Showing 75001 words to 78000 words out of 85263 words

Chapter 26 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt

04 Apr 2026

893

   K'in tashi tayi daga gurin ta marairaice mishi fuska, “Minene wai baby na?"
  “Gun da ka ɗauko ni zaka mayar dani"
“Au daga na miki alfarma na ɗauko na kawoki sai kuma kice sai na maida ki"
  “Eh ai bance ka ɗauko niba"
  Dariya yayi yasa hannu ya lak'atar mata hanci “I love you Maryam"
   Murmushi tayi ta rik'e mishi hannu “Yaya Qasin... " sai kuma tayi shiru.
    Risinawa yayi daidai kunne ya busa mata iska “Faɗi maganar Yayanki yana jinki"
  Ido ta sakar mishi tana murmushi.
Can kuma ta ɗauke ido ta tashi yana rike da hannunta suka koma saman kujera.
    “Faɗi maganar ki baby na"
   "Momi nake son ka kira min a waya ko kuma ka kaini"
“Zan dai kira miki ita a waya amman zuwa can kan ba yanzu ba kin yarda"
  “Eh kira min ita"
Wayar shi ya ciro ya danna kiran yana faɗin “yanzu kuwa yar gidan Momi"
  Bata daɗe tana rawa ringing ba Momi ta ɗauka sai da ya gaisa da ita sannan ya mik'awa Mairo, tana karɓa ta tashi ta nufi ɗakinta da gudu,
Da ido ya bita har ta shige sannan yayi murmushi.

    Saman gado ta zauna tana yima Momi ina kwana “Momi an tashi lafiya?"
  “Lafiya kalau Maryam ya gidan?"
“Lafiya kalau ina Usman da Nura?"
  “Suna nan kalau ko jiya sai da sukayi maganar ki"
  “Momi kice ina gaida su"
  “Toh zasu ji lafiya dai ko?"
  “Lafiya kalau Momi wai jiya Yaya Qasin yake faɗa min Mansura zata dawo"
“Eh haka ne toh mi akayi?"
  Shiru tayi, Momi tace “Maryam kaki saka tsoro a cikin ranki karki kuskura mayar da kanki ballagaza a gaban kishiryar yanzu fa kin tashi daga matsayin da kike na da kin koma *BABBAR MACE* kada ki shashanta kanki ki wulakanta kanki kin gadai mijinki yana sonki,
   Kuma zaman Aure ya kaiki karki biye mata ki kyautata mishi dab haka ne zai k'ara mishi sonki karma ki shiga sabgarta ban kuma idan tayi miki abu karki rama ba.
yadda take mace haka kike matsayinta da naki duk ɗaya ne dan haka karki soma min wani complain indai akan Mansura ne kuma bari kiji na faɗa miki karki yarda ki nuna mata kina tsoro ta dan ba'a nunawa kishiya haka"
   Ajiyar zuciya ta sauke cikin sanyi murya tace “Toh Momi zanyi"
    “Wai Maryam miye anfanin makarantar da nasaki waike ba zaki waye ba kima kamar sauran mata? Yaushe zaki fara ɗaukar darasin da ake koya miki a makarantar?"
  “Daman Momi ni ba wani abin zance zanji ne kawai inda gaske ne zata dawo"
“Toh yanzu ai kinji zata dawo kae naji kin mayarda kanki wata kalar mace ki rik'e k'imarki Allah ya haɗa kanku ya baku zama Lafiya"
   “Amin Momi na gode a gaida gida"
“Gida zaiji ki fara girkinki yau dan bazan sake aiko muku abinci ba"
   “Toh Momi"
Dariya ta dingayi har Momi ta karshe wayar.
   Sannan ta tashi ta koma parlor, kusa dashi ta zauna ta mik'a mishi wayar “Gashi nan na gode"
Karɓa yayi “Toh kun gama sirrin?"
“Eh mun gama sai gobe kuma"
    “Da wayar wa?"
Tashi tayi taja mishi kunne biu “Da kunnen ka" ta watsa da gudu ɗaki.

