ba son yarinyar nan kake ba kuma kaga matarka ba hali ne da ita ba zata iya cutar da ita kuma kaga yarinyar nan marainiyace ba Uwa a Uba bata da wani gata sai na Allah"
Murmushi yayi "Momi in dai har wannan ne matsalarki ko kuma abinda yake damunki toh ki kwantarda hankalinki In'sha Allahu hakan ba zai faru ba"
Momi ta ɗan motsa baki tayi mishi kallon manya "Amman mi yasa can baya baka nemi aurenta ba sai yanzu ? Alhalin saida na taya maka auren nata tun farko ?"
Agogon hannunshi ya duba ya tashi yana faɗin "Momi bari naje kar nayi latti" Bata ce mishi uffan ba shima bai jira mi zata ce ba ya fice.

*3:45 pm...*

Ya shigo gida ɗakin shi ya wuce bayan yayi wanka ya sake shiryawa ya nufo parlor.
Zaman doguwar kujera ya zauna ya kai hannu ya ɗauki remote ya chanja channel.
Murmushi yayi jin an shafa kanshi "Kin tashi ?"
"Waya ce maka bachi nake?"
"Ai nasan shi kike yi tun fa ɗazun na shigo na fa har nayi wanka banji motsinki ba"
Zagayowa tayi ta zauna kusa dashi. "Na barka ne ka ɗan huta tukuna tashi muje kaci abinci"
Cikinshi ya shafa "A k'oshe nake"
"Taf ai baka fara ba na dagargaje nayi maka girki kace kai a koshe kake"
"Toh ai kin riga kin saba min da cin abinci a waje ne"
"Ni gaskiya sai kaci"
Ta faɗa tana ɓata fuska.
Kumatunta ya rik'a "To miye sirrin ne nayi min girki yanzu bayan baki saba yimun hakan ba"
"Ban saniba nidai kawai ka tashi muje kaci plz" Tashi yayi rik'e da hannunta suka nufi dining.


*© KHADEEJA CANDY*
[6:17PM, 3/23/2017] Khadeeja_ce👌: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

_INNALILLAHI WA'INA ILAIHI RAJI'UN._
_Yau ce Ranar da Mahaifina ya Cika shekara biu a cikin kabarinshi. Ya Allah ka haskaka mishi k'abarinshi ka faɗaɗa mishi ka yalwanta mishi ka haskaka mishi ka gafarta mishi ka sa Aljanna ce makomarshi ka zamo gatanshi ka isar mishi ka bishi da bishi da kyakkyawan halinshi._
_Hak'ik'a nayi Babban rashi Babban bango jigo na rayuwata kuma gata na farincikina Abin alfahari na mun shaku da dashi sosai sai gashi mutuwa tayi mana yankan k'auna a lokacin da bamuyi tsamani ba._
_Ya Allah ina rok'onka da kyawawan sunayenka. Ya Allah ka haɗa fuskata da ta Mahaifina a Aljanna Ya Allah ka gidana da nashi Aljanna domin shine mafi soyuwa a cikin rayuwa ta._
_nayi Babban rashi taɓonsa ba zai taɓa goguwa ba a cikina rayuwa ta har na koma ga Mahaliccina._
_Allah kayi mishi gata kamar yadda shima yayi mini._

_NA RASA GATA NA A DUNIYA WADDA BAYA SON KUKANA_😭😭😭😭😭😭


*53*

Saida Momi tayi ma Qasin tas. sannan ya tashi ya fice daga ɗakin ba tare da wata kalmar ta fita daga bakinshi ba.
Yasan dai duk abunda zai faɗa mata ba fahimta zatayi ba dan ba tsayawa zatayi ta saurare shi ba.

