Showing 30001 words to 33000 words out of 85263 words
Chapter 11 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt
sai ita. kar dai ranta ya bache kana gudun bachin ranta amman ita bata gudun naka"
kallon mamaki yayi mata "momi muna zaine lafiya da ita fa ba muda wata matsala"
a hankaɗe momi ta kalleshi "na faɗa maka mansura ba mace bace Qasin har yaushe zaka san waye kai ne tunda mansura tazo gidan nan bata taɓa girka maka na safe da rana da dare kaci ba saidai ka siye takeaway koka zo nan kaci, wata hidima ta dangi bata taɓa tashi ta wanke kafarta taje ba bata taba shiga familinmu ba wani daga familinmu bai taɓa zuwa gurinta tayi masa kyakyawar tarba ba bata taɓa tako kafarta tazo nan part ɗina da sunan tazo gaidani ba matarka bata son haihuwa duk wannan bai taɓa damunka ba bai taɓa bata maka rai ba?"
da karfi momi take masa faɗan saida ya rumtse ido,
"mi yasa son mansura ya rufe maka ido haka Qasin? miyasa baka ganin laifinta baka son bachin ranta wanyannan abubuwan dana lissafa nasan suna damunka amman ka ɓoye saboda kar ranta ya bachi thobin kai ka jure ni bazan iya jurewa ba umarnine nake baka ba neman shawara ba kuma mun riga mu yanke shawara da babanka maryam zaka aura"
kallonta yayi da raunanniyar fuska "momi naji amman fisabilillahi a rasa wadda za a ce na aura sai maryam"
"kamar ya sai maryam
maryam ba mutum bace?"
kamar ya fasa kuka yace "momi kankanuwar yarinya ai kowa ma yaji dariya zai mun"
"kwarai za'a maka dariya kan tunda ka auro dodo ko aljana kamar maryam kake cewa kankanuwar yarinya shekara goma sha?"
tashi yayi tsaye yana kallonta yace "momi am more than 30 now taya kike ganin zan auri yarinyar da bata kai shekara ashirin ba?"
"tho abun kunya kayi ko saɓawa addini kayi Annabi (S.A.W) ya auri nana Aysha tana da shekara 6 aka kaita gidansa tana yar shekara 9 auren duk kuma abunda Annabi ya aikata Sunna ce ba akanka aka fara ba barre a kare kanka dan haka ni maryam nake son ka aura"
lumshe ido yayi ya buɗe "amman momi kona sureta hankalina ba zai taɓa kwanciya da ita ba ba zan taɓa samun natsuwa ba"
momi tace "saboda mi Qasin baka son tane?"
ya daɗe kansa a kasa kamin ya bata amsa "inason ta momi ina sonta sosai amman-"
shiru yayi ya kasa karasawa,
tashi momi tayi tana murmushi tace "ka zamo min ɗa Qasin bana son ka bani kunya mun riga mun kate magana da babanka kuma na sanar a kauye amincewarsu kawai muke jira mansura zaɓinka ce Qasin kasan ko kaɗan bana son aurenta amman na hakura saboda ka samu farinciki dan na fahimci kana sonta sosai tho nima inson ka farantamin ka auri maryam"
baice mata komai ba ya sauke ajiyar zuciya ya fice.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*32*
*_K'auye..._*
taliya ɗaya ɗaya Mairo take ɗauka tana kaiwa baki tana kallon Halilu Da Shima Taliyar Yake Ci Tana Dariya,
"wai lafiyarki mairo mikike dariya haka?"
Gwaggo ta tambaya cikin dariyar Mairo tace "Halilu ne yake bani dariya"
ɗagowa yayi ya kalleta "dariyar mie nake baki mairo?"
