Showing 9001 words to 12000 words out of 85263 words
Chapter 4 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt
Mairo amman hakan bai hanata farkawa a firgice ba.
“k'arɓi ga abinci kici saiki kwanta”
kin k'arɓa tayi ta tsurawa Momi ido can kuma ta mayarda su gurin abinci.
sakwarace da miyar agutsi da namomi hannun tasa ta k'arɓa “ni bazan iya cinyewa duka ba”
“ci kibar saura”
kusa da ita Momi ta zauna tana amsa waya.
saukowa Mairo tayi kasa ta hau cin abinci
cikin yan mintuna ta kare ta tashi tana suɗar miyar dake plate ɗin duk ta ɓata gurin da miya kamar mai ɓararen baki.
nunawa Momi hannunta tayi “na kare ina zan wanke hannuna?”
toilet Momi ta nuna mata
tana gyaran ɗaurin tawul ta shiga toilet ɗin
koda ta fito Momi ta gyara gurin tana mopping
tsaye tayi har momi ta kare ta nuna mata gado “hau ki kwanta”
ba musu ta hau Momi taja zanen rufa ta lulluɓa mata.
ta kashe wutar ɗakin ta kunna ta bedside lamp ta nufi kofa,
Mairo na ganin zata fita ta tashi da sauri “ni kaɗai zaki bari nan?”
Momi daga gurin da take tsaye tace “tsoro kike jine?”
“eh bazan iya kwana ni kaɗai ba”
“babu abunda zai sameki ki kwantar warki kiji?”
“aa ni bazan yarda ba”
saukowa tayi ta nufo Momi.
Momi tace “to bari na kunna miki wutar saiki kwanta kamin nazo yanzu zan dawo jeki kwanta”
lake kafaɗa tayi “a a ni bazan yarda ba”
tsawa momi ta katsa mata “wuce kije ki wanta nace”
jiki na ràwa Mairo ta faɗa saman gado ta ɗanne fuskarta cikin katifa,
Momi na ganin haka ta taja kofa ta fice
kuka Mairo tayi tayi kaɗankaɗan kuma ta kasa ɗago kan dan tsoron kar taga wani abu har bachi ya ɗauketa.
*_washe gari....._*
tunda asuba Momi ta tada Mairo
a firgice ta farka jikinta sai rawa yake hannun momi ta rika suka shiga banɗaki tare sukayi alwala.
bayan sun fito Mairo ta nufi yar zakarta ta zazzage ta ɗauki wata atamfar kauye tasa tare da hijab ta fara sallah,
tana sallamewa komai bata tsaya yiba ta koma bachi.
sai 8 da minta ta farka koshi dan siraj ya tada tane.
da murje murjen ido ta tashi tana mik'a idonta a lumshe tana soma kiran gwaggo.
“ke tashi momi na kiranki nace”
‘to’ tace tana turo baki kamar ta fasa kuka
shidai bai tsaya jiranta ba ya fice,
saida ta gama gunguninta sannan ta tashi ta nufi kowa duk jin take bata son gidan,
tana fitowa ta hango farlo down stairs.
wani irin ihu ta saki saboda juwa data gani tayi bayabaya tana kiran “na shiga uku wayyo Gwaggo na bani mutuwa zanyi”
duk kai suka ɗago sun Kallonta daga dining area siraj ne ya fara tambaya “lafiya?”
cikin kuka tace “na bani bazan iya saukowa ba na shiga uku Gwaggo”
duk fashewa sukayi da dariya banda siraj da yaja tsaki sai kuma Momi data hau mata faɗa “ke wai wane irin iskancine dake haka haka kawai zaki rika yiwa mutane uhu”
Qasin dake tsaye ya kalli Momi yana murmushi “tsorone taji momi kinsan yar kauye ce”
“to dan taji tsoro sai tayiwa mutane ihu iskancin da takeyi can kauye nan bazan ɗauke shiba”
tea cup ɗin dake hannunshi ya aje ya nufi up stairs.
hannunta ya riko ta rumgumeshi iya karfinta ta kulle ido gam sannan suka sauko.
har suka isa dining bata buɗe idon ba saida taji an zauner da ita sannan ta buɗe ido tana kare musu kallo,
da Qasin ta fara sannan Usman, Siraj sai kuma ta juyo gun Nura.
kofin tea Momi ta aje mata idonta cike da hawaye ta ɗauka ta kai baki
bata ajeba saida tasha rabin kofin Siraj da Nura da Usman sai dariyarta suke Qasin Murmushi yayi ya kalli agogon hannunsa yace “Momi ni bari na wuce gurin aiki”
“to Allah ya tsare”
“Amin”
saida ya kara kurɓa tea ɗin sannan ya fice.