       ***
Jalof ta girka da rana da dare kuma tayi mishi Tuwo da miyar akusi,
    Sosai Qasin ya jindaɗi ya kuma ci abincin sosai yana sa mata albarka. Da safe ma da dumamen tuwon ya karya.
   Sai goma na safe ya shirya ya fita,
Saida ta gama gyara gidan ko ina gwanin shawa'awa sannan ta shiga tayi wanka ta shirya cikin koriyar atamfa. Ta nufo parlor.
    Tana k'ok'arin zama taji an buga k'ofa basa zaman tayi ta nufi k'ofar tana tambayar waje ne,
   “Khadeeja'tu ce mak'ociyarki"
  Da far'ah ta buɗe mata “Ah Khadeeja sannu da zuwa"
  “Yauwa sannu Amarya ina dai fatar angonki baya ciki?"
“Shigo baya nan ya fita"
   Shigowa tayi ta zauna Mairo ta ɗauko mata drinks,
        Sannan ta zauna tana tambayarta ya gida,
  “Gida lafiya Amarya kin gyara gida sai k'anshi yake"
  Murmushi Mairo tayi “Kai Khadeeja'tu kullum baki rasa magana a bakinki"
   Dariya tayi suka cigaba ta ɗauko mat wani zancen.
  Suna cikin fira Qasin ya shigo.
       Da sauri Khadeeja'tu ta tashi suna haɗa ido ta sakar mishi murmushi ta gaishe shi sannan ta fice,
  Mairo kuma ta nufoshi tana faɗin “Har ka dawo?"
   Tsaye yayi yana kallonta fuskarshi ɗauke da murmushi “Kinyi min kyau baby na"
  Ita ma murmushin tayi “Na gode dear"
  “Haka kawai zaki ce?"
   Murmushi ta sakeyi dan tasan mi yake nufi ta hau saman Kujera ta kamo tsawon shi ta sakar ma kumatunshi kiss.
    Rumgume yayi ya ɗauketa suka nufi ɗaki, saman gado ya sauke ta ya bude drawer ya ɗauki wasu k'ananan documents sannan ya rik'o hannun ta suka nufo parlor,
    Dai-dai bakin k'ofar parlor ya tsayar da ita yana shafa gefen wuyanta “Yau mi zaki dafa?"
   “Mi kake so?"
“Dambu ai kin iya ko?"
Wani fari tayi mishi da ido wadda ita kanta batsan tayi ba “Sosai ma"
   “Toh shi nake so"
“Zan yi maka"
Murmushi yayi zai sake magana yaji horn.
  Juyawa yayi daga shi har ita suna kallon motocin da suka kunno kai gidan,
   Ko ba'a faɗa ba yasan Mansura ce da muk'arrabanta. Juyowa yayi ya kalli Mairo “Baby na bari naje office na jirana but please karki kula su kinji ba zan daɗe ba yanzu zan dawo alright?"
    Murmushi “Okay Allah ya tsare"
  Murmushi yayi mata as respond, har ya juya sai tayi saurin kamo hannun shi ta sakar mishi kiss.
    Daɗi yaji ya shima ya sakarma goshinta kiss, har ya shiga mota murmushi suke sarkarwa juna. Bayan yayi mata key ya ɗago mata hannu har ya fice bai kalli gurin da Mansura take ba.
    Yana ficewa Mairo ta juya ta shige parlor,

  Duk abinda suke Mansura na tsaye tana kallonsu ita da k'awayenta da kuma Sisters ɗin biu. 'Daya daga cikin k' awayen ta tabe baki ta kalleta “Amman Wallahi Qasin ya iya cin mutun da Auro miki wannan yarinyar a matsayen kishiya"
    Nan suma sauran suka hau saka nasu baki suna zugata,
    Sun daɗe tsaye a gurin suna cak-cakar ta sannan suka nufi cikin parlor.
    Basu sallama hakan yasa Mairo bata bi ta kansu ta cigaba da kallonta, “Kee baki ga mutane bane hala?"
   Nan ma banza tayi dasu. 'Dayar ta kalleta tana wata dariya “Wayyo ni Allah wai wannan ce Kishiyar ki?"
   Sai a lokacin Mairo ta kalleta “Eh nice ya ranki?"
   Duk tintsirewa sukayi da dariya Mansura tace “Ita kin ganta kamar k' aruwa ko?"
   “Lallai kuwa k'amar karuwa baki ga har da mishi kiss ba daman dai taba inba haka ba duk yaushe akayi Aure da har zata sake jiki tana irin wannan karuwancin?"
Faɗar sister Mansura.
    Tashi Mairo tayi tsaye ta ɗanja baya ta taɓe baki
“Daɗin abinda dai karuwancin mijina nayi ma kuma duk mace da kika ta zama karuwa a gaban mijinta toh ta isa ne"
   Mansura ta rike baki “Lalala ke yar k'auye yaushe kika zo da har zaki tsaya faɗa min magana Wallahi in kikayi wasa saina miki shegen duka naga uban da zai rama miki"
   Ba k'aramin ɓaci ran Mairo yayi ba cikin zafin rai tace “Yar k'auyen da kike rainawa tafi ki dajara a gurin mijinki da nice Wallahi bazan dawo matukar baje bikona ba dan hakan ya nuna mijina bai damu dani ba ko kuma baya sona"
   Tana kaiwa nan ta juya ta nufi kofar ɗakinta, da k'arfi Mansura ta fisgota ta watsa mata mari. Jefar ita tayi saman kujeara da niyar dukanta. Da sauri wata friend ɗinta fa rik'eta “Haba dai ke kuwa daga zuwan mu zaki daketa ai wannan tsakanin ku ne daga ke sai ita kiyi mata yadda kike so ke k'aramar yarinya kamar wannan ta isa ta raina miki wayo har ta faɗa miki magana haka kawai ki bari sai kin zauna saiki gyara mata nata zaman"
  Sakinta tayi tana faɗin “Ai da kin barni naci uban Shegiya"
   Mairo na tashi ta nufi ɗaki ta sauri tana kuka.


