Showing 72001 words to 75000 words out of 85263 words
Chapter 25 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt
tana haɗiyar yawu.
Wani daddaɗan K'anshi ne ya daki hancinta hakan yasa ta buɗe idon a hankali.
Arba tayi da wata kyakkyawar sark'ar gold “Yaya kamar zinari na wanene?"
Ta tambaya idonta a zare zuciyar na bugawa da sauri.
“Gold ne ba kama bace kuma ke na siya ma ko baki so"
Da sauri tasa hannu biu ta karɓa ta kuma durkusa k'asa “Inaso yaya na gode sosai Allah ya bika Jazakallahu khar"
Murmushi yayi ya ɗan tsosa bakinshi “Ur welcome dear" Ya tado da ita yasa bakinshi cikin nata.
Batayi k'ok'arin hana shiba har saida ya gaji dan kanshi ya zare bakin daga nata.
Tashi tayi da sauri “Bari naje na nuna ma Momi"
Kunkurumta ya rik'e “A'a Momi yanzu ai tayi bachi kuma kinsan bata son a tashe ta"
Kai ta ɗaga mishi tana murmushi mai fitar da sauti har cikin zuciyar ta take jindaɗin.
Laptop ɗin shi ya janyo “Zauna na nuna miki wani abu" kusa dashi ta zauna tana ciki da jindaɗi.
Kunna laptop ɗin yayi ya shiga nuna mata wasu pictures ɗin da bata san lokacin ya ɗauke suba.
Dariya ta dingayi ganin wasu bachi ma take “Lahhh Yaya yaushe ka ɗauka?”
“Kina bachi na ɗauka ba kece kike tsayawa kallo a parlor ba"
Murmushi tayi ta k'asa da kanta kamar wace taji kunya.
Nan ya shiga nuna mata nashi hotunan da yayi a k'asashe waje. Ganin ta fara jin bachi yasa ya janyota ya kwantar da ita saman jikinshi.
Aiko nan da nan bachi ya buget. Qasin kamar mai jira ya rufe laptop ɗin, bai ko bari bachi nata ya nina sosai ba, ya kwantar da ita kan gadon ya rabata da rigar jikinta ya shiga shafa ta yana aika mata kiss ta ko'ina.
Wasa yayi da ita sosai sai da yaji ya gamsu sannan ya tashi a wahale ya shiga bathroom. Wanka yayi ya fito ya saka kayan bachi sannan ya nufo ta ya mayar mata da rigar,
Itakan sai bachi take abinda bata masan yayi ba. ɗaukar ta yayi kamar baby tare da sark'ar ya kawota part ɗin Momi ya kwantar saman doguwar kujera ya aje mata sak'ar aje.
Ya daɗe tsaye yana kallonta sannan manna mata kiss a goshi, ya kashe wutar parlor tare da Tv yaja mata k'ofa.
***
Asubar farin Momi ta tashi ta daman haka take mata kullum saboda zuwa makaranta tunda har Asabar da Lahadi zuwa suke basu da ranar hutu.
Cikin magagin bachi ta motsa tana faɗin “Yaya duk sunyi kyau"
Momi ta jijjigata da k'arfi “Ke tashi kiyi wanka kiyi sallah wane yaya kuma?"
Muk'a ta shiga k'ok'arin yi sannan ta tashi, sark'ar dake gefenta ta faɗo. Bata kula ba ta wuce ɗaki tana murza ido da mamakin ganinta parlor Momi ita da bachi ya ɗauke a part ɗin Qasin.
D'aukar sak'ar Momi tayi ta rufa mata baya bayan ta k'are mata kallo, Sai da tayi sallah ta shirya sannan Momi ta tambayeta ina ta samo sark'a.
Dariya tayi “Ashe da gaske ne ni na ɗauka duk mafarki nake Yaya ya bani jiya da dare"
Momi tayi murmushi “Aiko ya kyauta tunda daman bakida sak'ar zinari kuma ya siya miki mai tsada ina fatar dai kin mashi godiya dan godiya tana ɗaya daga cikin abin da take saka Namiji jindaɗi idan yayi miki kyauta koda kusa kyautar bata kai ta kawo ba"
Kular abincinta ta ɗauka tana faɗin “Nayi mishi Momi bari naje ga motar makarantar mu can ta iso"
“Toh Allah ya tsare ya kiyaye"
“Amin Momi sai na dawo"
Kai Momi ta daga mata tana murmushi, iya natsuwa yanzu kan tasan Mairo ta samu saidai wayou ne ba tada tabbaci ko tayi amman da tasan ko minene dai sannu-sannu bata hana zuwa sai dai a daɗe ba'aje ba.