nan ta ɓata fuska "ni dan Allah ku daina cemun mairo nan a birni fa maryam ake cewa yafi daɗi"
Gwaggo tayo dariya "lallai mairo yanzu fa an waye ko ɗan zuwan nan da kikayi tho ai nan k'auye duk mai suna maryam mairo ake ce masa"
"ni dai gaskiya ku daina cemun mairo haka fa jiya su hawwa damary suka rika cemun mairo duk naji haushi"
Gwaggo tace "lallai xuwa birni yayi miki daɗi mairo an fara chanjawa ga kiba ga fari ni har maganarki naji ta fara chanjawa"
"ai dole Gwaggo kullum fa da nama muke karya wa da rana ma muci da dare ma haka ga kwai ga madara ga komai na daɗi ai dole nayi kiba"
wani guntun tsaki Halilu yaja "Gwaggo sai kace marar ido yanxu dan Allah ina kibar da mairo tayi nan daman can ai tanada ɗan jikinta saida kice tayi fari da ɗan girma koshi ba sosai ba"
leme baki Gwaggo tayi "ai kai daman ba son kake a ambaci abun alkharin taba"
murmushi yayi ya ɗauke kai
Mairo ta watsa masa harara tace "aiko Halilu duk wadda ya gannin sai yace nayi kyau nayi fari nayi kiba"
Gwaggo tace "ke fita harkarsa ai shi haka yake baya kaunar a ambaceki da alkhari saidai abunds zaisa ya rika dukanki yana shuri kamar an aiko shi"
mairo tace "aiko Gwaggo kinga ɗana je can ba duka ba komai"
ta karasa maganar tana yiwa Halilu gwalo,
hartatarar ta yayi "dan Allah gafara can ai bazaki koma ba"
"ai wlh sai na koma da hutun mu ya kare zan koma birni na barka nan dan yaro"
kwafa yayi "gani kike kamar wasa nake ko tho bari ki gani bazaki koma ba kowa yayi miki tsaye"
ganin da gaske yake yasa Gwaggo ta kallonshi tace "kamar ya bazata koma ba?"
"babu komai kawai dai bazata koma ba"
"koma warta aiko yanzu ma take dan mai dalilice za'ayi sai in abunda ake son k'ullawa bai yiyu ba kuma bama fatar haka"
ɓata fuska Halilu yayi "tho karma ku soma Gwaggo wannan haɗin da kuke son yi ba zaifa haɗu ba"
Gwaggo ta leme baki "sannu baba ba zai yiyu ba tunda kai ka haifeta wai miyasa baka son mairo ne Halilu? mita tare maka?"
"Gwaggo ba wai bana son cigaban mairo bane ko kaɗan babu wannan a zuciyata hasalima nafi kowa son cigabanta amman Gwaggo ina son ki duba wannan lamarin da kuke son haɗawa kwata² bashi da wata ma'ana"
rike baki Gwaggo tayi "bashi da ma'ana kamar ya nifa ban gane inda ka dosa ba?"
matsowa yayi kusa da ita ya sassauta murya "dan Allah Gwaggo karki yarda da abun nan dasu momi suke son hadawa wata kila ma wata cutace zasuyi ya za ace kamar mairo Qasin ya aure ta haba Gwaggo ki duba fa"
Gwaggo tace "ban fa gane maka ba Halilu ka fito fili kamun bayani yadda zan fahimta mana mi kake nufi ne?"
"Gwaggo taya za ace kamar Qasin yace yana son mairo? mairo tashin yaushe ce kuma yar kauye yaushe mairo tayi wayewar da har zaice yana sonta shifa digirine dashi kuma mai kuɗi ɗan birni.
kuma fa har yana da mata haba Gwaggo ki duba fa"
"tho in banda abunka Halilu minene aciki Qasin ɗan'uwanta ne ka kuma san inda wani abun cutane babu yadda za ayi babansa da mamarsa su amince har suzo tambayar in an basu kuma fa muma abunda muke nemane ya samu tunda kafi kowa sanin abunda uan garinnan suke cewa anki ayiwa mairo aure an kaita birin minene² kananan maganganu anyi kara anyi ice tho yanxu dan an bashi aurenta ai ba wani abun bane tunda ko ba shiba dole ne ai ne ayi mata aure"
"th tunda har haka ne ai kinga kara ma a aura mata wani ɗin ko ɗan gujewa masu cewa dan kwaɗayi aka kaita birni kinga yanxu ai sai su kara cewa wani abun in aka haɗa auren"
Gwaggo tace "babu fa abunda zai sa mu fasa haɗa auren nan duk kuma uban da bai zagemu ba bai haihuba dan an zagemu zagin lake mana zaiyine maganar banza"
da tsaki Gwaggo ta karasa maganar cike da bachin rai.
Mairo ta aje kwanon abincin ta matsa kusa dasu tana musu kallon rashin fahimta tace "mi kuke yiwa faɗa Gwaggo?"
tashi halilu yayi tsaye fuskarsa babu yabo ba fallasa yace "aure za'ayi miki mairo Qasin za'a aura miki"
da sauri ta nuna kanta tana kallon Gwaggo "ni?"
