Showing 60001 words to 63000 words out of 85263 words

Chapter 21 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt

04 Apr 2026

902

baya son maganar.
"Toh yanzu ya zakayi?"
"Nima ban saniba banaan miye mafita ba"
Siraj ya busarda iskan bakinshi tare da sauke ajiyar zuciya "Idai har kana sonta toh kaje ka lallaɓata koda a waya ne. Maryam ba tada matsala tana da sauk'in kai. Kuna kasan ba wani wayau ne da ita sosai ba kana lallaɓa zaka shawo kanta wannan shine kawai nake ganin mafita"
Jimm Qasin yayi kamar mai tunani. can kuma ya jinjina kai "Ina ganin haka zanyi ka kawo shawara zan samu lokaci inje In'sha Allah"
Tashi Siraj yayi yana faɗin "Good luck" Ya nufi k'ofar fita.
"Thank you very much" Daf da zai fice Qasin yayi mishi godiyar yana murmushi.

Saida dare ya raba sannan ya tashi ya nufi part ɗin shi.
A hankalin ya tura k'ofar parlor ya shiga.
Da sauri Mansura ta tashi tsaye tana sanye da kayan bachi "Qasin ina kaje?"
K'arasowa yayi kusa da ita ya dafa kafaɗanta "Miyasa kika tambaya my dear?"
"Dubi fa agogo ka gani Qasin ɗaya saura"
Ta faɗa fuskarta ɗauke da damuwa.
Saida ya kalli agogon sannan ya shafa gefen fuskarta
"Ai ni bansan dare yayi ba ina can gurin fira"
"Fira?"
"Eh aure fa zan k'ara"
Wani tsire baki tayi "Taf ai Wallahi ko baka isa ba baza ka fara ba"
"Saboda mi?"
"Saboda Qasin dan Mansura kawai akayi shi. duk matar da tace zata saka sonka cikin ranta toh zata wahalarda kanta ne kawai"
Gira ya ɗaga mata "Allah ko?"
"Baka yarda ba kenan nidai yanxu faɗamin ina kaje?"
"Ina tunatar dake a koyaushe Mansura nifa nake auren ki bake kike aurena ba dan haka inda naje inda zanje duk bai shafeki ba kedai yanzu muje mu kwanta"
Bai jira abinda zata ce ba ya duka ya tallabeta kamar yar baby ya nufi bedroom ɗinshi da ita.

'''*** *** '''
*K'auye...*

"Alhamdulillahi yanzu kan cikina ya cika sosai" Mairo ta faɗa tana gyatsa.
Murmushi Gwaggo tayi "Haba ko kefa yanzu ba sai kiji k'arfi-k'afi ba haka nakeso kullum naga cinki kin k'oshi"
"Ai yanzu ina cin abinci ba laifi"
"Eh ai bance baki ciba amman dai yau kinfi ci da yawa dan rabon da kici abinci haka har na manta"
Mairo zatayi magana wani yaro yayi sallar.
"Assalamu alaikum wai ance ana salama da Mairo"
Mairo ta mere baki.
"Taf lallai ma jeka kace bata nan wani irin sallama yanzu da rana tsaka"
Gwaggo ta kalleta "A'a ba ayi haka ba baki san ko waye ba maza ba a musu wulakanci"
"Kofa wanene ni baza niba yanzu da rana ake fira"
"Saifa kinje ai bakinsan uzurinsa ba" ta kalli yaron "Kai jeka kace tana zuwa"
Juyawa yaron yayi ya fice bayan ya amsa da toh.
Gwaggo ta kalli Mairo "Tashi ɗauki mayafinki kije nace gaki nan zuwa"
Tashi tayi tana turo baki "Amman dai ni gaskiya Gwaggo bana son irin abun nan da kike min ni gaskiya wani karon ba zani ba"
Kai Gwaggo ta ɗaga mata "Eh naji yanzu dai jeki" kamar ta fasa kuka ta ɗauki hijabinta da kwanon da taci abinci ta fice.