'''**'''
Bayan Sallar Azahar Qasin ya shigo part ɗin Momi, sun ɗan daɗe suna fira anan ne take mashi zance sark'ar daya ba Maryam tana godiya.
Dariya yayi “Haba Momi dan naba Maryam sark'a sai kuma kimin godiya?"
“Eh mana ai idan kayima Maryam abu kamar ni kayima tunda Maryam yata ce"
“Amman dai Momi bata ce miki wani abuba ko?"
“Kamar na mi kasan ai yanzu ta rage yawan zubar nan wani abun kace tace ne?"
Kai ya girgiza “A'a"
“Wai Qasin ya maganar tarewarku ne?" Yana unk'urin tashi tayi mishi maganar hakan yasa ya koma ya zauna yana faɗin “Momi toh ai ke nake jira"
Momi tace “Jiya Abbah ka yayi maganar daya kirani a waya har nake ce mishi akwai kayan da ba'ahada ba yace zai turo kuɗi ayi komai,
K'auye ma ance tambaya kawai suke Gwaggo ku sai fama matsifa take"
“Nima dai Momi shi nagani yanzu dai babu wani abinda ake jira"
“Idan ya turo kuɗin zan siya mata duk abunda ake bukata sai asa ranar tarewar taku"
Murmushi yayi “Hakan yayi Momi Allah ya taimaka"
“Amin amman dai kasan dole ne kaje bikon Mansura ko da baka tare daga kai sai ita ba ka kyale ta can"
“Momi ai Mansura bata gari"
“Bata gari kuma?" Momi ta tambaya.
“Eh wai taje raka yayarta a indiya duba lafiya"
“Da gaske?"
“Allah kuwa nima a bakin Sadiq naji kinsan yana Auren k'anwarta kuma dana kira wayar yak'i shiga"
“Amman da izinin waye taje kai kasan da tafiyar ne?"
“A'a sai bayan ma taje ne nake ji"
Momi ta rik'e baki “Amman dai gaskiya daga ita har iyayenta basa da tunani Allah ya kyauta"
“Amin ai sai ta gane kuskurenta bari naje nayi sallah naji kiran La'asar"
Maganar yake yana kallon agogon hannun shi, Momi tace “Nima ai bari na tashi naje nayi sallar"
Tashi yayi ya fice, ya bar Momi tana mamakin hali irin na Mansura.
'''** ** ** **'''
Da murmushi Momi ta sauko downstairs tana kallon kujerar da Yarima yake zaune,
“Masha Allah Yarima har an iso?"
Ba tare daya kalleta yace “Eh miyasa kike nema na?"
Ruwa Momi ta ɗauko mishi da cup ta dire mishi sannan ta zauna a ɗayan kujerar tana faɗin “Ya gida ya kowa da kowa"
Ya daɗe yana kallon zoben hannun shi sannan ya amsa mata “Lafiya kalau"
Momi tayi gyaran murya cikin fuskar manya ta soma magana “Wata alfarma nake nema a gurinka Yarima"
Sai a lokacin ya kalleta “Allah yasa zan iya"
“Zaka iya dan bata gagareka ba kuma kana da ikon aiwatarda ita"
Shiru yayi yana murza yatsunshi, yasan Momi da wayo kuma gashi she's look so serious akan ko minene.
Sai da ya busar da iskar bakinshi ya ɗora k'afarshi ɗaya saman ɗaya sannan ya kalleta kamar mai karantar abu a fukarta.
*© KHADEEJA CANDY*
[11/9, 7:00 AM] Khadeeja Candy: *♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com
*Vote me on Wattpad* @khadeeja_Candy
*61*
Ya daɗe yana kallonta sannan ya ɗauke kanshi “Ina jinki"
Momi saida ta sauke ajiyar zuciya sannan tace “Aure nake son kayi Yarima"
Nan ya sake kallonta yana ɗan murmurewa.