*WASHE GARI...*

Gurare tara da kwata Qasin ya samu Abbah ɗakin shi.
bayan sun gaisa ya nemi guri ya zauna ya noce kai Abbah na ganin haka yasan akwai magana a bakinshi.
"Lafiya Qasimu ?" Abbah ya tambaya yana kallon fuskarshi.
D'agowa yayi bayan ya sauke ajiyar zuciya "Abbah tunani nake yi akan Auren Maryam amman bazan yanke hukunci ba har sai naji abinda zaka ce"
Tashi Abbah yayi daga kishingiɗen da yake ya zauna "Wato tun rasuwar mijin. yarinyar nan ta soma bani tausayi.
kayi tunani mai kyau Qasimu ko babu komai daman ni inason Auren zumunci ballantana Maryam da take cikin wani hali abin tausayawa gaskiya kayi abu mai kyau kuma ina goyon bayanka ɗari bisa ɗari"
Daɗi sosai Qasin yaji ɗago kai yayi ya kalli Abbah "Nima Abbah tausayi take bani sosai hakan yasa na yanke shawarar aurenta n dawo da ita kodan zaman da take son yi tare damu"
"Gaskiya ne naji daɗin wannan shawarar da kayi Allah ya taimaka"
"Amin. amman fa Abbah kai nake so ka nema min Auren"
Ya faɗa yana ɗan sosa kai.
Abbah yayi dariya "Toh In'sha Allahu zan samu lokaci kamin naje Abuja saina je can k'auyen"
Godiya sosai Qasin yayi mishi sannan ya tashi ya fice.

Goma da mintuna ya kare shirin shi tsaf na fita office. laptop ɗinshi ya ɗauka tare keys ya nufi parking space.
"Yaya" Gudu Nura ya k'araso gurin yana faɗin "Yaya Momi na kiran ka"
Faɗuwa gabanshi yayi ajiyar zuciya ya sauke "je kace gani nan tafe"
Kai ya ɗaga mishi "Okey" ya juya ya bar gurin.
Saida ya buɗe Motar ya saka laptop ɗinshi sannan ya rufe ya nufi part ɗinta.
Bai tararda ita parlor ba hakan yasa ya nufi up stairs.
"Gani nan Qasin"
Juyowa yayi ya kalli dining inda yaji muryar Momi tare da nufar gurin.
Kujerar dake facing ɗin nata yaja ya zauna "Momi gani Nura yace kina nema na"
Shiru tayi har na wani lokacin sannan ta kalleshi ta soma magana "Qasin dan nace bazan nema maka auren Maryam ba shine kaje ka samu Abbah ka da maganar ?"
Ajiyar zuciya ya sauke "Momi toh naga babu yadda zanyi ne tunda babu wadda ya dace ya nema min auren nan sai ku ke kuma kince bazaki nema min ba baki ma bani goyon baya ba"
"Saboda mi zan goya maka baya Qasin kayi abin da gaba ba zamu jidaɗin shi ba"
"Saboda mi zai zamo abin rashin jindaɗi aciki ba cutar da ita zanyi ba Momi kuma naga kema fa kinason nayi nima kaina ina buk'atar auren nan toh minene abin rashin jindaɗi aciki"
"Qasin abunda nake son ka gane shine. Duk auren da akayi babu so toh yana da wahala auren ya ɗore ba son yarinyar nan kake ba kuma kaga matarka ba hali ne da ita ba zata iya cutar da ita kuma kaga yarinyar nan marainiyace ba Uwa a Uba bata da wani gata sai na Allah"
Murmushi yayi "Momi in dai har wannan ne matsalarki ko kuma abinda yake damunki toh ki kwantarda hankalinki In'sha Allahu hakan ba zai faru ba"
Momi ta ɗan motsa baki tayi mishi kallon manya "Amman mi yasa can baya baka nemi aurenta ba sai yanzu ? Alhalin saida na taya maka auren nata tun farko ?"
Agogon hannunshi ya duba ya tashi yana faɗin "Momi bari naje kar nayi latti" Bata ce mishi uffan ba shima bai jira mi zata ce ba ya fice.