Fitowa yayi daga cikin motar. yana sanye da wando pencil black color da blue t-shirt. Jingine yayi jikin motar yana kallon k'ofar gidan.
Da ture-turen baki ta fito suna haɗa ido ya jefeta da wani kyakkyawan murmushi.
Murmushi ita ta mayar mishi cike da fa'ah ta k'araso gurin da yake.
"Lahhh Yaya Qasin daman kaine?"
Murmushi ya sake mata as respond.
"Amman shine baka shiga ba kace ana nemana?"
Kai ya ɗaga mata still yana murmushi.
"Toh mu shiga ciki mana nida Gwaggo duk mun ɗauka ma wani ne Wallahi"
Sai a lokacin yayi magana.
"A'a bazan shiga ciki ba"
"Saboda gurin ki nazo ba ba gurin Gwaggo ba"
"Ni?" ta nuna kanta.
"Eh kefa nazo taɗi ne dan kar wasu su fini zuga su kwace min ke"
K'asa tayi da kanta tana guntse murmushi daya zoma.
Wata irin kunya ce ta baibayeta rungume jikinta tayi kamar mai jin sanye.
Fuskarta Qasin ya lek'a "Toh duk salon k'iyayyar ce kodai baki jindaɗi zuwan nawa bane. daman Abbab yace kince baki sona"
Da sauri ta kalle tana zaro ido "Lahhh ni Wallahi ban ce ba"
"Abbah yace lokacin da akayi miki maganar kuka kika rigayi"
"Eh ba kai nake yima kukan ba ni bana son aure ne kawai" Cike da shagwaɓa tayi maganar tana son yin kuka.
"Maryam...?"
Amsawa tayi ba tare data kalleshi ba.
"Na'am"
"Bakisan Aure sunnan Annabi bace kike cewa bakiso karatunki bai kaiki gurinda Annabi (S. A. W) yake cewa Aure Sunna tace duk wadda yak'i Sunna ta toh baya tare dani. shifa da kanshi yace kuyi Aure ku haifafa dan inyi alfahari da yawanku Ranar Alk'iyama.
Maryam mi yasa baki son Aure? Bakison ki zauna tare dani da Momi. Maryam ina sonki bazan cutar dake ba bazan miki wani abuba please ki yarda dani"
Kallonshi tayi fuskarta na nuna abinda yake zuciyarta k'arara.
"Yaya nifa ba ce bana sonka ba ni ba sonka ne bana yiba Auren ne bana so tsoro nake ji"
"Toh ki daina jin tsoro dan Halilu ya rasu baya nufin nima zan rasu kinji dan Allah ki amince da maganar Aurena Maryam kinji?"
Kai ta ɗaga mishi tana lank'wasar yatsun hannunta.
Ya ɗan daɗe yana fira da ita yana kwantar mata da hankali saida yaga ta soma gajiya da tsayuwar sannan yasa hannayenshi aljihu yace "Nikan bari na wuce kar tsayinki ya k'are ki faɗar min"
Dariya tayi "Toh mu shiga ciki sai mu zauna"
"A'a ni ba zan shiga ba yanzu zan wuce kice dai ina gaidata"
"Da gaske ba zaka shiga ba?"
"Allah bazan shiga ba wannan zuwan naki ne bana kowa ba"
Hannu yasa Aljihu ya ciro kuɗi masu ɗan dama ya mika mata.
Hannu biu tasa ta k'arɓa "Ahh Yaya duka?"
Nan ya sake mik'a mata wasu "Wannan naki ne wannan kuma na Gwaggo kice ina gaida"
Farin ciki ne wanwar a zuciyarta "Na gode Yaya Allah ya saka da Alheri" Murmushi yayi mata yana mamakin hali irin na Mairo watau har yanzu bata daina halinta na son kuɗi ba.
Buɗe Motarshi yayi ya shiga "Na tafi Maryam kiyi min Addu'a"
"Allah ya kiyaya ya tsare na gode sosai"
"Kada ki damu amman fa zanyi kiwarki"
Rufe ido tayi ta nufi gida da gudu.
In banda kallo babu abinda ya bita dashi yana murmushi har ta shige. Haka kawai sai yaji tayi mugun burgeshi.
Ya daɗe yana kallon k'ofar gidan sannan ya tada motar ya kama hanya.