“Yes dole kice nayi Aure tunda kinga burin ɗanki ya cika ko banyi tunani zaki iya sakani a gaba ba kiyi min irin wannan maganar"
“Yarima shekaranjiya Hajiya ta kirani ta faɗamin kace kai ba zakiyi Aure toh akan wane dalili? Kaine kaɗai ɗan data haifa kaine farin cikin ta miyasa baka tunanin kyautata mata kayi mata abinda zai sata farin ciki"
Taɓe baki yayi “Inayi abinda nasan zan iyane kawai dan kinsan ko Allah baya kallafawa rayuwa har sai abinda rayuwar take iyawa da kanta so idan kina da wata maganar kiyi"
“Bani da wata maganar wannan ce kawai kuma a tunani na isa nace kayi kayi shiyasa na rik'e ka dan wannan matsalar ce kawai take damun mahaifiyarka da kuma duk wani masoyinka"
Tashi yayi tsaye yasa hannayenshi aljihu.
“Ko zanyi Aure ba yanzu ba so maganar Aure ta daina damunku have a wonderful day"
Yana kaiwa nan bai tsaya jiran abinda zata ce ba yasa kai ya fice.
Ko kaɗan Momi bata jindaɗi yadda yayi mata ba duk da yake tasan kaɗan ne daga halinshi babu wadda ya isa ya sashi abinda bai tashi ba.
As usually biyar dai-dai motar makarantar *KOYI DA KANKI* (gidan sisto😉) ta sauketa k'ofar gida.
Tana shigowa kayanta karatunta kawai ta aje ta nufi bathroom, wanka tayi ta shirya cikin wani farin material sannan ta nufo dining room,
Saida ta cika cikinta sannan ta tashi tana hamdala, ta dawo saman kujeara ta zauna tana shafar ciki.
Sallamar Momi ce tasa ta ɗago kai ta kalli k'ofa “Wa'alaikissalam Momi sannu da zuwa"
“Yauwa sannu kin dawo?"
“Eh tin ɗazu har naci abinci nayi wanka Momi ina kikaje?"
Upstairs Momi ta nufa tana faɗin “Gidanki wasu kaya na kai"
'Dauke kai tayi ta cigaba da kallon tana cikama bakinta iska.
Daga can cikin ɗakin Momi ta kwalama Mairo kira,
Tashi tayi tare da amsawa “Na'am Momi"
Shiga tayi cikin ɗakin tana faɗin “Momi gani"
“Zo ga kaya nan ki buɗe"
Duk'awa tayi gaban sait ɗin akwatunan ta shiga buɗewa “Momi na waye ne tun ɗazun na gansu?"
“Naki ne shine lefen da mijinki yayi miki"
'Dauke hannayenta tayi tayi k'asa da kanta.
Murmushi Momi tayi tace “Ranar Asabar mai zuwa za ayi walima In'sha Allah kuma za' kaiki ɗakin mijinki kuma ki shirya gobe mai dilka zata zo ta fara gyaraki"
B'ata rai ta ɗanyi kamar bata jindaɗi ba. Ta tashi jiki a kasale ta bar ɗakin,
Shiru Momi tayi kamar mai tunani can kuma ta shiga duba kayan da kanta.
Tun daga lokacin Mairo bata sake walwalah ba, Momi kuma bata bi ta kanta ba ta cigaba da shirye-shiryenta da take mata hankalin Momi bai kwanta ba sai taga komai na gidan ya kammala.
Kullum mai dilka sai tazo tayi mata Momi ta ɗaukar mata hutu a makaranta cikim yan kwamakin Mairo ta zama wata irin mace abar sha'awa, jikinta yayi kutil-kutil sai sheki take tayi wani assirtattaccen fari,
Ranar da akayi mata dilkar k'arshe ne take tambayar Momi ko su Gwaggo zasu zo,
Momi tace “Bana tunani zasu zo dan bn fada musu ba kinga ai ko mun nan mun isa tunda akwai yan'uwan nan ko a nan bayan kin tare zan faɗa musu sai suzo so ganki kinji?"
Kai kawai ta ɗaga mata ta tashi idonta cike da hawaye ta fice.
Washe gari Jumma'a tunda safe mai kitso da lalle tazo aka hau aikin gyara ta, wunin ranar komai bata sa abakinta ba har akayi aka k'are,
Kallon ɗaya Momi tayi mata ta fahimci tana cikin wani yanayi mai wuyar fassara.