*3:45 pm...*

Ya shigo gida ɗakin shi ya wuce bayan yayi wanka ya sake shiryawa ya nufo parlor.
Zaman doguwar kujera ya zauna ya kai hannu ya ɗauki remote ya chanja channel.
Murmushi yayi jin an shafa kanshi "Kin tashi ?"
"Waya ce maka bachi nake?"
"Ai nasan shi kike yi tun fa ɗazun na shigo na fa har nayi wanka banji motsinki ba"
Zagayowa tayi ta zauna kusa dashi. "Na barka ne ka ɗan huta tukuna tashi muje kaci abinci"
Cikinshi ya shafa "A k'oshe nake"
"Taf ai baka fara ba na dagargaje nayi maka girki kace kai a koshe kake"
"Toh ai kin riga kin saba min da cin abinci a waje ne"
"Ni gaskiya sai kaci"
Ta faɗa tana ɓata fuska.
Kumatunta ya rik'a "To miye sirrin ne nayi min girki yanzu bayan baki saba yimun hakan ba"
"Ban saniba nidai kawai ka tashi muje kaci plz" Tashi yayi rik'e da hannunta suka nufi dining.


*© KHADEEJA CANDY*
[9:17PM, 3/24/2017] Khadeeja_ce👌: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

_Godiya ta musamman ga Balkisu Ammani Chuchu and Ashnur Pyar na gode sosai Allah ya bar Zumunci ya kara haɗa kan mu yan NAGARTA WRITTER'S ASSOCIATION_
_Special thanks to All My Fan's, Friends, and some of my co-Writer's i appreciate your prayers oll_

_No words can express how happy I am when I received your call and messages. u mean so much to me. thank you for being there always. (ROSE OKKAFO rosy lurv) 😘_

_In dedication to PERFECT WOMAN'S, and CLASSIC LADIES. u are very kind Mrs Tijjani thanks for the love_.

*NOTE*
_Nayi kuskure a page ďina na baya wadda nayi kamin wannan instead of nasa *53* saina sake mamaita *52* ya zama nayi *52* so biu kenan. Dan haka wannan zai zama *54* the second *52* ya zama *53* hop Kun fahimta ?_.


*54*

Kujera taja mishi ya zauna, Sannan ta shiga zuba mishi abincin.
mamaki yayi sosai ganin kalar abinci har huɗu gasu pizza da cake.
Haka ta sashi gaba ta rik'a tura Mishi abincin saida yaci yayi naket. sannan ta tashi ta ɗauko wani dan k'aramin box ta mik'a mishi tana murmushi.
Karɓa yayi yana "Minene ?"
"Open it"
"Okey"
Ya faɗa yana ɗaga gira. Arba yayi da wani agogon hannu golden color mai kyau.
D'agowa yayi ya kalleta
"Na waye ?"
"Na kane kaina siyo ma"
ta bashi amsa still tana murmushi.
"Wai duka wannan mi yake nufi ne Mansura nifa ban gane ba ?"
Hannayenta ta ware
"As how don't tell me you forget about today ?"
"Today is Wednesday so what is..."
"Today is our Anniversary"
Ta tari numfashi shi tana ɗan zaro ido.
Hannu yasa ya rufe bakinshi "Oh Allah ni Wallahi kwata kwata na manta"
Wani kallo tayi mishi mai ɗauke da mamaki "Did you hear yourself ?"
"Yes. Toh tunda mukayi auren nan babu wani abin farinciki daya faru da har zaisa na iya rik'e ranar zagayowar haihuwar mu! Mansura tun... "
Shiru yayi ganin irin kallon da take mishi.
Kanshi ya shafa zuwa fuskarashi ya lumshe ido. Haka yaji maganar daya furta mata kamar tuɓul da baka.
"What are you saying Qasin ?"
Idonta cike da hawaye tayi mashi tambayar.
Girgiza kai yayi yana haɗiyar yawu.
"I mean you... you know i..."
Gargada muryarshi ta dinga yi yana tunanin abinda zai furta mata. sai wani juye juye yake da kai. ya gagara haɗa ido da ita.
Tashi tayi hawaye na mata zuba ta nufi ɗakinta.
Da sauri ya rufa mata baya yana kiranta "Mansura Mansura saurara kiji mana"
Da gudu ta k'arasa ta bankaɗo k'ofar da k'arfi.
Yana isa ya mika hannu zai buɗe yaji tasa key. Ajiyar zuciya ya sauke ya janye hannunshi daga jikin k'ofar.
Ya daɗe tsaye a gurin sannan ya juya ya nufi hanyar fita.

