Showing 1 words to 3000 words out of 85263 words

Chapter 1 - MAIRO Complete Hausa Novels by Khadeeja Candy.txt

04 Apr 2026

883

[11/9, 6:52 AM] Khadeeja Candy: *♡...  MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*1*

"Na rantse da Allah yau sai an biyani ni babu ruwana"
rik'e take da kunkuru tana marmaɗen ido da murguɗa baki jikinta sai rawa yake wai ita ga matsifaffeya.
yaron dake gabanta ya risina har k'asa yana bata hak'uri
"dan Allah Mairo ki yafe min wlh ba zan kara ba ni naga kinje wani gurin ne shiyasa na cika miki ban san ba kyaso ba"
sai a lokacin ta kalleshi cikin matsifa tace "saka nayi cewa nayi na cika min kai mai hegen salo yau ko saika busar dashi ko na maka hegen duka"

wata dattijuwa take wanki gefen kogin ta kalleta tace "ke Mairo wai miyasa baki jin magana ne yanzu miye laifin yaron nan dan ya cika miki tulu?"
harara ta watsa mata ta murguda mata baki "ke kuma tsohuwa ina ruwanki dake nake yi ne da zaki samun baki ko sashi nayi da zai cika min tulu wannan ai rainine"
"ke fa baki da kirki Mairo daga magan zaki wani taso min kamar wata warinki"
"mtsssss yau daman kin san ba warinki nake ba kika samin baki a magana dan neman tsokana"

daidai nan Almu ya iso da jakinsa da jalkunan ɗinba ruwa.
yana kallon Mairo yasan matsifa ce take ganin yadda take marmaɗen ido tana rawar jiki
murmushi kawai yayi ya gaida dattijuwar

"inna ina kwana?"

"lafiya kalau Almu an tashi lafiya?"

"Alhamdulillah inna"

kallon mairo yayi "ke lafiyarki kike wannan harare2?"

banza ta masa ta cigaba da karkada jiki.
inna ta taɓe baki

"ai haka take indai rashin kunya ne ta iya ga yar banzar matsifa"

juyowa mairo tayi kanta "wai ke ina ruwanki dani kinga ban hega saggarki ba ki fita tawa bana son shinshigi"

da marmaɗe2 ta ksrasa maganar tana murguda mata baki.
      mari Almu ya kai mata ya fizgota ya jefar
"ke wai miyasa rashin kunya yayi miki yawa kamar inna zaki tsaya kina faɗawa irin wannan maganar sa'arki ce?"
wani ihu mairo ta saki ta shiga murk'ususu cikin kasa tana jan gashin kanta
"wayyo na shiga uku ya kashe ni wayyo Allah ya kare ni wayyo gwaggo"

tsoro Almu yaji ganin yadda take ihu duk'awa yayi ya rikota "tashi mu gani?"
wani mugun cizo ta kai masa a hannu saida ya saki kara ya saketa da sauri.
inna ta rike baki "oh ni hajjo wannan wace irin masifaffiyar yarinya ce haka?"
Almu dai shiru yayi yana murzar hannun dan ba karamin cizo tayi masa ba,
ya dade a haka kamin ya nufi kogin ya shiga cika jalkunansa.
       ihunta ta cigaba dayi tana murje2 daga Almu har inna babu wadda ya sake bi ta kanta.
Almu na daf da cika kayansa halilu ya iso gurin yana ganin mairo yayi saurin ta data "ke lafiya miya faru?"
langaɓe masa tayi ta cigaba da kukan
nan ya kalli inna da Almu ya shiga tambayar su ba'asi "wai miya sameta ne haka?"
inna tace "babu kawai rashin kunya tayi min Almu ya ɗan zungureta shikenan fa ta faɗi ta shiga koke2"
cikin kuka Mairo ta ɗago "wlh karya suke itace ta fasa kuka tace masa na zageta shi kuma ya ɗaga ni sama ya jefar na kare"
tana kaiwa nan ta saki wata kara kamar wadda aka sokawa wuka.
rik'e baki inna tayi jin irin karyar da Mairo ta zagga
Halilu ya kalli Almu "haba Almu ya zaka mata haka kamar wata warinka ko namiji"
Almu yayi murmushi "haba dai Halilu sai kace bakasan halin Mairo ba wlh karya take"
Halilu yace  "wai minene mafarin wannan masifa?"
inna tace "ɗiban ruwa tazo fa saita eje tulun ta tafi yawonta shine haruna ya dauka ya cika mata shine data dawo tace sai ya biyata shine ya zubar da ruwan daya zuba kuma duk da haka tace wai saiya busar tulun yadda yake shine ya shiga bata hak'uri taki hak'ura wai ita saita dake sai natibmata magana shine fa ta shiga fada min magagganu har Almu saida tayi masa rashin kunyar"
Halilu yace "daman shine kawai take yiwa wannan kuka?"
"shine kawai babu wani abun da akayi mata"
cewar inna.
kai halilu ya kaɗa ya Nufi ecen dogon yaro ya k'allo ya juyo gurin mairo cikin zafin nama ya watsa mata ita,
mairo najin saukar bulala ta tashi da gudu ta nufi gida tana uhu.