Bayan Sallar Isha'i Momi tasa Mairo gaba tana faɗa mata wasu abubuwan da ya kamata ace ta sani da kuma jan kunneta akan abubuwan da tasan tana yi masara kyau.
Kamar yadda Momi tace washe garin Jumma'a wato Assabar akayi Walima. Ba laifi anyi taro dik da ba wasu mutane sosai Momi ta gayyato ba yan'uwan da suke garine kawai sai abokaninta da kuma wasu daga cikin abokanin Mairo yan makarantar su,
K'arfe 9 motocin ɗaukar amarya suka zo, huɗuba sosai Momi tayi mata itako tana ta aikin kuka.
Daker aka fitar da ita daga gidan aka sata mota. Har aka zaunar da ita saman gadonta kuka take kamar ranta zai fita.
Mutane da suka kaita suka rik'a bata hak'uri har suka gaji suka kyaleta, basu fi awa ɗaya da zama ba ango ya shigo shida abokaninshi nan sukayi musu tasu huɗubar suka sannan sukayi musu sallama.
Har bakin k'ofa Qasin ya raka abokaninshi sai zolayarshi suke shi dai in banda murmushi babu abinda yake,
Yadda ya barta haka ya dawo ya sameta tana aikin kuka.
Kusa da ita ya zauna ya kai hannu a hankali ya yaye mahafin data rufa da shi. Nan ta ɗago kai ta kalleshi da jajayen idanunta dake cike da kwallah.
Hannu yakai ya taɓa gefen fuskarta “Mi kike yima kuka haka Maryam?"
Daker ta iya tsayarda kuka tayi mishi magana “Yaya wani yanayi nake jin kai wadda ban taɓa jin kaina a ciki ba"
'Daya hannun shi yasa ya shafe mata hawaye ya kwantar da ita saman jikinshi yana buga bayanta alamar rarrashi.
Sai da ya tabbatar da kuka ta ɗan tsaya mata sannan ya ɗago kanta yace “Tashi muje muyi Sallah kinji?"
Kai ta ɗaga mishi ya rik'o hannunta bayan ya cire babbar rigarshi suka nufi bathroom.
Tare sukayi alwalar ya sake rik'o hannunta suka fito. Da kanshi ya shinfiɗa musu carpet ya buɗe akwatinti ya ɗauko mata hijab tasa sannan ya kabbarta sallar.
Raka'ah biu sukayi suka sallame saida suka yima Allah godiya sannan sukayi ma Annabi sallati bayan sun k'are ya juyo ya rik'a kanta ya karanta Addu'ar da Annabi Rahama (S. A. W) ya koyar da mu, har lokacin hawaye take.
Tashi yayi ya ɗauko Plate da cups. Ya dawo kusa da ita ya zauna ya buɗe ledar kazar dake saman drawer ya zuba a plate kofunan kuma ya cikasu da juice.
Daker ya lallaɓata taci koshi kaɗan ta hau saman gadon ta kwanta,
Bayan ya k'are ya ɗauke plate ɗin ya chanja kayan jikinshi zuwa na bachi sannan ya hau shima ya kwanta bayanta.
_Washe gari_
Tara da rabi Momi ta aiko musu da breakfast saida ya ɗora kulolin dining sannan ya shiga ya tashe ta tayi brush sannan suka nufo dining tare.
Shida kanshi ya zuba mata abinci sannan ya zuba kanshi yaja kujera ya zauna,
Suka soma kalace.
Daf da zasu gama cin abincin wayar shi tayi ringing. Hakan yasa shi tashi tsaye ya ciro wayar a aljihu yana duba mai kiran.
Ya daɗe yana kallon wayar sannan ya ɗora ta saman dining ya cigaba da cin abincin ba tare da yayi picking ba,
Mairo kamar ta mishi maganar sai kuma wata zuciyar ta hana ta tashi tayi tana goge baki.
“Har kin k'oshi?"
Kai ta ɗaga mishi tana ɗan murmushi. Ta nufi ɗaki,
Da rana Momi ta aiko wata daga cikin 'ya' yan k'awayinta suka kawo masu abincin rana ita kadai suka tararda sai mak'otanta dn Qasin ya fita lokacin,
Sun daɗe suna taya ta fira. Nan duk ta sake dasu ta jindaɗi.