"eh ke aure za ayi miki mairo ai kinsan kin kai munzalin aure ai"
kamar ta fasa kuka tace "ni wlh Gwaggo bana son aure ni yar k'ank'anuwa dani za'ayi mun aure ga yan mata nan a birni manya dasu ba ayi musu aure ba sai ni"
hannunta Gwaggo ta riko ta zaunar da ita kusa da ita "mairo nan kauye ne ba birni ba kuma kinga mutane sai gulma suke suna faɗin anki yi miki aure"
"tho ni ina ruwana dasu nidai ma bana son hutun na fasa a mayarda ni gurin momi"
halilu yace "momi itace ta kawo wannan shawarar tace a aura miki Qasin"
shiru mairo tayi tana tunani, Gwaggo tace "karki ji komai mairo alkharine ake nema miki ba sharri ba kinga ma sai kiyi ta zamanki can birni kina yin yadda kike so, ko bakyaso?"
kai ta ɗaga "ina so Gwaggo amman nidai ina jin tsoro"
idonta cike da hawaye ta ke maganar.
nan Gwaggo ta shiga tallaɓata tana kwantar mata da hankali
ido halilu ya tsura mata kamin ya sauke ajiyar zuciya ya fice.
'''*****'''
"dan Allah Momi ku nemawa Nura admission a A.B.U Zaria nidai ganibnake kamar can yafi"
Usaman ne ke maganar yana kallon Momi dake zaune saman tree-setter tana cin abinci,
Momi saida tasha ruwa sannan tace "ni bana ra'ayin A B U nan nafi son State University nan da aka buɗa ance ana karatu sosai kuma kaga nan garin ne hankalina yafi kwanciya iddan yayana suna kusa dani"
dariya yayi yace "momi ni da nake ɗan fodio fa?"
"eh tho ai duka ɗaya ne tun cikin sokoto take nidai bana son ayi nesa ne kawai irin gari haka ko wata kasa"
"amman momi ai kinga yaya ba nan yayi karatu ba shi har kasar ma ya bari"
kafin momi ta bashi amsa aka turo kofar parlour,
juyowa sukayi suna kallon Yarima daya shigo cikin wata bugaggiyar shadda sky blue.
ba tare da yayi sallama ba ya nufo gurinda suke zauna hannayensa sanye cikin aljihu yana tsosar baki kamar mai shan sweet.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*33*
Saida ya kusa kawowa kusa dasu sannan yayi sallama Momi ta amsa mishi da Usman,
kujerar dake kusa da Momi ya zauna yana yiwa Usman wani kallon raini ciki² Usman ya gaisheshi, ba tare daya amsa ba ya kalli Momi yace "sannu Momi an wuni lafiya?"
da far'ah Momi ta amsa masa "lafiya kalau Yarima kana nan?"
"no shekaran jiya na dawo dan naje Uk ne tun ranar da muka fita da Maryam"
"Allah sarki tho ya gida ya da kowa²?"
shiru ya ɗanyi kamin ya bata "Lafiya kalau kowa yake"
juyarda fuskarsa yayi gurin tv, Momi ta cigaba da cin abincinta Usman ya tashi ya fice,
daf da zata cinye ya juyo ya kalleta "Momi ina Maryam?"
"Maryam ta tafi Kauye kasan anyi hutu ta tafi ganin gida"
shiru yayi ya ɗan ɓata fuska "yau kwananta 6 tun ranar asabar taje sai kuma hutu ya kare"
gefen fuskarsa ya shafa "oh Momi nako yi mata tsaba na ɗauka tana nan"
"da yake baka cikin garin shiyasa baka sani ba"
tashi yayi tsaye yana murzar zabban hannunsa "ni zan wuce kuma Hajiya tace na faɗa miki tana son ganinki"
Momi ta kalleshi "lafiya dai ko?" wani murmushi yayi "yo ni momi ya za ayi na sani sai dai kinje zakiji"
"tho shikenan sai gobe zanzo insha Allahu ka gaisheta"
kai kawai ya ɗaga mata ya fice yana kallon upstairs,
*_7:12pm..._*
"Assalamu Alaikum"
a hankali momi ta ɗago kai ta kalleshi tare da amsawa ciki² "Amin wa'alaikassalam"
suku² ya nufi kujera ya zauna kansa a kasa yace "Momi an wuni lafiya?" momi fuska babu tabo ba fallasa tace "lafiya kalau ya iyali?"
saida ya haɗeye yawu sannan ya amsa mata "lafiya kalau Momi"
gyaran murya momi tayi tace "Qasin in baka aikin komai inason ka kaini gidansu Hajiya yanzu ta aiko tana nemana ɗazu naso na ɓari har gobe kuma dai hankalina bai kwantaba nafi son yanje naji koma minene"
"wace Hajiyar Momi?"
kallon mamaki momi tayi masa "Auntie Hasana mana"
"Yarima yazo nan ne?"