'''***'''

1:28pm. Abbah ya isa k'auye. kai tsaye massalacin juma'ar garin ya wuce ganin sauran mintuna kaɗan a tada sallar.
Bayan an taso daga masallacin ya nufi gidan tsoho.
Kusan awarshi biu cikin gidan sannan ya fito ya nufi gidan Gwaggo.
Yanayin sallama ta tarɓeshi da far'ah "Ah ah ah lale marhaban da mutanen birni yanzu ake tafe ?"
Dariya Abbah yayi "Toh tafiyar ce ta kama haka tun safe nazo nazo Allah bai nufa ba amman dai nan nayi sallar juma'ah"
Tabarma Gwaggo ta shimfiɗa mashi "Bari na shinfiɗa maka a nan ɗakin nan zafi Wallahi"
Bayan ya zauna ta ɗauko mishi furau furau da maheci (hand fan) ta mik'a mishi. "Karɓi ko wannan ka ɗan zage zafi abinci kan yanzu na ɗora.
ya hanya dasu Hajiya ?"
Abbah saida yasha ruwan sannan ya amsa mata
"Lafiya kalau kowa yake duk kuma suna gaisheki"
"Tob madallah yau lafiya akayi mana zuwa ba zata kuma kai kaɗai ?"
Abbah yayi murmushi.
"Lafiya kalau wani muhimmin abune ya kawo ni Maryam ?"
"Na aike ta nan mak'ota ta karɓo min surfe ince dai kasan ta fita wanka tun kwanaki ko ?"
"Eh na sani ai munso muzo yanayin aikin ne bai barmu ba ta fita lafiya dai ko ?"
"Ta fita lafiya kalau Alhamdulillahi mabi ɗa na nan sai tasowa suke har da abokanin margayi"
Da dariya ta k'arasa maganar. Abbah ya gyara zama shi "Masha Allahu toh ai nima yana ɗaya daga cikin abinda ya kawo ni"
"Na me ba ?" Gwaggo ta tambaya.
"Na neman auren Maryam"
Gwaggo ta k'ara matsowa "Toh ko wanine yace yana son ta ?"
"Eh ɗanki ne yake son in an bashi ita yayi ta biu"
"Qasin kake magana ?"
Gwaggo ta faɗa tana zaro ido.
"Eh shi fa kuma nayi magana da tsoho yace ya bashi yanzu sauran muji bakin yarinya"
Hannu Gwaggo ta ɗaga sama "Alhamdulillahi Allah na gode maka daka nuna min wannan rana amman na jindaɗi wannan lamari Allah ya tabbatar"
Abbah ma daɗi yaji "Ni nafiki jindaɗi dan tun zamanta na farko mukaso ayi abun Allah bai nufa ba"
Fuskarshi shinfiɗe da murmushi yayi maganar.
"Daman ni kullum fatana Allah ya zaɓa mata miji na gari inda zata jidaɗi. kuma Kaga ko shekaran jiya saida tayi maganar birnin nan tana son zama gurinku sosai. Allah dai ya yarda mude mun aminta ba wata matsa Wallahi" Faɗar Gwaggo.
"Haka ne amman yanzu sai munji ta bakinta idan tana sonshi tunda yanzu ba kamar baya bane kuma Annabi (S. A. W) yace a nemi izinin mace kamin a aurar da ita toh kinga ba mu sani ba ko akwai wadda take so"
"A'a babu wani wadda take so Mairo ma wani so ta sanine tun can baya ma da tana da yar hayaniyarta ballantana yanzu da ta koma shushushu ai babu wani abu tunda dai har yace yana son ta"
Abbah ya girgiza kai "A'a baza fa ayi haka ba sai naji rayinta tukuna yanzu dai aika a kiramin ita"
"Oh toh tunda ka matsa bari na aika a kirata" Tashi tayi tana faɗin "Bari na ɗauko mayafina na aiki haruna".