*© KHADEEJA CANDY*
[11/9, 7:00 AM] Khadeeja Candy: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

     *_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

*Vote me on Wattpad* @khadeeja_Candy

*62*

Sai da Mairo ta tabbatar da sun gama gyare-gayarensu su tafi, sannan ta fito ta shiga kitchen.
   Tana kare girkin ta kama ɗakin,
   Sai goma dare Qasin ya dawo gidan kai tsaye ɗakinta ya nufa “Baby na kinga ni sai yanzu aiki ne ya rik'e ni"
   Fuskarta shagwaɓa tayi “Amman kuma har dare kadai ko dan matar ka ta dawo ne?"
   Kusa da ita ya zauna “Oh karki kawo wannan a ranki yanzu dai muje ki haɗa min ruwa nayi wanka sai mici abinci ko?"
  Hannunta ya rik'a suka fice tare.
  
  Bayan yayi wanka ya saka kayan bachi suka dawo parlor suka ci abinci sai dare-dare suke, ba k'aramin bachi ran Mansura yayi ba ganin ko ɗakinta bai leko ba.
   Sun daɗe suna fira parlor saida dare ya tsala sannan suka nufi gurin bachi,
  _Washe gari_ guraren 8 Mairo ta fito ɗakinta zaune ta tararda Mansura tana kallon k'ofar ɗakinta bata kula taba ta nufi kincin.
   Aiko tana shiga Mansura ta rufa mata baya, a bakin kofa ta tsaya ta katsa mata tsawa “Ke uban mi zakiyi a kitchen ɗin?"
  Juyowa Mairo tayi tana hararata “Uban ki zanyi kinsan ai yafi daɗi ci wai ke Mansura mi kike ɗaukar kanki ne?"
   “Ke ni zaki faɗama wannan maganar? Ke nan fa gidana ne kuma Wallahi in baki bi a hankaliba sai na miki ɗan ba zan duka"
  Taɓa hannu Mairo tayi “Amman naga ai da kunya ki kira kanki matar gida matar da bata san darajar mijinta mijin kullum cikin kuka yake da ita ke bari kiji na faɗa miki yanda nan gidan yake gidan mijinki haka nima yake gidan miji n babu banbanci dan haka ki fita idona kona gyara miki zama"
    Hannu Mansura ta kai zata mare ta da sauri Mairo ta rike “Kinyi na ɗaya bazaki kara na biu ba kinyi kaɗan ki sake sakamin hannu a fuska ko wacan karon da kikayi na  kyaleki saboda mijina ne"
  Jefar da hannun nata tayi ta juya ta cigaba da aikinta.
    Tsaye Mansura tayi tana mamaki da kuma jin tsoro dan gani take kamar ba Mairo ba,
    Ruwan zafi Mairo ta ɗora sannan ta shiga feraye ɗankali. Har lokacin Mansura na tsaye tana kallonta,
  Can ta matsa kusa da ita ta kai mata wani mugun shuri, tashi Mairo tay daga zaune ta dake ta wankeata fuska da mari biu ta janyo muciya ta buga mata ita a kafaɗa,
  Da sauri tayi baya ta dafe kunci tana zaro ido “Maryam ni kika yima haka?"
   Wani ya tsine hanci tayi “Kaɗan kenan daga abubuwan dana tanadar miki saibna gyara miki zama acikin gidan nan kuma ki fice ki bari guri ko yanzu na chaja miki halinta"
   Kai ta gyaɗa “Ke wai gidan ubanki ne nan Wallahi zan halakaki"
   “A'a ba gidan ubana bane amman inajin ke gidan naki uban ne ko ki fice ki bani guri ko Wallahi na miki wanka da ruwan zafi nan"
  Tsaye tayi tana kallonta cike da tsoro saida taga ta nufi ruwan zafin sannan ta juya da sauri ta fice.
'Dakinta da dawo ta zauna tana mamakin Mairo tabbas aljanune da ita haka zuciyar ke nasa mata dan daga ganin faɗan nan bana banza bane iskokinta ne ke son tasowa, haka ta dinga tunane-tunanenta tana naman hanyar da zata biyo mata.
   