Faɗawa Mairo tayi jikin Gwaggo tana dariya ta nuna mata kuɗin.
"Ahh Mairo ina kika samo wanene yazo?"
Da dariya tace "Yaya Qasin ne Wallahi"
"Wane Qasin dai?"
"Na birni mana na Momi"
"Wai Qasimu kike magana?"
"Eh nayi-nayi dashi yace shi ba zai shigo ba wai guna yazo saidai nace yana gaishe ki"
"Gurin ki kuma?"
"Eh wai shi fira yazo"
"Au" Gwaggo tayi dariya "Sai yanzu na gane hausarki toh Allah yasa ki k'arɓa mashi da ga dukan alamu dai yana sonki kece dai baki sonshi"
"A'a Gwaggo nifa bance bana sonshi ba kune da kuda Abbah kuka ce amman ni bance bana sonshi ba"
"Ah toh kina sonshi kenan yanzu fa amincewarki kawai muke jira da kowa yayi na'am da Auren nan kice kawai ake jira kin amine ko?"
Murmushi tayi ta duk'unk'une kanta cikin hijab ta shige jikin Gwaggo.

*** *** ***

Cikin satin zuwan Qasin uku k'auye duk zuwan da yake bai taɓa yarda ya shiga cikin gidan ba.
Saidai yace yana gaida Gwaggo ko ya aika mata da kuɗi ko siyayyah.
A yan kwanakin nan da yayi yana zuwa sai duk yaji ya hak'u da ita. Ita idan tana tare dashi sai ta riga jinta cikin wani yanayi na daman.
Idan zai tafi har jin take kamar ta bishi har dai zuwanshi na ukun nan daya ɗauketa suka tafi zaga gari.

*Saturday Morning*

Duk zazzaune suke part ɗin Momi suna fira. Kasancewar yau weekend.
Sallamar da Abbah yayi tasa duk suka kalli k'ofa tare da amsawa. Kusa da Momi ya zauna yana amsa gaisuwar da suke mishi.
Nan suka sake dasa wata sabuwar firar yan siyasa. Sai kusan sha biu na rana Qasin ya kalli agogo yace "Bari na tashi akwai inda nake son zuwa"
Abbah ya kalleshi "Qasin baka tambaye ya akayi akan maganar Maryam ba kasan jiya sati ɗaya kenan"
Murmushi yayi "Abbah tsoro nake ji"
"Tsoro sai kace ba Namiji ba" Momi ta faɗa
"A'a bafa irin wannan tsoron nake nufi ba na kar naji mummunan amsa nake nufi"
"Toh ba zakaji ba dan ta aminci jiya da yamma Baba Saminu ya kira yace min yarinya tace ta amince"
Wani kalar murmushi ne yazo ma Qasin ya kasa ɓoye farin ciki shi sai dariya yake haka kawai yaji wani irin jindaɗi ya mamaye shi bakinshi har kunne ya kalli Abbah "Amman na jindaɗi Wallahi Allah ya tabbatar da alheri banyi tunanin zata amince ba"
Usman ya kalleshi yana dariya "Ashe yaya kana sonta"
Harara ya watsa mishi ya kawarda kai.
Siraj ya dafa shi yana murmushi "Congratulations Bros Allah ya saka albarka a ciki"
Duk suka amsa da 'Amin' suna dariya.
Siraj ya ciro wata takarda cikin aljihu shi ya mik'awa Abbah yana faɗin "Abbah nafa samu transfer"
"Transfer?" Duk suka kalleshi da mamaki.
Abbah ya karɓa yana tambaya "Zuwa ina kuma?"
"Abuja suka mayarda ni Abbah"
Qasin ya kalleshi fuskarshi da ɗan damuwa "Amman dai gaskiya ban jindaɗi ba anya zaka iya zama can kuwa?"
"Zan iya mana ai transfer tazo a daidai dan daman na gaji da garin nan"
Abbah yace "Toh Allah yasa haka shine mafi alheri"
"Amin Abbah nima haka nake rok'o"
Momi dai uffan bata ceba saidai tunda ya faɗi maganar yanayin ta ya chanja.
Har suka gama tattauna akan maganar transfer bata ce k'ala ba saima tashi da tayi ta bar gurin.

