Showing 18001 words to 21000 words out of 85263 words
Chapter 7 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt
komai ba sai Mairo take tsaye rufe da baki tana shawaye.
rikota mansura tayi suka fito gurin Qasin ta nufo tun kamin ta karaso ta jefa masa tambaya “mi kayi mata Qasin?”
ba tare daya kalleta ba yace “mi kike tunanin zanyi mata?”
“ka bani amsa ta kawai Qasin ya zaka saka ta cikin ɗaki harda zare bel zaka ɗaketa mi tayi maka?”
wani dogon tsaki yaja ya tashi fuska a haɗe ya fisgi hannun Mairo suka fice.
tunda suka fito Mairo take masa magiyar karya daketa,
yana shigowa parlour ya jefarda ita saman kujera yana kiran momi.
jin shiru yasa ya nufi upstairs. bai jima ba ya fito ya nufi kicin nan ma bai jima ba ya fito ya nufi gurin Mairo dake kuka,
da sauri ta tashi zaune tana share hawaye sai wani numfashi take kamar zai ɗauke,
“ina momi?”
“ta fita koda na dawo ban ganta ba Yarima kawai na isko”
cikin rawar muryar kuka take masa maganar,
ido ya tsura mata tayi kasa da kanta hawayen na zuba.
candynovels.wordpress.com
© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*19*
ajiyar zuciya ya sauke ya ciro handkerchief ya kama fuskarta yana share mata hawayen “yi hakuri kinji bazan sake ba daina kuka”
kai ta ɗaga masa tana wani wahalallen numfashi,
kwantarda ita yayi saman kujera “wanta kiyi bachi?”
harta kwanta sai kuma ta ɗago ta kalleshi “yaya karka faɗawa momi kaji?”
kai ya ɗaga mata ya tashi ya fice.
takura kanta tayi saman kujera ta matse guri ɗaya kamar wadda aka cilasta tana matsar kwallah har bachi ya ɗauke ta,
''' * * * '''
*_2 hours letter..._*
can cikin bachi taji muryar momi da Siraj,
da sauri ta tashi tana soshe2.
Momi na kallonta taja wani dogon tsaki “haba Maryam ace mutum kana girma kana cin k'asa kamar ki ace inkin dawo makaranta ba kisan ki cire uniform ba saidai ki samu guri ki kwanta dubi kiga har lokacin islamiya ya wuce kuma baki san ki saka uniform kije ba”
ɓata fuska tayi “to momi ba fita kikayi ba kika barni”
nan momi kasa ce mata komai tayi dan takaici in banda tsakin data sakeyi ta nufi kicin,
momi na shigewa Siraj yaja mata kunne “ba wani daman baki son makaranta yar kauye”
fashe masa tayi kuka ta tashi tana aika masa mugayen duduna tana son huce haushinta akansa.
tsawa momi ta katsa mata “wuce ki cire uniform ɗin nan kiyi wanka kila ma ko abinci baki ciba?”
kai ta ɗaga
Momi tace “Allah ya shiryaki maryam wuce kije kiyi wanka duk kika sake yin abunda kikayi yau saina miki shegen duka”
kamar ta fasa kuka ta nufi stairs Siraj na zolayarta,
ta kusan minti 30 toilet ɗin tana wasa ruwa saida taji motsin momi a bedroom sannan ta fara wanka,
koda ta fito momi na zaune saman kujera tana duba wasu matirial da atanfofi.
kallonta kawai Mairo tayi ta nufi waduraf ta ɗauko wata atamfa red colour riga da saket tasa ko mai bata shafa ba ta janyo k'aton hijab ɗin momi tasa ta shimfiɗa carpet ta soma sallah,
momi na kalle da ita saida ta rama azahar sannan tayi la'asar.
bayan ta sallame ta cire hijab ɗin ta jefar saman bed ta nufi kusa da momi ta zauna,
“momi kayan waye?”
kyaleta momi tayi saida ta kare danne2 wayar da take sannan ta kalleta “na siyarwane”
shafa kayan ta shigayi “wlh momi suna da kyau suma siyarwa zakiyi?”
momi bata amsa ba ta kama hannunta ta kira sunanta a natse “Maryam”
dariya tayi “na'am momi”
“magana zamuyi ki bani hankalinki kinji banason kisa wasa ki daina dariya kinji?”
wani haɗe fuska tayi saida tasa momi murmushi sai kace wani cartoon ta wani tada kafaɗu “thom ina jinki?”