_PROUD OF YOU Miss S-S_😘

*© KHADEEJA CANDY*
[2:41PM, 3/27/2017] Khadeeja_ce👌: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

*55*

Da far'ah Mairo ta shigo cike da ladabi ta k'araso kusa da Abbah ta risina.
"Abbah ina wuni?"
Da murmushi Abbah ya amsa "Lafiya kalau Maryam barka da fita wanka"
"Yauwa Abbah yanzu ka zo? Yasu Momi?"
"Lafiya kalau suke suna gaishe ki kuma suna miki barka da fita wanka"
"Ina amsawa Abbah ina Siraj?"
"Yana can gida am.. Maryam" Ta ɗaga kai ta amsa "Na'am Abbah"
"Jeki waje kice ma direba ya baki jika tana nan cikin Mota ki kawo"
"Toh Abbah" Tashi tayi ta fita.
Bayan yan mintuna ta shigo rik'e da *BABBAR JAKA* ta aje mishi gabanshi
"Abbah gashi"
Abbah yasa hannu aljihu ya ciro kuɗi masu ɗan dama ya ɗora saman jakar.
"Am...Maryam wannan kuɗin da kayan da kika gani na neman aurekin ne Qasin ya aiko yana son idan an Amince mishi kizo a matarshi ta biu"
Da sauri ta nuna kanta "Abbah ni?" Ta tambaya tana zaro ido. Abbah ya gyara zamanshi "Eh kefa Maryam amman fa ba cilas bane shima ya saka kanshi cikin manema ne idan kin aminta shi kenan sai ayi yar gida indan kuma baki ra'ayinshi toh mu duk wanda kika kawo zamuyi maraba dashi".
Nan da nan idonta suka kawo ruwa "Abbah bana son aure yanzu ni bana son aure dan Allah Abbah kar kumin aure yanzu kaji?"
Mamakine ya bayyana a fuskar Abbah "Baki son aure kamar yaya Maryam ai duk ɗan aure bazai k'i aure ba"
Gwaggo tace "Ita fa fun abinda ya faru naga tsoro ya kamata duk tabi ta chanja"
"Karki kuskura kisa abinda ya faru da Halilu cikin ranki har ya iya zama wani dalili na tsorata ki haka Allah yake lamarinsa babu yadda bawa zaiyi sai godiya da kuma hak'uri" Faɗar Abbah.
Kwanta tayi jikin Gwaggo tana kukan da baza'ace ba shagwaɓa bace.
Nisawa Abbah yayi ya kalli Gwaggo "Ina ganin lokaci ya kamata mu bata tayi tunani sannan muni daga bakinta"
Gwaggo ta lasa baki "Toh ba nak'i zancen kaba amman dai ita Mairo har wani tunani tasan ta tsaya tayi ita dai tsoro ne kawai take ji kuma nasan In'sha Allahu zata daina"
"A'a mu barta dai har nan da zuwa sati tukuna"
Kai Gwaggo ta gyaɗa "Toh Allah ya kaimu ya saukwake"
Abbah ya amsa da 'Amin' Nan ta kalli Mairo "Tashi ki shiga ɗaki ni bari na duba abincin can ina ga ruwan ya tafasa"
Tashi tayi ta nufi ɗaki Gwaggo kuma ta nufi gurin girkinta.
Sai bayan La'asar Abbah ya baro garin daf da magriba ya iso gida.

Bayan Sallar Isha'i Qasin ya shigo part ɗin Momi.
Siraj kawai ya tararda zaune yana danne danne waya. Saida ya zauna sannan ya ɗago kai ya kalleshi "Yaya" "Na'am Siraj chatting kake ne"
"Eh Wallahi na ɗan kwana biu ban hau bane ya naga fuskar ka kamar ɗauke da damuwa?"
Ajiyar zuciya ya sauke "Ina Momi?"
"Tana part ɗin Abbah"
"Bata faɗa maka yadda Abbah yayi da Maryam ba?"
Dakan uku-uku gabanshi yayi nan ya aje wayar gefe ya fuskanci shi sosai "Bata faɗa min Wallahi miya faru?"
Saida ya sauke sauke wata ajiyar zuciyar sannan ya soma magana "Abbah yace ana faɗa mata kuka ta dinga yi tana faɗin ita bata son aure kowa yayi na'am da maganar yanzu matsalar daga gurinta take"
Shiru Siraj yayi ya tsorama Qasin ido "Wai yaya da gaske son ta kake?"
Qasin ya kalleshi "Hakan nake tunani"
"Tunani kake ma kenan"
Kawarda fuska yayi kamar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login