Tana ficewa Mairo tayi k'wafa ta buga tsale “Yauwa yanzu kin fara gane karatun kenan ai nima yar issakar kaina ce"
  Cigaba tayi da girkinta tana mai jindaɗin abinda tayi har ta gama sannan ta shiga tayi wanka ta shiga tada Qasin,
   “Yaya tashi abincin yayi"
  Janyo ta yayi ya rumgume “Toh bbyna"
  Ya daɗe rumgume da ita sannan ya tashi ya shiga bathroom,
Bayan ya gama abinda zaiyi ya fito suka nufi dining, suna cikin karyawa ne Mansura ta fito daga & ɗakinta dan muryar su taji ya tabbatar mata da suna dining.
  Har ta zauna Mairo harararta take. Plate taja da cup zata zuba ta bude kular k'wai zata zuba,
   Nan Mairo ta tashi tsaye “Ke mi zakiyi?"
  Banza ta mata ta cigaba da zubawan,
Kular k'wan Mairo ya janyo da k'arfi “Ai baki isa ba Wallahi indai zakice sai dai ki girka ni mijina kawai nake iya girkama abinda duk wata k'atanyar banza tayi kaɗan Wallahi"
   Kallo Mairo Qasin yayi kamar yayi magana sai kuma yayi shiru ya cigaba da cin abincin,
   Mansura ta Taɓe baki “Ni ba biye miki zanyi ba dan na fahimcin baki da hankali ba ki kuma da tarbiya"
   Nan Qasin ya saka baki “Ke ya isheki haka ke idan na Maganar tarbiya har kina da bakin magana?"
  Mamaki ne ya cika Mansura “Qasin ni kake faɗama haka saboda kayi sabuwar Amarya kan uba" ta faɗa tana gyaɗa kai.
  Filas ɗin ruwan zafi Mairo ta buɗe tana faɗin “Yanzu zakiga rashin hankalin nawa"
   A fuska ta watsa mata su kamin ta ankara ta k'ara watsa mata su har so uku, cikin hanzari Qasin ya rik'e yana “Maryam lafiyarki?"
   Ita kuma ta faɗi tana ihu da murzar jiki.
   “Wayyo Allah na shiga uku ta kashe ni wayyo Allah"
Nan ya saki Mairo ya nufe yana kiran sunanta, rik'a ta yayi ya tada ita ya nufi mota da ita.
Tsaye Mairo tayi tana kallonsu har suka fice sannan ta cikama bakinta iskan dan tasan tayi ɓaran-ɓarama.

*© KHADEEJA CANDY*
[11/9, 7:01 AM] Khadeeja Candy: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