a natse momi ta soma mata magana yadda zata fahimta “maryam ki daina abunda kikeyi kinji ba kyau kinga kara girma kike ba ragewa ba ya kamata ki rika sanin ciyon kanki ki daina abunda kike”
“tho ni kuma momi mi nayi?”
ajiyar zuciya momi ta sauke “yanzu fa saida kika rama azahar sannan kikayi la'asar kina ganin kin kyauta?”
kai ta girgiza alamar a a momi tace “tho kingani wadda fa yake haɗa salloli azaba ake masa ba kyau ki daina kinji?”
nan ta ɗaga kai “kuma kinga in kika dawo makaranta maryam basai nace ki cire uniform ba ki rika cirewa duk abunda kika san aikin kine ki rikayi basai nace kiyi ba kinji? ki zama yarinyar kirki”
wata dariya ta rikayi tana kallon momi tana tsutsar leɓenta na kasa,
can dai ta kawarda fuska tace “tho momi na gane koma minene kike nufi”
shafata momi tayi “yauwa yata haka nake so kuma ki dage ki rika karatu ba wasa banda faɗa ko jan magana kinji?”
nan ma kan ta ɗaga ta tashi tsaye “nidai bari naje naci abincin yunwa nake ji”
bata ko tsaya jiran abunda momi za taceba ta fice.
tana saukowa downstairs Qasin na shigowa.
suna haɗa ido ta juya da sauri zata koma hannu yakai ya rikota “ya haka ina zaki?”
upstairs ta rika nunawa “ɗaki zan kwanta ne”
murmushi yayi yaja ta suka nufi kujera bayan ya zauna ya zaunarda ita “baki san ba kyau bachin maraice ba?”
“eh ni ban saniba”
“tho ba kyau ki daina karki sake bachi da maraice”
“tho na daina bazan sake ba”
idonta a kasa take amsa masa dan tsoron kallonsa take.
lura da hakan yasa ya sakar mata hannu yace “tsorona kike ko maryam?”
shiru tayi tana wasa da hannayenta fuskarta ya riko “faɗa min mana tsorona kike ne?”
ɓata fuska tayi ta soma magana “nidai bana son duka in mutun yana dukana tsoronsa nake sosai”
murmushi yayi “tho na daina bazan sake ba ai ban dakekiba”
“eh amman ai kaso ka dakeni dan dai anty mansura tazo ne ka kyaleni”
tana maganar tana wani langwashe langwashen kai da turo baki,
dariya yayi tace “ai ba mansura ce ta ceceki ba daman ba dukanki zanyi ba”
harara ta watsa mishi “kai wlh karya ne tho miyasa ka ɗaga dankon zaka buga min?”
“minene sanki?”
rufe ido tayi tace “wannan wadda kaso ka dakeni dashi”
“bel?”
kai ta ɗaga tana kara matse ido dariya yayi yace “ki yarda maryam bazan iya dukanki ba kawai dai horaki nayi”
kwanta masa tayi saman jiki tana dariya,
“wlh karya ne dukana kaso kayi”
kunnenta riko ya rika murɗawa “ni nake karya?”
dariya ta rikayi tana faɗin “na daina ba kaiba”
haka ya rika wasa da ita soma masa kuka sannan ya saketa ta nufi kicin shi kuma ya fice.
washe gari tunda safe Mairo ta shirya kanta duk abunda momi ta saba mata ita tayiwa kanta,
sosai momi ta jidaɗi da schoolbus ɗinsu tazo har bakin gate momi ta rakata ta buɗe mata motar ta shiga.
hannu ta rika ɗagoma momi har suka fice,
*_2:30pm..._*
ta shigo gidan da sallama ta shiga parlour momi ta amsa mata da fa'ah “wa'alaikissalam yar mama an dawo?”
kai ta ɗaga mata tana cire takalmin makaranta,
daga gurin da take zaune ta jefasu gurin da aka tana da dan ajeye takalmin tana faɗin “momi yau Yarima ya kai mana ziyara a makaranta”
Usman dake zaune kisa da momi yace “da gaske?”
“eh wlh harda chocolate ya raba mana”
momi tace “gurinki yaje ko makaranta gaba ɗaya”
“a a makaranta dai kofa jiya yaje kuma yazo gidan na-”
shiru tayi ta kasa karasawa sai rabon ido take. momi tace “jiya ya zo nan? bayan fitana ko?”
wata dariya tayi “ke momi na tuna mafarkine nayi ba gaske bane”
tashi tayi da sauri ta nufi upstairs “bari naje nayi sallah nayi shirin islamiya”
tanayi tana waigo momi harta shige.
momi kan daɗine ya isheta tana gani ta fara samun kan Mairo.
© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*20*
washe gari ma Mairo ita ta shirya ma kanta komai bayan ta saka safa ta riko schoolbag ɗinta ta nufo downstairs.
da dariya ta sarasa saukowa ta rumgume Qasin dake zaune saman kujera rike da laptop,
aje laptop ɗin yayi yana murmushi ya zaunar da ita saman kafafunsa “maryam har kin shirya?”
ɗagowa tayi tana murmushi “eh kuma ni na shirya kaina”
saukar da ita yayi jin motar makarantarsu ya karɓi jikar hannunta yasa mata,
da sauri momi ta fito kicin rike da kular abincinta tana faɗin “oya karɓi ga abincin ki naji motar ku”
da gudu ta karɓa ta nufi gurin da takalminta suke ta saka harta fice sai kuma ta dawo ta tsaya bakin kofa “momi ba zaki bani komai ba?”
“mi zan baki?”
shiru tayi tana bugun kofar parlour.
hannu Qasin yasa aljihu yana cirowa ya mika mata ɗari biyar,
wata dariya ta saki jikina na rawa ta karɓa tana masa godiya “na gode yaya” kai ya ɗaga mata ta fice da gudu.
ɓata fuska momi tayi tace “Qasin bana so karka sake ka ɗauki kuɗi har ɗari 500 ka bata”
hannu ya ɗaga “shi kenan na daina amman naga kamar bada yawa bane”
cikin faɗa momi tace “tho na dai faɗa maka bana so duk kyautar da ita karta wuce 100 zuwa k'asa”
tana kaiwa nan ta nufi kicin,
da sauri Qasin yace “owk momi yi hakuri ai ya wuce zo kiga wani abu?”
yi tayi kamar bata jishi ba shige kicin ɗin saida ta kare abunda take sannan ta fito.
har lokacin yana zaune ƴyana danne2 sa,
kujerar dake kusa dashi ta zauna “gani ya akayi?”
ɗagowa yayi ya kalleta “momi ɗan ruwan tea ma bazan samu ba?”
taɓe baki momi tayi “au daman jiran kake na ɗauko maka breakfast? inma shine dalilin zamanka nan tho tashi ka koma part ɗinka dan kasan munyi ba'ada dakai tun farko”
dariya yayi “a'a momi bashine ba abu zan nuna miki”
laptop ɗin ya ɗauko ya ɗora saman jikinta “kinga wani design ɗin wata kwangila da za'ah ba kanfaninmu”
duba momi ta shigayi tana faɗin “amman kan abun da girma sosai mi za a gina haka?”
“wani kanfani suke so a gina musu na sarrafa motoci _JAMES GLOBAL AUTOMOBILES_ sunan kanfanin shine na farko da zai kafa branch a Nigeria”
momi tace “aiko dasun kyauta muma mu ɗan samu cigaba kuma matasan mu su samu aiki”
“sosai ma momi kinga in aka ginashi mutun kusan ɗari biyar zasuyi aiki karkashin su kinga ai an ɗan rage kuma kanfanin sun iya motoci ana son motocinsu sosai sune zakiga J.G.A mutunin ɗan amerika ne”
momi tace “amman naji daɗi to kai zaka gina musu gurin ne?”
“tho haka ake tunani amman dai ba ni kaɗai bane mu uku aka kaimusu zasu zaɓa ne saisu bada kwangilar ga wadda suka yarda da aikinsa amman dai mutane da yawa ni suke cewa saboda kanfanin fitaccen kanfanine kuma muna aiki babu kissa ciki”
murmushi momi tayi “tho ai haka ake so Allah ya taimaka yasa ka samu”
“amin momi dan gaskiya zamu samu kuɗi masu yawa”
“to Allah ya yarda ya taimaka”
“amin”
tashi yayi rike da laptop ɗin yana kallon “bari naje can na karya”
kai momi ta ɗaga mishi “da yafi”
murmushi yayi ya fice.
*_7pm..._*
Mairo na zaune parlour kasan carpet ita da Siraj yana duba littafanta na makaranta sai zolayarta yake tana masa kuka yana sa ta karanta gurinda bata iyaba yayi mata dariya ita kuma ta buga masa fillo. suna haka sukaji an taɓa kofa duk juyawa sukayi suna kallon kofar,
cike da takama Yarima ya shigo ba tare da yayi sallama ba ya nufo gurinda suke,
wani irin haɗe fuska Siraj yayi kamar bai taɓa dariya ba,
wannan karon Mairo batayi unkurin tarboshi ba ido kawai ta sakar masa tana dariya.
da murmushi ya karaso kusa da ita tashi Siraj yayi tsaye da niyar tafiya tunowa da magagganun momi yasa ya kalli yarima yace “sannu da zuwa”
banza ya masa yana tsutsar lips ɗinsa.
juyawa Siraj yayi cike da bachin rai ya fice,
hannu Mairo ya riko yana murmushi ya nufi kujera suka zauna tare.
kallonsa tayi tace “ba kaji Siraj yana mska magana ba?”
lakatar mata hanci yayi “na jishi bana jin amsa masa ne”
murmushi tayi gyaɗa masa kai,
wasa ya shigayi da hannayensa yana faɗin
“pretty gal ya maranta?”