Saida sukayi mata kwaliya suna gyara mata gidan sannan suka fice.
Da dare direba Momi ta aiko ya kawo musu tuwo da drinks haɗin gida.
Haka Momi tayi ta musu kuma kullum sai ta kirata a waya ta tambaya ko da wani abun tace mata babu,
Ranar da tacika sati ɗaya da dare Qasin ya shigo musu da kuloli. Tashi tayi ta tarbo shi ta karɓi kulolin takai dining ta aje tana faɗin “Yau kai aka aiko"
“Naje can ne shine tace na wuto dasu kuma ta bani sak'o na faɗa miki"
Nufi shi tayi tana faɗin “Minene mi tace?"
Kumatunta ya rik'a ya manna mata kiss “Bazan faɗa ba sai nayi waka munci abinci tukuna"
Dariya tayi “Toh je kayi ina jira"
Matsowa yayi kus da ita ta yadda zasu iya shak'ar numfashin junansu ciki kashe murya yace “Ni kaɗai zanyi?"
Matsawa tayi baya ta ɗan mashi fuskar shanu “Toh kai da wa zakayi?"
Kafaɗunsa ya ɗaga “Nidai baki ji nace kizo muyi ba ai ko?"
Gira ta ɗaga mishi “Good boy je kayi wankan ka"
Kanta ya shafa yana dariya “Oh i like you baby"
Dariya itama tayi ta cigaba da kallonshi har ya shige ɗaki.
***
Bayan sun gama cin abincin ya rik'o hannunta suka dawo saman kujeara suka zauna.
“Yaya dan Allah fada min minene Momi tace tun ɗazu sai jamin rai kake"
Janyota yayi ta kwanta saman kirjinshi “Kamin na faɗa miki abinda Momi tace ina son fada miki wani abun"
“Toh ina jinka"
Shiru ya ɗanyi sannan ya shiga shafata “Ban da gobe idan Allah ya kaimu Mansura zata zo ta gyara ɗakinta so bana son ki kula ta koda ta tsokaneki kinji?"
Faɗuwa gabanta yayi ta dan daɗe kamin tayi magana “Ba Momi tace min taje k'asar waje ba kota dawo ne?"
“Ta dawo ita ta aiko gurin Momi tace zata zo ta gyara ɗakinta dan ni na faɗa mata ba zan je bikonta ba tunda bani ne nace taje gida ba"
Taɓe baki tayi “Yau ni ina ruwana da ita tazo tayi duk abinda zatayi nidai faɗa min abinda Momi tace"
Sai da ya shafa kanta sannan yaja hannunta yasa a bakinshi ya ɗan cijeta,
“Cewa tayi na cije miki ɗan yatsa"
Kukan shagwaɓa tayi mishi “Allah sai na rama Momi ba zata ce ka cijeni ba"
Dariya yayi yaja mata kunne “Ke cewa tayi na faɗa miki daga gobe ki fara girki da kanki"
Kallonshi tayi “Wasa dai kake?"
“Allah ba wasa nake ba haka tace in kuma baki yarda ba na kira miki ita a waya yanzu kiji"
“Ai Momi ba zata ce haka ba gaskiya dani ruwan tea kawai na iya dafawa"
“Tace komai kika iya kiyi babu ruwana nidai na faɗa miki sak'onta"
“Toh naji Yaya dan Allah zaka kaini gurin Momi gobe?"
“Yaushe kika zo gidan da har zaki fara fita?"
“Itace tace a kawo ni ɗazun a waya baka jiba?"
“A'a k'arya kike batace koma tace bazan kaiki ba"
“Toh kai da kake fita fa?"
“Namiji ai bai gaji zama ba"
“Nidai gaskiya ka kaini ko na maka kuka"
“Tashi ki shirya na kaiki gurin Gwaggo"
Dariya tasa mishi “Wasa kake min nasa ni ai"
Hancinta yaja “Au ashe kina da wayo"
Ita kuma tayi dariya ta kwantar da kanta.
Da safe shi y haɗa musu breakfast sai da ya kammala komai sannan ya yaje ya tashe ta,
Tare suka wanke baki sannan ya tallabota kamar yar baby suka nufo dining. Sai da ya k'osar da ita sannan shima yaci.