*© KHADEEJA CANDY*
[10:45AM, 3/28/2017] Khadeeja_ce👌: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

*_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

_I
[11/9, 6:58 AM] Khadeeja Candy: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

     *_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

*Vote me on Wattpad* @khadeeja_Candy

*57*

Tana shigewa gida shima ya buɗe Motar shi ya shiga.
Driving ya rik'ayi da gudun tsiya. ya rike sitarin Motar da k'arfi. Ya haɗe rai kamar bai taɓa dariya ba sai faman buɗan hannta yake.
         Cikin yan mintuna ya isa gida. Kamin a buɗe mishi gate ya danna horn baji ba gani kamar zai tada gidan.
Da gudun mai gadin ya buɗe. Wani mahaukacin parking yayi ya fito ya nufi parlor Hajiya.
Da k'arfi ya banko k'ofar parlor ya shigo Hajiya na zauna ita da k'awarta suna fira yanayin yadda taga fuskarshi tasan ba lafiya da sauri ta tashi tsaye.
“Lafiya Yusuf?"
hak'oranshi ya haɗe ya ɗantse gam sannan ya bata amsa.
“Ba lafiya ba lafiya ba"
      Hajiya tasan sarai zai iya faɗar komai a gaban k'awarta.
duk da yake aminiyarta ce amman kuma ɗa da uwa sai Allah, hakan yasa ta rik'a hannunshi suka nufi ɗaki.
          K'ok'arin zaunar dashi ta shiga amman yak'i saima fisge hannunshi da yayi daga rik'on da tayi mishi.
Kallonshi tayi fuskarta ɗauke da damuwa da kuma mamakin abinda ya ɓata mishi rai har haka.
“Wai miya faru ne Yusuf waya ɓata maka rai haka ne?"
   “Kune ku kuka ɓata min rai tun yaushe yake bibiyarku akan kuje ku nema min aure Maryam amman kuka k'i toh gashi nan yanzu Qasin zai Aure ta"
Shiru Hajiya tayi kamar wadda ruwa ya canye.
can ta sauke ajiyar zuciya tace “Alhamdulillahi Allah ya karɓa Addu'a ta"
Da sauri ya kalleta “Kinji mi nace kuwa?"
Faɗa Hajiya ta rufe shi dashi.
    “Naji Yusuf naji wai kai har yaushe zaka san ciyon kanka ne yaushe zaka san abinda ya dace dakai da wadda bai dace ba.
Ina mamakinka Yusuf Namiji kamar ka mai ilmin da wayewa da arziki da mulki da isa da Sarauta da kamala.
          ta ko ina Allah yayi maka baiwa amman ka lashi takobin kai sai ka Auri yarinyar da bata san A ba bari B yarinyar k'auye, k'azama, yar k'aramin gida,  kuma k'aramar yarinya.
Kai ko kunya baja ji aganka da ita a matsayin mata?
   a family nan taya zaka nuna ta ko gun abokanka ma ai abin kunya ne.
Auren nan ni mahaifiyarka bana so haka mahaifinka shima baya so. 
   toh akan mi zaka nace sai ita daga gamon tsintsiya da ragga.
Toh bazaka Aure ta dan bata dace da kai ba daman na daɗi ina rikon kada Allah ya haɗa Auren nan"
     Kai ya gyaɗa mata “Fine Addu'arki ta k'arɓu na rasata. Ku kuma kin rasa suruka har a bada!"
    “Mi kake nufi?"
Juyowa yayi ya fuskance ta.
    “Bazan Auri wace nake soba saboda na rasata. Dan haka bazan taɓa Auren wace kuke soba sai dai na Mutu banyi Aure ba"
Yana kaiwa nan bai jira abinda zata ceba ya kaɓa rigarshi ya fice.
   Faɗuwa Hajiya tayi zaune saman gado tafe da kai tana faɗin.
        “Innalillahi wa inna-ilaihi raji'un ya Allah ka shirya min wannan bawa naka ka sassauta mishi wannan Zuciya"