“lafiya kalau”
“ina momi?”
“tana ɗaki na kirata?”
hannu yasa yana taɓa lips ɗinta “a a karki kirata”
saida ya ɗaga kansa ya kalli upstairs sannan ya kalleta yace “gurinki nazo kinsan munyi dake zan saki abu ko?”
kai ta ɗaga “eh kuma kace zaka bani kuɗi kuna kace zak-”
rufe mata baki yayi da sauri jin motse saukowar mutun downstairs,
saida yayi mata alama da tayi shiru sannan ya juya da murnushi yana kallon momi.
“Yarima yanzu ake tafe?”
“eh momi ya wunin gidan?”
taka kokarin zaunawa tace “lafiya kalau maryam baki ɗauko masa abun sha ba?”
war tayi da ido tace “lahh mantawa nayi bari na ɗauko”
tana sauka ya riko hannunta ya tashi tsaye “a a momi barshi kawai yanzu zan wuce”
“da wuri haka?”
“eh kinga an kira sallar isha kuma daman biyowa kawai nayi naga Maryam”
da ɗan mamaki momi tace “owk tho a gaida gida”
hannu yasa aljihu ya ciro dubu 20 ya aje mata “ayi hakuri da wannan momi”
murmushi momi tayi “Yarima kenan Allah dai ya amfana”
baice komai ba yaja hannun Maryam suka fice,
motarsa ya buɗe mata ta shiga bayan ya rufe ya zagayo shima ya shiga.
“ina zamu?”
tambayar data fara jefa masa kenan tana kallonshi,
baice mata komai ba yasa hannu baya ya ɗauko laptop ya ɗora mata saman jiki “kinga wannan abun?”
“eh”
“kin taɓa ganinta?”
“eh sunanta kwanfuta”
mirmushin jindaɗi yayi “good wa kika taɓa gani da irinta?”
“malamin makarantarmu da yaya”
“tho kinsan mi nake ao dake?”
kai ta girgiza “a a”
“ta yaya nake son ki ɗauko min”
da sauri tayi waje da ido ta rufe baki “kaikai nidai babu ruwana baya so fa ina taɓa mishi kaya”
“ke mayarwa zanyi kawai inason na arane na ɗanyi wani abu sai na baki ki mayar”
lake kafaɗa tayi “a a gaskiya saidai nace ya aro maka”
haɗe mata fuska yayi “a a karki kuskura kice masa haka bazai bayar ba kuma inma yaji dukanki zaiyi kuma nima na ɓata dake”
hannu yasa ya ɗauko wata leda dake bayan ya mika mata “kinga kayan daɗi nan na siyo miki kuma gobe zan karo miki wasu kullum zan rika siyo miki kuma na baki kuɗi amman fa sai in kin aikata abunda nace”
shiru tayi tana tunani kamar ta fasa kuka ta kalleshi tace “amman inna ɗauko cewa zaiyi mi zanyi da ita”
“no ai bazaki bari ya gani ba a boye zaki ɗauko karki yarda kowa ya gani koda kuda ne”
“tho inna ɗauko ina zan ɓoye?”
shiru yayi yana kallonta kamin yace
“ke bakisan gurin da zaki ɓoye ba?”
“eh duk gurinda zan ɓoye gani za ayi”
“tho ki kaɗa rijiya”
“kai rijiya?”
“eh koki jefar wani gurin innazo sai ki faɗamin na ɗauko”
“ba zai lalace ba?”
“ba zaiyi komai ba kinji”
kai ta ɗaga mishi sosai yaji daɗi ya shafa kanta “good pretty gal”
“amman mi zakayi da ita”
idonsa ya shiga susa kamar wadda abu ya faɗawa “am zan ɗan ɗauki wani abune a ciki na cofa sai na baki ki mayar kinga bazai gane ba ko?”
da mirmushi ya karasa maganar itama tayi masa murmishin karfin hali,
kuɗi ya ciro masu yawa ya mika mata “gashi ki siye duk abunda kike so amman kinsan bazaki faɗawa kowa munyi wannan maganar dake ba ko”
“eh bazan faɗa ba”
“good kuma tsakanin gobe sa jibi nake son ki ɗauko min ita”
kai ta ɗaga mishi,
daga nan ya mika hannu ya buɗe mata motar shima ya buɗe suka fito tare.
