Showing 84001 words to 85263 words out of 85263 words
Chapter 29 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt
sannan ya fito tare da wasu manyan likitoci, saida ya shiga wani ɗakin ya cire kayan daya fito dasu daga ɗakin tiyatar sannan ya nufo gurin su Momi.
A fuskarashi Momi ta karanci abinda ke bakinshi, da murmushi ya k'arasa yana kallon Momi da ita murmushin take idonta da hawaye.
“Anyi nasara Momi babu sauran kuka sai dai ayi adduu Allah ya bashi sauki"
Godema Allah Momi ta dinga ita da Mansura da sauran yan uwa da suke gurin,
Murmushi Siraj yayi ya nufi k'ofar ɗakin da aka chanja ma Qasin, a nan ya tararda Yarima tsaye hannayenshi sanye cikin aljihu,
Uffan Siraj bai ce mishi ba sai ma kauda kai da kuma yayi, murmusawa Yarima yayi ya mik'a mishi hannu yana faɗin “Congratulations Siraj"
Hannun nashi Siraj ya kalla sannan ya kalleshi “Banyi zato wannan daga gareka ba so tell me minene sirrin?"
Murmushi Yarima ya sakeyi yace “Babu komai Siraj kuma bana so ka sake daukata cikin makiyan Qasin no more"
Fuskarshi Siraj ya k'urawa ido nan Yarima ya k'araso kusa dashi ya dafashi “Siraj abinda ya samu Qasin ya karantar dani abubuwa da yawa just look at him da ace mutuwa yayi da yayi kyakkyawar cikawa kowa yana kuka da rashin shi ni kaina ban taba jiya n abinda naji game Qasin ba irin wadda na daga jiya zuwa yau,
Siraj Qasin yana da farin jini gurin kowa ba kuma komai ya jawo mishi wannan ba face kyakkyawar mu'amala da kowa"
Sukuku Siraj yayi yana kallonshi kamin yace “Yarima kaine da kanka kake wannan maganar?"
“Nine Siraj ina nadamar abinda nayi ma Qasin da ace ya mutu da bansa ya duniya da mutane zasu kalleni ba bansan abinda zan fadawa ubangijina ba"
Ajiyar zuciya Siraj ya sauke yace “Idan har da gaske kayi nadama ba afurincika kawai za'a gani ba a aikace za'a gani Yarima zanfi kowa jindaɗi idan ka zubarda duk wani mummunan hali nake ka chanja rayuwarka ka maida kanka ba kowa ba,
Mulki fa ba ya dawwama kamar yadda sarauta bata dawwwama dole ne ka barsu ko su barka shin idan da tunani mutuwa miya zau kawo girman kai da ɗagawa baka fi kowa ba a gurin Allah kuma babu wadda ya fika sai wadda yafi wani tsoron Allah,
idan har da gaske ne toh zanfi kowa farin ciki da haka"
Yarima yace “Inason ka zubarda duk wani kallo da kake mi na marar kyau hali ko kuma wadda zai iya cutar da kai ina son mu koma normal bida Qasin"
Murmushi Siraj yayi “Nima zanso haka sai dai har yanzu gani nake kamar ba Yariman dana sani bane"
Murmushi kawai yayi ya juya yasa hannun shi aljihu ya nufi kofar da zata fitar dashi daga gurin gaba ɗaya,
Da ido Siraj ya bishi har ya fice,
Kai tsaye gida ya nufa gurin hajiya,
Parlor ya sameta kishingiɗe ita da bak'inta suna fira, tana ganin shi ta zaune yana kallon shi.
'Daya bayan ɗaya ga bisu duk sai da ya gaishe su, sannan ya nufi cikin ɗakin,
Ba Hajiya ba har ba har su saida sukayi mamakin abinda yau Yarima yayi musu abinda bai tanaɓa.
Tashi Hajiya tayi ta tufa mishi baya zuciyarta cike da tambayoyi ta shiga ɗakin,
Yana ganinta ya sakar mata murmushi "Hajiya ta?"
“Na'am Yusuf"
Sai ta zauna sannan tace “Ka chanja Yarima fiye da yadda nake tsammani ka fara zama yadda nake mafarkin zaka zama"
“Yafiyarki nake nema nasan na ɓata miki da yawa"
Kai ta girgiza mishi tana murmushi “So nawa kake so nace na yafe maka Yusuf? Na faɗa maka nida Mai Martaba tuni muka yafe maka babu sauran ɓacin ranka cikin ranmu"
Dukawa yayi har k'asa yace “Hajiya ina neman wata alfarma agareku?"