"eh shine ya faɗa min ai"
tashi yayi tsaye yana faɗin "bari na kiran Siraj sai ya kaiki akwai inda nake son zuwa"
haɗe fuska momi tayi cikin tsawa tace "babu wani gurin da zakaje Qasin kawai ka fito fili yace baka son zuwa gidan iya isa ba sai kayi min nuku² ba"
lumshe ido yayi ya dafa kai "oh Momi baki fahimceni ba-"
hannun Momi ta ɗaga mishi tana tari numfashinshi "na fahimceka Qasin na san abunda kake nufi amman karka amta wannan Yarima ɗan'uwanka ne kuma inason ka sani bazan taɓa yardar maka ba ka ɗauki kiyayyah ka ɗora masa babu wani dalili nayin haka koba ɗan uwanka bane ai ba abun kwaraine bane ballantana ɗan uwa mi yasa baka da tunanine in kaje gidansu Yarima faɗuwa kayi shi da yake tako kafarsa har nan gurina fa,
ya fika sanin muhimmancin yan'uwan taka Qasin ya fika iya siyasa dan ko kiyayyah ce Yarima bai taɓa fitowa fili ya nuna maka ba ballantana ni har a zuciyata nasan Yarima baya kiyayyah dakai"
komawa yayi ya zauna ya kama hannayen Momi ya rike cikin sanyayyiyar murya ya shiga mata magana "bana kishin Yarima ko kaɗan Momi bana kishinsa kawai dai halayensa ne banaso kuma momi bazan taɓa yarda na faɗa a gadar zaren da yake kullamin ba momi kinfi kowa sannin waye Yarima kinsan duk inda ya ganni ko yaga wani dags cikin familinmu sai ya musguna masa kodai ya faɗa masa gana mara daɗi ko kuma yayi masa wani abun na bachin rai ni kuma na tsani haka momi saboda babu abunda Yarima zai nuna min
sannan momi kin hana na rama momi kince Yarima ɗan'uwana ne nasani shiyasa ma nake ɗaga masa kafa amman momi kinsan Maryam ma yar'uwata ce ko kuma duk abunda ya sameta ya sameni bazan taɓa mantawa ba"
lumshe ido momi tayi ta sauke ajiyar zuciya a ranta tana _...ba zaka taɓa ganewa ba Qasin..._
can ta buɗe idon ta kalleshi tace "naji zaka iya tafiya"
"momi ki shirya na kaiki mana"
"a'a sai goben kafin ka fita"
"momi kar kimun rashin fahimta bana nuf-"
numfashinsa ta tara tare da tashi tsaye "a a Qasin na fahimtace ka karka damu gobe zaka kaini"
bata tsaya jiran mi zai ce mata ba ta nufi stairs,
Momi na shiga ta tararda wayarta saman madubi tana ringing da sauri ta karasa ta ɗauka Hajiya ta gani a screen kamin ta ɗanna picking ta kara a kunne,
_"Amin wa'alaikissalam Hajiya ya gida?"_
banji mi akace mata ba na daiji tace _"eh ina gida lafiya dai?"_
_"tho sakin iso"_
sauke wayar tayi gabanta na ɗan faɗuwa tana mamakin abunda yasa Hajiya take son ganinta haka.
*_© Khadeeja Candy_*
[11/5, 9:43 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*34*
*_9:35pm..._*
Hajiya ta iso gidan tun kamin ta fito mota momi ta fito ta tareta cike da far'ah, rumgume juna sukayi kowane na dariya suka shigo parlour,
momi bata barta ta zauna ba suka nufi bedroom drinks kala² momi ta jere mata da kayan ciye² bayan ta zauna suka ɗauko firar yaushe gamo,
can momi ta kalli Hajiya tace "nifa Hajiya ina mamakin zuwan nan naki haka kawai"
murmushi Hajiya tayi "ba zuwan haka kawai bane maman Nura ɗazu ai nayiwa Yusuf sako ya faɗa min kince sai gobe zaki zo shiyasa ni kuma na kasa hakura har goben nace bari nazo yau"
"nima ai na tashi zuwa ɗazun bayan magriba sai kuma nace bari dai na bari har goben lafiya dai ko?"