Usman ya kalli Mairo yana driya yace “bakison bredin hala?”
banza ta masa har Momi ta kare cin abincinta da Usman suka tashi.
sannan ta ɗauki bredin tana hawaye ta rika somawa kamar turo da miya tana ci.
© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*10*
Siraj dai sai kallonta yake can yaji bazai iya zurewa ba yace “wai mi kike yiwa kuka?”
cikin kukan tace
“ni gida nake so”
dariya yayi “gida?”
“eh”
“mi aka miki to?”
“bana son gidan nan bana son gida a sama kuma mumi faɗa take min”
fashewa sukayi da dariya Nura yace “hala baki taɓa ganin gidan sama ba?”
“eh nidai bana sansa”
tashi nura yayi yana faɗin “amman gaskiya kauyancinki yayi yawa”
k'ara turo baki tayi kuka nason fito mata fili Siraj dai kallonta kawai yake har ya kare cin abinci ya tashi,
Mairo tasowa tayi ta dawo kusa da doguwar kujera dake parlour ta zauna har lokacin hawaye take.
jin tafiyar momi yasa ta ɗago kai tana kallon up stairs “lafiya kike kuka?”
fuskar momi a haɗe take mata tambayar
“gida nake so gurin Gwaggo”
murmushi momi tayi “karya kike yi ai ke kika dage saikin biyomu jiya jiya muxo yau kice a kaiki gida babu yadda bayiba akan ki zauna kika ki”
hannayenta ta haɗe tana rokon momi
“na daina mumi bazan sake cewa a zo dani ba”
“uhmm tashi muje kicin kiyi wanke wanke”
lake kafaɗa tayi “ni ban iya wanke wanke ba”
kunneta momi ta kamo “ke bari kiji na faɗa miki iskancin da kike can kauye nan bazaki min shiba”
kuka Mairo tasa sai kiran Gwaggo take.
haka momi taja hannunta suka nufi kicin.
gurin wankewanke momi ta nuna mata ta “oya sa hannu ki wanke” kallon momi tayi idonta cike da hawaye tace “wlh ban iya wanke wanke ba”
“dukanki dai kikeso nayi kamar zakice baki iya wanke wanke ba kuma rikon kauye ba birnin ba koki wanke shi ko na miki dukan tsiya” momi na kaiwa nan ta juya tabar kicin ɗin,
haka Mairo ta hau wankewanke tana kuka
sama take wankewa dan har ga Allah bata iya ba tunda Gwaggo bata sata aikin komai inba sharaba koshi inta ga damane take yi.
haka ta wankesu samasama kofukan da akasha tea ma ɗaurayisu kawai tayi ta aje,
koda ta kare ta fashe tea cup ɗaya kuma duk ta ɓata gurin da ruwa ɗan kwalinta tasa ta goge ruwan ta jefashi bayan firjin.
jikinta a sanyaye ta nufo parlour tsaye tayi tana kallon momi dake zaune saman kujera.
ganin bata kula taba yasa ta karaso kusa da ita “na kare”
sai lokacin momi ta kalleta “to wuce kiyi wanka”
“ina?”
“inda kika ga na miki jiya”
lake kafaɗa tayi tayi baya baya “ni bazan hau sama ba gaskiya”
taɓe baki Momi tayi ta cigaba da kallon tv.
*****
ranar Mairo wuni tayi tana kuka saboda faɗan da momi tayi mata kuma ta hana mata abincin rana saboda takiyin wanka.
da magariba Mairo na gefen kujera zaune Momi ta nufi kofa da sauri Mairo ta tareta tana “ni ki bani abincina yunwa nake ji”
tureta momi tayi saida ta faɗi wani mahaukacin ihu ta saki momi saida ta rufe kunnuwanta ta hau shurenta.
“lafiya?”
Qasin na shigowa abunda ya fara tambaya kenan
momi ta nunata da yatsa “rainin wayo ne da ita so nake na gyara mata zama”
karasawa yayi ya tada ta “mi tayi momi?”
“iskancin da take can kauye ne take son tamun”
kallon Mairo yayi “mi kika mata?”
cikin kuka Mairo tace “ban mata komai ba muguwace azzaluma ƙk'atuwar banza kuma ban yafe miki b-”
da sauri Qasin ya rufe mata baki “ke karna sake ji ba mamanki bace”
kai ta girgiza tana hawaye “ni ban sonta ba mamana bace”
kwafa momi tayi “aiko kashinki ya bushe cikin gidan nan”
“wai minene mafarin wannan abun ne momi?”
momi tace “rantsuwa nayi duk batayi wanka ba bazan bata abinci ba”
kallon Mairo yayi “ke mi ya hana miki wanka maryam kin fi son ki zaina da k'azanta?”