“Ka faɗi ko minene zanyi maka shi Yarima"
“So nake ku zaɓa min matar Aure keda Mai Martaba"
Wani irin daɗi Momi taji sai kawai idonta suka cika da kwallah.
“Na gode Yusuf Allah yayi maka albarka zamu zaɓa maka matar data dace da kai In'sha Allahu"
Tashi yayi tsaye ya rumgume ta ya lumshe ido.
*Wannan kenan*
***
Ranar da Mairo ta cika sati ɗaya da haihuwa yaro yaci suna Yusuf sunan Yarima akayi mishi lak'ani da little Yarima sosai Yarima ya jindaɗi karku so ganin irin kayan da yayima jariri da uwar shi,
Aɓangaren su Momi basai na faɗa muku irin kayan barka da ta zuba ita da mutanenta ba dan kusan hausawa sunce abu namu.....
Su Gwaggo kan bana cewa komai dan nasu farin cikin baya faɗuwa,
*** *** ***
Ciyo ne yake zuwa nan take amman Lafiya sannu-sannu take Shiga haka Qasin ya cigaba da jinya yana samu kyakkyawar kulawa daga ɓangaren mtanshin da kuma Momi, Yarima da Hajiya ma ba baya ba kusan kullum sai yajs Asibitin har ya samu sauki aka sallame shi,
Ranar daya dawo gida Mansura da Mairo kamar su zuba ruwa k'asa su sha dan murnar, anan gasa ta shiga tsakaninsu kowace ta rik'a k'ok'arin ganin ta kyautata mishi kuma suka haɗa kansu kamar babu abinda ya taɓa shiga tsakanin su,
Bayan wata hudu da sallamar Qasin daga Asibiti aka ɗaura Auren Yarima da Amaryar da Hajiya ta zaɓa mishi yar wani tsohon kwannan katsina,
An zubarda nera tsayawa faɗa muku irin shagulgulan da akayi a biki ɓata lokacine, manyan mutane suka halarci bikin ta ko ina.
***
Bikin shi da wata biu akayi na na Siraj da Amaryar shi a Abuja akayi komai can ne Mansura ta ziyarci wata Asibiti mai zaman kanta dan a duba mata lafiyar mahaifarta.
Duk wani bincike da ya dace saida likitocin sukayi sannan suka tabbatar mata da bazata iya ɗaukar ciki ba dan mahaifarta ta lalace sosai ta yadda bazata iya rikon ciki ba,
Bakin ciki Mansura tayi sosai tayi dana Sanin abinda tayi.
***
Little Yarima nada shekara da wata biyar Mairo ga sake samu ciki. Murna gurin Momi da Qasin ba'a magana, Qasin kamar ya haɗe ta dan farin ciki.
Cikin jindaɗi ta kwanciyar hankali tayi fa rainon cikinta har ya girma ta haifo yan biu duk mata, aiko lokacin ne Qasin yace bata ga komai ba indai so da kauna ne yanzu na fara nuna mata shi.
Mairo tayi sani fari tayi bulbul gwanin shawa'awa Mansura ma ba bayab dan duk wani bacin rai nata aje shi tayi gefe suka rika juna ita da mairo kamar ba kiyashi ba ba zaka gansu kace wani abu ya taba shiga tsakanin su ba,
Aɓangaren Yarima ma ba shida wata matsala shida matarshi farin ciki ne da jindaɗi kawai a gidan duk wani hali nashi marar kyau ya zubar suka koma shi da Qasin kamar AMINNAN JUNA, Momi tafi kowa farin cikin ganin halin da su Qasin da Yarima suke yanzu,
Ita da hajiya suka koma kamar yadda suke da komai normal.
Suka shiga wata sabuwar rayuwa mai cike da jindaɗi.
TAMMAT BIHAMDILLAH!
Oh Allah hope for your mercy. Do not leave me for myself. Correct all of my affairs for me.
Anan na kawo karshen wannan littafin mai suna MAIRO kurakuran dake ciki Allah ka yafe min yar karamar faɗakarwa dake ciki Allah yasa mu anfana da ita, duk da ba a nan naso na tsayawa amman ku kuka hanani kashe Qasin 🤷🏿♀.
SPECIAL THANKS TO
Nagarta writter's Association
W. A. F Association
Tsintsiya writers Association
And some of my co_Writer's
Love you all my fan's and readers Allah ya haɗa mu da alkharinsa
Amin.
*KHADIJA ABUBAKAR ALK'ALI CE👌🏿*
KE MUKU BISSALAM 🙌🏿