     *_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

*Vote me on Wattpad* @khadeeja_Candy

*63*

Asibiti ya nufa da ita bayan an bata gado, ya kira a gidan su ya sanar.
Cikin yan mintuna mahaifiyarta ta iso tare da k'anenta biu, tambayarshi suka rik'ayi yadda abin ya faru bai faɗa musu gaskiya sai kawai yace ruwan zafi ne ta ɗauko sai ya watsar mata a fuska da jiki.
   Sai da ka kira sallar Azahar sannan ya baro asibitin ya nufo gidan Momi, a masallacin dake kusa dasu ya tsaya yayi sallah sannan ya shiga ciki.
   Tun daga yanayin Sallamar shi Momi ta gane akwai abinda yake faruwa bayan sun gaisa ta soma tambayarshi, “Ya akayi yau naga kamar ranka a ɓace?"
  Saida ya sauke ajiyar zuciya sannan yace “Momi Maryam ce ta watsama Mansura ruwan zafi"
   “Subhanalllahi garin yaya?"
Nan ya kwashe abunda ya faru ya faɗa mata.
  Baki Momi ta rik'e “Da gaske Maryam ce tayi?"
  “Itace Momi kuma ni irin masifar nan ce nake gudu kar wata rana suje suyi abinda yafi haka kuma"
   “Ai maganin biri karen baguzawa abinda Maryam tayi Batayi dai-dai ba amman kuma hakan zai sa Mansura ta ɗan saurara mata"
  Qasin ya gyaɗa kai “Ko kuma tace saita rama ba"
   “Abinda nake so dakai indan taji sauk'i sai ka tarasu guri ɗaya kaja musu kunne"
  “Toh Momi zanyi haka In'sha Allahu"
  Sai da yaci abinci sannan ya bar gidan.

  Mairo na zaune parlor ya shigo da sallama amsa mishi tayi tana kallon cikin idonshi, k'in yarda yayi ya haɗa ido da ita tana mishi sannu da zuwa ya amsa ya wuce dakinshi,
   Da ido ta bishi har ya shige sannan ta zauna saman kujera tana sauke ajiyar zuciya. Duk sai raji ba daɗi. Ta kusan minti 30 a haka sannan ta tashi ta nufi ɗakin nashi.
   “Assalamu alaikum" a sanyaye tayi sallama shi kuma ya amsa mata yana daga kishingiɗe tana dannar wayar shi,
   Juyawa tayi zata koma nan ya ɗaga kai ya kirata “Maryam"
  “Na'am" Juyowa tayi ta k'araso kusa da gadon shi idonta cike da hawaye.
   Nan ya unk'ura ya tashi zaune “Mi akay?"
  “Ba komai"
“Ba komai kike kuka?"
“Naga kana fushi danine"
  “Kan mi zanyi fushi dake ni bana fushi dake amman abinda kikayi ban jidaɗi kuma baki kyauta ba"
  “Amman ita ta kyauta data fasa min kai ko?"
Cike da shagwaɓa tayi maganar.
  Murmushi yayi mata ya janyo ta ya zaunar saman k'afafunshi,
  “Toh ramuwace kikayi kenan?"
  “A'a nidai bance ba"
“Amman nasan nufi kenan naji yanzu kin rama ai shi kenan ko dan Allah karki sake kinji ku zauna lafiya nine za jindaɗi in kika min haka karki sake kulata"
   Kai ta ɗaga mishi “Bazan sake ba amman sai idan ita bata min ba"
   “Ba zata miki ba zanja mata kunne itama"
  “Naji tashi muje kaci abinci"
   Tashi yayi badan yana jin yunwa ba sai dan yana gudun yace baya ci tace mishi fushi yake da ita.
   Zamansu su cigaba dayi na ma'aurata wani abu bi sake shiga tsakanin su,

***      ***      ***    ***
Mansura kin yarda tayi ta dawo gidan bayan an sallame ta daga asibiti danginta sai masifa suke ita kuma tace sai da ya zaɓa ko ita ko ita ko kuma ya raba musu gurin zama shi kuma yace ba zaiyi ko ɗaya ba Momi tace mishi ya samu musu ido idan ta gaji ita zata nemi dawowa,
   

*BAYAN WATA UKU*
     Rufe yake da ido Mairo na gudu yana binta suna yar link'wa. Saman kujeara ta hau tayi tsaye tana taɓa bayan shi juyowa yayi cikin hanzari ya rike yana faɗin “Na kama" ita kuma ta fashe da dariya suka faɗi k'asa,
  Wata razzanann ihu ta saki lokacin da kuiwar  hannushi ta daketa a mara by mistake.
    Da sauri ya buɗe idon yana tambayar ba'asi. kasa magana tayi sai kuka take tana rike ciki, nan ya shiga duba cikin. Jikin da yaganine ya katse mishi hanzari,
     da sauri ya ɗaga ta amman ta kasa tsaye sai kuka take tana kiran Abban ta saman kujera ya zaunar da ita ya nufi ɗaki, riga yasa ya ɗauko keys ya dawo parlor a guje ya ɗauke ta ya nufi mota da ita.

           Asibiti mafi kusa ya nufa da ita yana isa ka wuce da ita Emergency,
  Shi kuma ya kasa zaune ya kasa tsaye sai safa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login