“a a itace tace saina hau saman sama sannan nayi wanka ni kuma tsoro nake ji”
kallon momi yayi yana murmushi “kinji momi tsoro take ji kinsan ko ɗaxun saida aka saukarda ita”
“ba wani tsoro iskancine kawai”
“ba iskanci bane ko?”
ya tambayi Mairo kai ta ɗaga yace “bata hakuri sai kuje tayi miki wanka kuma karki kara rashin kunya kinji”
saida ta daɗe sannan ta kalli momi kasa2 tace “yi hakuri bazan sake ba”
da ita da dashi duk tsurawa momi ido sukayi sunajiran abunda zatace
saida ta watsa masu harara sannan ta fixgi hannun Mairo suka nufi up stairs.
kankame momi Mairo tayi ta rumtse ido nan momi ta sakar mata hannu “wuce da kanki”
kuka tasa nan momi ta katsa Mata tsawa dole ta rike karfen ta rika hawa da rumtsen ido har ta haye.
momi ce tayi mata wanka Mairo kan ana mata wanka tana tunanin yadda za ayi ta tsera ta gudu ta bar gida,
bayan sun fito momi ta wulgo mara kayanta ta sauka downstairs ta ɗebo mata abinci.
*_washe gari....._*
tun asuba momi ta tada Mairo bayan sunyi sallah bata barta ta koma bachi ba suka nufi kicin.
tare suka haɗa komai na breakfast ranar momi batayi mata faɗa ba dan tare sukayi komai duk da ba wani iyawa tayi ba daman momi abunda bata so ta saka aiki kaki da kuma kuka.
*_8:30am....._*
suka kare hada komai momi ta nunawa Mairo gurin da zata jera.
ba musu ta rika jera abinci badan ranta yaso ba sai dan gudun matsifar momi aranta kan ɗebima momi albarka kawai take tana aiban ta'ta.
Mairo ce ta fara zama bayan ta jere breakfast ɗin sannan momi,
Usman da Nura dake zaune saman kukera suka nufo dining.
Siraj sai janta yake ita kuma ta wani haɗe fuska kamar ta fasa kuka .
momi da kanta ta zubawa Mairo breakfast su kuma suka shiga zubawa kansu.
Nura ya kalli Momi yace “yau yaya ba zai karya nanba ?”
momi tana k'ok'arin zuba ma kanta tace “zaizo mana ai kasan nan yake karyawa kila bai tashi bachi bane”
kamar daga sama sukaji an banko kofar parlour duk juyawa sukayi suna kallon Qasin daya shigo fuska a haɗe.
yana karasowa momi tace “lafiya?”
takardun dake hannunsa ya nunawa momi cikin zafin rai yace “kwangila ce Yarima yakai a kanfaninmu”
murmushi momi tayi “wow...-”
tare numfashinta yayi ya juyarda fuska “haba momi kamar bakisan Yarima ba he just want to ruin my life kuma deal ne between me and him saina gani tsakanin ni da shi who is going to be loser”
tashi momi tayi ta daga hannunta da niyar yi masa magana sai kuma ta kasa jefarda takardun yayi ya fice cike da bacin rai.
*HAPPY JUMMA'AT MUBARAK.*
_i Really Need Your Prayers fans Ina Ciyon Zuciya_
© *Khadeeja Candy*
[11/9, 6:52 AM] Khadeeja Candy: © *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*11*
sanyi jikin momi yayi ta kasa kai komi bakinta Nura da Usman ne kawai suke cin abinci shima Siraj ya damu sai kallon momi yake,
tashi momi tayi ta nufi gurin daya watsarda takardun ta shiga haɗawa.
saida ta haɗesu guri ɗaya sannan ta kalli Siraj daya juyo yana kallonta tace “Siraj jeka kiran min yayanku”
kai kawai ya ɗaga mata ya tashi ya fice.