          **********

Abbah ne ya fara shiga tare da kawunshi Momi na baya ita da Qasin.
Gwaggo ta fito daga ɗaki tana amsa sallamar.
“Amin wa'alaikumussalam ah'ah marhaban da manyan bak'i harda kawu"
Komawa tayi cikin ɗakin ta ɗauko sabuwar tabarma ta shinfiɗa musu.
“Bissimillah Kawu ga tabarma ku zauna"
Ta kalli Momi “Ah Hajiya sannu da zuwa Qasin mu?"
Ya amsa yana k'ok'arin zaunawa
     “Na'am Gwaggo ina wuni?"
     “Lafiya kalau ya hanya aikan kumsha rana wannan k'walele"
   “Gaskiya kan ana rana kwanakin nan gari kamar zai kama"
Faɗar Kawu.
Abbah yace “Har dai nan arewa gaskiya ana buga zafi sosai"
    “Zafin bana kan ai saidai hamdalla"
Momi ta faɗa tana firfita da gefen mayafinta.
Tashi Gwaggo tayi ta ɗauko musu fura tare da bulbulo ruwan tulo mai sanyi ta aje musu,
   Abbah ya ɗauka ya mik'awa Kawu saida ya sha sannan duk suka sha.
Aka ɗauko sabuwar firar yaushe gamo.
   