Qasin na tsaye bakin kofa yana kallonsu yana rumgume da hannayensa fuskarsa a haɗe,
faɗuwa gaban Mairo yayi da sauri ta juya ta riko hannun Yarima ta soma kuka “nidai bazan iya zuwa ba ga yaya can yana kallona”
mirmushi yayi yaja hannunta suka nufi kofar parlour.
har suka isa Yarima bai kalli gefen da Qasin yake ba,
ita kadaice ke masa kallon tsoro jikinta har wani ɓari yake, da kansa ya buɗe mata kofar data shiga yayi mata byebye yana murmushi hannu itama ta ɗago mishi sannan ya rufe kofar,
yana juyowa Qasin yace “ka bani kunya ka kuma zubar da girmaka momi bata taɓa yiwa yayanta gurɓatacciyar tarbiya ba kuma bana tunanin za'a samu matsala a maryam dan haka ta banbanta da sauran matan da kake gani.
maryam karamar yarinya ce in zakayi sama kayi kasa ba za ah aura maka itaba balle baka daman lalata mata rayuwa dan haka banga abunda zai haɗaku ba”
yana kaiwa nan ya juya ya shigewarsa parlour.
kasa tafiya Yarima yayi sosai maganganun suka ɓata masa rai sai wani busar da iskar baki yake,
_ɗan iskane ni Qasin na karshe har yanzu baka gama sanina ba zan nuna masa true color na_
a zuci yake wannan zancen yana wani kashe ido.
candynovels.wordpress.com
[11/9, 6:53 AM] Khadeeja Candy: © *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
_na gode Sosai da k'auna yan *perfect women's*👌🏻 Allah barmu tare 😍 kaina a kasa maman husna & mrs tijjani much love😘_
*21*
Mairo na zaune kusa da momi tana nuna mata kuɗin,
Qasin na shigowa ta tashi tsaye da sauri tana masa kallon tsoro gabanta sai faɗuwa yake ganin yadda ya haɗe fuska,
yana karasowa kusa da ita ya fisgota ya jefar kasan carpet ya cire bel ɗinsa ya watsa mata,
wani ihu mairo ta saki ta durkushe guri ɗaya,
da sauri momi ta tashi ta rik'e "lafiya Qasin miya faru?"
kallon momi yayi rai a bace yace "bata jin magana ne momi so nake nayi mata dukan da in taga Yarima ko kallonsa ba zata sake yiba"
bel ɗin momi ta karɓe "miya faru wani abu tayiwa Yarima?"
"ba wani abu tayi masa ba shi daine yake son yayi mata illah"
kallon mamaki momi tayi masa "wani abun yayi mata ne?"
"momi kinfi kowa sanin halin Yarima ba mutunin kirki bane taya zaki rika barinshi yana keɓanta da maryam?"
sai a lsokacin moni ta gane inda ya dosa kallon maryam "Ke Tashi Kije ɗaki"
tashi maryam tayi ta gudu ta nufi stairs tana kuka.
saida ta shige sannan momi ta kalli Qasin tace "mi yasa kake da zafin zuciya haka ne Qasin?"
"ba zafin zuciya bane momi ina tsoron abunda zaije ya dawo ne kinfi kowa sanin halin Yarima saboda mi zaki barta ta keɓanta dashi ba ɗan'uwanta bane ba wani nata bane hasalima bashida wata alaka da ita ta dalilin mi zai rika bata kuɗi haka masu yawa kuma ki zuba ido kina kallo keda kanki kika ce bakison ina bata kuɗi mai yawa saboda karta lalace to akanmi zaki barta da Yarima?"
cikin faɗa yake maganar har jijiyar wuyansa na tashi,
kai momi ta girgiza tace "bana tunanin haka Qasin nasan waye Yarima"
wani murmushin jin haishi Qasin yayi ya fice,
a hankali momi ta kai zaune saman kujera tana nazarin kalamansa.
sai a lokacin wani tunanin ya soma bijiro mata,
ta kusan awa biu a haka sannan ta tashi ta shiga ɗaki.
*_washe gari..._*
Qasin na zaune garden ya wani aiki a computer yaji an dafashi,
a hankali ya ɗago suka haɗa ido da mairo da gefen