Mairo dai sai satar kallonsu take tana tsomen beredi,
guri momi ta samu ta zauna dafe da kai kamar mai mata ciyo.
tana haka Qasin da Siraj suka shigo dining Siraj ya nufa Qasin kuma ya nufota yana faɗin “gani momi”
kujera momi ta nuna masa har lokacin tana ɗafe da kai.
bayan ya zauna ta kalleshi tace “Qasin ka rika hakuri kasan da wadda kake zama Qasin ni bana tunanin saboda ɓata maka suna ko karyarda kai Yarima ya ɗauki kwangila ya baka”
kawar da kai yayi alamar bai jidaɗin maganar ba.
ganin haka yasa momi ta taso ta dawo kusa dashi ta zauna “Qasin ni a ganina kamar ma Yarima yana son ɗaukaka kanfaninku ne”
juyowa yayi ya kalleta “a a momi so yake ya karya ni kawai kuma bazan taɓa yarda da wannan kwagilar ba ba zai taɓa cinma burinsa a kaina ba”
dafashi momi tayi “ban sanka da zuciya haka ba bana son ka runtse ido ka yanke hukuncin da zai zamar maka nadama nafison ka yanke hukunci ido a buɗe
bana son abunda zai saka cikin matsala Qasin”
kallon momi yayi yana nazarin kalamanta can ya lumshe ido ya sauke ajiyar zuciya ya sake buɗe idon yace “momi banida mafita sai wannan momi bana son Yarima yayi nasara a kaina momi ki duba min plz”
itama Momi ajiyar zuciya ta sauke tace “baka ganin mayarda kwangilar zai zame maka matsala?”
“zai iya zama kan dan lokacin da zai bada kwangilar tare da yan jarida yazo”
“to karka kuskura ka mayarda kwangilar zai zubar muku da mutuncin kanfani”
“momi ba nida wata mafita sai wannan”
“haba Qasin sai kace kai ba namiji ba kai bakasan yadda zaka sarrafashiba ka bashi kunya ka taka abunda ya taka Qasin ka zama gawurtaccen namiji ba rago ba”
Siraj da tunda ake maganar hankalinsa na gurin tasowa yayi yana faɗin “yes yaya kaima namijine ka ya k'eshi ks kara ɗags martabar kanfaninka kabi shawarar momi plz”
ajiyar zuciya Qasin ya sauke a karo na uku ya kalli momi “momi ba hannuna da nasa ya bani kwangilar ba PA ɗina yaba kuma banida tambas dan zai iya haɗa kai dashi ya cutar dani”
Siraj yace “ka chanja PA kawai”
“haba Siraj how many PA I have to change just because of him? PA 4 na chanja akanshi bazan sake chanja wani ba not anymore”
cikin faɗa yake maganar jijiyar wuyansa na tashi da sauri Usman da Nura suka juyo suna kallon su, Mairo kara sakin baki tayi tana kallonsu daman hankalinta yana gurin,
dafashi momi tayi “ga wata shawara Qasin”
kai ya ɗaga mata ba tare daya kalletaba ‘uhmm’
“mi zai hana ka karɓi kwangilar kayi da kanka?”
murmushi yayi mai cike da jin haushi “haba momi ai zubarda kai ne daɗi zaiji na k'arɓi kwangila da hannuna masa”
“ba faɗuwa kayi ba Qasin cigabane a gareka da kuma ɗaga darajar kanfaninku”
kai ya girgiza “momi ba zaki gane ba”
“kaine baxa ka gane ba Qasin idan kayi haka mutane zasu yaɓeka suce bakada girman kai sannan kodan kwangilar tayi ya kamata kayi haka kuma idan tayi kyau zaka jawowa kanka customers ayaba maka ka kara samun ɗaukaka”
Siraj yace “gaskiya ne yaya ka ɗauki shawarar momi”
ya daɗe zaune gurin kamin ya ɗago kai ya kalleta “shi kenan momi zanyi yadda kikace”
murmushin jidaɗi Momi tayi ta shafa kansa “Allah ya maka albarka ya shige maka gaba”
shida Siraj suka amsa da ‘amin’
tashi yayi ya nufi kofa yana sauke ajiyar zuciya,
da gudu Mairo ta taso ta nufo shi tana faɗin “dan Allah ka je dani yawo inson fita”
fuska a haɗe ya shafa kanta yace “ba yanzu ba” ɓata fuska tayi idonta suka cika da hawaye shirinta na guduwa ya rushe .
juya tayi tana kallonsa har ya fice.
tashi momi tayi ta nufi up stairs tana faɗin “Maryam in kuka k'are ki haɗa kayan ki kai kicin ki wanke kuma ki share parlour nan ki goge”
kara ɓata fuska Mairo tayi abunda ta rsana kenan hawayen dake makale a idonta suka zubo.
© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*12*
bachi Mairo take saman kujera ta wani turo baki sai numfashi take da k'arfi,
Momi na saukowa ta tadata “ke ke ke Maryam”
a firgice ta farka ta kara turo baki fuskartar momi ta rik'o “kinyi wanke2?”
kai ta ɗaga tana murza ido momi tace “tashi kije kiyi wanka”
tashi tayi kamar ta fasa kuka ta nufi up stairs zuciyarta cike da tsoro,
rik'e k'arfin tayi ta rumtse ido tana tafiya a hankali har ta haye.
'''* * *'''
Momi na kicin tana girki taji uhun Mairo da sauri ta aje robar dake hannunta ta nufi up stairs.
tsakiyar ɗaki ta tararda Mairo sai juye2 take tana kuka jikinta ba kaya kikata momi tayi “ke lafiya miya faru?”
kasa magana tayi sai toilet take nunawa momi tana tuma,
da sauri momi ta nufi toilet ɗin,
kalle2 ta shiga ta rasa dalilin dayasa Mairo kuka hankalinta bai kai gurin shower da take kunne ba sai gab da zata fita sannan idonta suka kai gurin juyowa tayi ta nufi shower da niyar kashewa,
nan hannunta ya taɓo ruwan dake zuba da sauri tayi baya baya da yar k'ara saboda ta fasasshin ruwan da suka taɓa mata hannun,
ta daɗe tsaye cikin toilet ɗin tana duba hannunta,
sannan tasa hannun hagu ta kashe shower.
koda ta fito duk'e ta tararda Mairo sai faman kuka take tana kiran ta bani ta shiga uku ta data momi tayi tana faɗin “sannu Mairo ni wlh na manta da yadda shower take mantawa ma nayi na haɗa miki ruwan da kai na yi hakuri kinji”
kai ta ɗaga tana kuka tace “ni a kaini gida gurin Gwaggo”
hakuri momi tayi ta bata daker tayi hakuri momi ta haɗa mata wasu ruwan tayi mata wanka ranar har kanta saida momi ta wanke,
da suka fito momi ta rasa kayan da zata saka mata dan ita bata ga wasu kayan kwarai da zata sa mata ba haka dai momi ta ɗauko wata tsohuwar a tamfa tasa mata,
momi ta kalleta tace “hau gado ki kwanta”
da sauri ta nufi gadon ta faɗa rub da ciki,
momi na gab da wucewa Mairo ta ɗago da jajayen idanunta ta kalli momi “mumo ko zaki aikeni?”
juyowa momi tayi “aike kuma Maryam kamar ya?”
tashi tayi zaune “in siyo miki wani abu ko aike”
murmushi momi tayi tace “a a ni babu abunda za'asiyo min koma abu zan siya saidai na aiki direba ko yara su siyo”
komawa tayi ta kwanta tana zubarda hawaye.
kai kawai momi ta girgiza ta fice.
Mairo tunda ta kwanta take wahalallen bachi sai uku da rabi ta farka koshi dan momi ta tadata ne.
hannunta Momi ta riko ta suka nufi bathroom kin shiga tayi ta lak'e kafaɗa “ni bazan shiga ba”
“yi hakuri ni zan haɗa miki ruwan ba zakiji zafi ba”
daker momi ta lallaɓata ta yarda suka shiga,
brush momi tasa tayi tare da alwala sannan suka fito,
tsareta momi tayi saida tayi sallah sannan ta riko hannunta suka nufo downstairs.
zaune suka tararda Qasin yana cin abinci laptop na gefensa yana aikin danne2.
tsaki momi taja bayan ya jama Mairo kujera ta zauna,
ɗagowa yayi yana kallon Momi “lafiya dai momi?”
saida ta zauna sannan tace “hala baka ci abincin ba?”
sosa kai ya ɗanyi yayi murmushi “indomi ce ta ɗafa”
taɓe baki momi tayi “to Allah ya kyauta ya sawwake”
kasa amsawa yayi saima kallon Mairo da yayi yace “bakida lafiya ne hala?”
kin masa magana tayi saima faman cin abincinta da take tana sauke ajiyar zuciya,
momi ce ta kalleshi tace “k'onewa tayi da ruwan zafi shine take fushi”
“ayyah sorry kijin injin bata jimu ba?”
“bata jimuba zafin daine ya raɓeta”
kanta ya shafa “sannu kinji?”
kai ta ɗaga masa tana aika lomomi,
suna haka Usman ya fito ɗakinsa ya nufi kofa.
kiransa momi tayi “Usman”
“na'am Momi”
“dan Allah jeka ɗaki ka ɗauki ATM ɗina kaje nan Damary plaza ka siyo ma Maryam kayan sawa”
“owk momi”
da sauri ya nufi upstairs.
tashi Mairo