Hajiya ta dafa momi "lafiya kalau ɗanki ne yaga wata yarinya yace yana so"
farincikine ya bayayyana a fuskar momi duk da faɗuwar da gaban ta yake "masha Allahu ba dai Yarima ba?"
"shifa ai nima farinciki kasa ɓuyiwa yayi a gareni kuma yace nazo na tambaya masa shine fa nace tho ya kira min daya faɗa min kince sai gobe ni kuma na kasa hakuri"
momi tace "ai dole abunda aka ta jira shekara da shekaru nima ai na jidaɗi sosai"
Hajiya tace "yace yarinyar tana nan gidan ke kike rikonta yace mun sunanta maryam"
wani irin gaɗuwa gaban momi ya karayi shiru momi ta ɗanyi kamin ta haɗe yawu tace "maryam Hajiya?"
yanayn yadda tayi maganar yasa Hajiya ta kalleta "eh ita koda matsala ne?"
"a'a ba wata matsala kawai dai naga yarinyar karama ce dan bazata wuce 13 ba"
murmushi Hajiya tayi "kar wannan ya dameki ys faɗa min daman karamar yarinyace har yake cemin kiyonta yake sai ta girma tukuna tho shekaran jiya nida Mai Martaba muka sashi gaba muna masa faɗa mishine fa yake faɗa min shi babu yarinyar da yakeso inba ita ba sai kinga yadda mahaifinshi yayi murna"
momi jiki ba kwari tayi murmushi tace "ai dole kan abunda kowa yske mafarki nimaai nayi farinciki"
Hajiya tace "ina kika sani nima daɗin nake ji kamar me shine babbah yanzu kingaya kamata ace yanzu yayo aure kanensa na biu fa yanzu za ayiwa aure shi yasa ma ai abun ya damu mai martaba yasa yayi masa haka dan cewa yayi im bashi wadda yake so tho shi zai mema masa duk wadda yaga dama shine fa sai ya faɗa mana ita kaɗai kawai yake so dafa duk akayi magana sai yace shi bai samu wadda yake so ba kinga sai yanxu Allah yayi"
ajiyar zuciya Momi tace "kinsan komai yana da lokaci wata kila sai yanzu Allah ya kaddaro za ayi saida fs hajiya wani hanzari ba gudu ba"
kallonta Hajiya tayi "ina jinki minene?"
"its maryam ɗin yar kauye ce kuma ba tsyi wani karatu ba dan zuwannan ma da nayi da ita Qasin ya sata makaranta"
"kar wannan ya dameki duk ba matsala bace tho da dai har yace yana so ai duka ɗsys muke gurin Allah babu wadda yafi wani"
lumshe ido momi tayi ta buɗe ta kallii hajiya tace "shikenan zanje kauye sai nayi masa magana dan yarinyar ma tana can hutun na da akayi sai na kaita ganin gida"
"wai yar insce?"
"wlh kanwar su Qasin ce yar kanne mahaifinsu da mukaje kauye sai muka zo da ita......"
"tho yanzu dai kije kauyen ki nema masa"
cikin karfin hali momi tace "insha Allah haka za ayi"
hajiya tace "ki faɗawa mai gidanki dan ni cikin satin nan nake son aje inma ta kama har dani duk sai muje koda da Mai Martaba ne"
"a a ni ma ai ns isa na nema masa ba sai kunjeba inma dolene kuje ai sai na faɗa muku amman sai in babansu ya dawo dan yayi tafiya"
murmushin jindaɗi Hajiya tayi "ai ba matsala bace Allah ya dawo dashi lafiya ana nan anata harkokin business ɗin ko? ba hutu"
"eh ai shi koyaushe baya samum zama gida neman kuɗi kawai aka sawa gaba ba a nan ba a can zamansa gida kaɗsƙan ne kuma a koma"
"tho mai sa akan ai daman bai gaji zamaba musamman in akwai iyali"
haka momi tayi ta smsa mata firarda suke kamar marar lafiya sai kusan 11 da wani abu ta bar gidan,
daren momi kasa bachi tayi tana tunsnin yadda zata billowa lamarin, har a ranta Qasin take son maryam ta aura sai kuma yanzu dabo biu ziciyarta take mata akan