_2:02pm..._
Momi na k'are Addu'a sallame sallah Gwaggo ta kawo mata wake da shinkafa.
“Ga naki Abincin kici su kuma ga nasu can in sun dawo"
Murmushi Momi tayi “Sannu Gwaggon yara ba'a gajiya?"
  “Gajiya da mi kin jiki da wata magana"
    Momi ta k'arayin murmushi a karo na biu “Toh Allah ya biya.
   wai nika Gwaggo nace banga Maryam ba tunda nazo"
  Gwaggo tayi dariya.
“Maryam yar gidanki ai yanzu ta daina zama nan tunda abin nan na faru ta koma gidan Hindatu". _(k'aunar Gwaggo)_
  “Wani abin ne ya faru?"
Cike da son sani Momi tayi mata tambayar.
       Gwaggo ta gyara zama.
   “Wallahi rannan ina zauna tsakar gida na faɗa miki ta shigo min da baki duk jini,
Fuska kuma a kumbure sai kuka take wai Yarima ne ya fasa mata baki"
Momi ta zaro ido “Yarima kuma mi tayi mishi?"
   “Bata mishi komai ba kawai dai tace dan ta faɗa mishi Qasimu zai Aure ta shine fa yaji haushi ya mareta"
     “Daman yana zuwa nan ne?"
  “Eh can ba'a sara ba yakan zo ni abin ya ban mamaki nace ba ɗan'uwanki bane?"
   “Dan'uwa nane baisan da maganar Auren bane Shiyasa"
  “Ayyah aiko tun lokacin sai duk tabi ta tsorata ta ringa ganin kamar dawowa zaiyi yayi mata wani abin,
Shiyasa sai ta koma can gidan Hindatu da zama"
   Momi zata sake magana su Abbah suka yi sallama.
Haɗa baki suka yi ita da Gwaggo gurin amsawa.
Bayan sun zauna Momi ta labarta musu abinda yake faruwa.
       Mamaki ne ya cika Abbah “Amman mi yasa Yarima yayi haka sai kace marar tunani"
   Momi ta nisa tace  “Yarima kayan Allah kasan Halin shi da zuciya"
   “Toh miye abin zuciya a ciki harda bugu?"
  Gwaggo ta tari numfashin Abbah “Shiyasa ma duk muka k'agu muga anyi bikin nan ta ɗaga daga gunmu zuwa gidan mijinta"
Sai a lokacin Qasin yasa baki.
     “Haka ne kan kuma dan Allah inason da an ɗaura Auren nan na zuce da ita"
   Harara Momi ta watsa mishi “Wannan wane irin abune haka ina ka taɓa jin anyi haka?"
  Kawu yace “Toh ai ba wani abin bane tunda ba budurwace ba kuma ai can zata zauna"
      Abbah ya karɓa mishi “Nima dai haka na gani indai an ɗaura Aure ai ba wata matsa"
“A'a gaskiya bazan yarda ba shikenan
daga ɗaura Aure sai yaje da mata sai dai ka aiko da Mota aje da ita gaskiya muda dangi mu kai ta ɗakinta"
  “Ki daiyi hak'uri ya wuce da matarshi kawai" cewar Abbah
   “A'a ban yarda ba gaskiya"
“Shikenan Gwaggo na amince da an ɗaura Aure zan aiko a tafi da ita da duk mai son zuwa"
    Gwaggo tayi murmushi “Yauwa toh kaga haka yafi Tsoho yasa muku ranar ne?"
   “Eh ansa Ranar Jumma'a mai zuwa yace kuma yace sadaki dubu ashirin"
     Gwaggo ta rik'e baki
     “Dubu ashirin haba dai shiko Tsoho ai ya cika sai kace budurwa"
Murmushi Abbah yayi “Babu komai ai tunda yace yana so"
   “Toh Allah yasa alkhari a ciki"
  Abbah ya amsa da    “Amin kuma mun faɗa mishi bam son komai komai ni zanyi Amaryar kawai za'a kai mana"
    Gwaggo saboda jindaɗi ta sara ina zata saka kanta godiya tayi musu sosai da Addu'ar Alkhari.
Abbah yace
      “Ai babu komai itama ya tace koba Qasin ta Aura ba zan iya mata haka"
   Gwaggo tayi murmushi
    “Ai nasanka alhaji ba daga nan ba indai wannan ne tun muna yara"
   Duk dariya sukasa aka tada labarin k'uruciya.

    Saida yamma liss suka baro garin bayan sunyi biye biyen gidajen dangi.
  A lokoja road Qasin ya sauke kawu sannan ya nufo hanyar nasu gida.
    Part ɗin Momi yayi parking su Abbah na fita shima ya fita ya nufi part ɗin shi cike da farin cikin da baisan dalilinsa ba.
        Yana shiga ya faɗa bath room ya watsa ruwa ya fito ya shiga sallar I'sha, dan Magariba tun a hanya sukayi Momi ce kawai zatayi ramako.
   Bayan ya sallame sallar yana cikin Addu'a Mansura tazo ta zauna saman sallayar tana mashi murmushi.
    Saida ya shafa Addu'ar sannan ya mayar mata da murmushin.
  “Dear na ya akayi?"
“Lafiya kalau dear ina kuka je tun safe?"
Kumatunta ya rik'a ya girgiza “In da kika aike mu"
   “Please nidai faɗa min tun safe fa kuka fita kuma harda Momi da Abbah?"
Janyota yayi ta kwanto jikinshi.
   “Zan faɗa miki amman ba yanzu ba sai nan da kwana biyu mi kika dafa min?"
    “Ni ban dafa komai ba kai nake jira kawo muje muyi takeaway"
   “Hum toh tashi ki shirya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login