***   ***   ***

da ihu ta isa gida tana murxa gurin da Halilu ya buga mata bulalar.
da sauri gwaggo ta tare ta "lafiya Mairo miya sameki?"
rumgumeta tayi "wayyo gwaggo zasu kasheni gwaggo basa sona sun min taro suna ta duka na"
gwaggo ta dagota "su waye Mairo faɗa min uban wa ya taba ki cikin garin nan?"
cikin kuka ta shiga yima gwaggo k'arya data saba "tsohuwar gidansu hajara ce tace wa Almu wai na zageta shine shi kuma ya daga ni sama ya jefar gwaggo ya k'arya ni na bani mutuwa zanyi"
da sauri gwaggo ta zaunar da ita ta shiga duba ta tana matsifa "wannan wace irin k 'etace haka wlh duk suka karyaki sai munyi shari'ah dasu mugayen mutane azzalumai"
gwaggo na taɓa mata k'afa ta saki wani mahaukacin ihu "wayyo na shiga uku gwaggo nan gurin Halilu ya buga min ecce"
gwaggo tayo waje da ido "ecce kuma yaushe mi kika masa?"
"ban masa komai ba daga zuwansa suka fada masa k'arya shine ya dauko k'aton ecce ya buga min gwaggo basu sona na shiga uku"
tashi gwaggo tayi ta shiga ɗaki ta ɗauko mayafinta ta nufi kofa.

  
        '''
NOTE'''
*_Assalamu Alaikum ina bawa fans ɗina hak'uri bisa ga rashin ganin cigaban novel ɗina mai suna LAMARIN DUNIYA na k'are novel ɗin gaba ɗaya kamin na fara posting sai phone ɗina ya samu matsala kuma wadda nayi publishing a blog ɗina blog ɗin ya samu matsa. ta dalilin matsalar da phone ɗina ya samu amman ana kan gyara blog ɗin da zarar an kare zanyi muku C & P Insha Allah ko kuma na baku blog address ku karanta bayan haka dan Allah ina rokon duk mai novels ɗina ko wane iri ya turo min ta wannan number_*
+2348036126660
*_taku har kullum Khadeeja Candy_*

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:37 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*2*

gwaggo na k'ok'arin fita halilu na k'ok'arin  shigowa sukaci karo nan taci kwalarsa ta k'asara shigowa dashi tana masifa "ashe baka da hankali halilu dan kana magu zaka sa ecce ka bugawa Mairo bancin bugun da Almu yayi mata wai mi ta tare maka ne?"
kai ya girgiza "haba gwaggo wai miyasa duk tazo tayi miki k'arya saiki yarda ya za'aiyi na buga mata ecce fisabilillahi?"
"ai halinka na sani ba sonta kake ba zaka iya mata komai"
kallon mairo yayi da tayi shiru tana kallonsu kamar wata munafuka yace "ke dukanki nayi?"
kai ta daga ta turo baki tana matsar kwallah.
"eh gurin da Almu ya karyani ka buga min ecce"
gwaggo ta kara ciyo kwalarsa "mugu yanzu abunda kake ya kamata kenan a gaban idonka ka bari Almu yayi mata wannan illar wai miyasa baka son yarinyar nan ne halilu?"
"ohhh gwaggo haba haba wane irin illa Almu zaiyi mata rashin kunya fa tayiwa tsohuwar mutane shine ya dan zingureta fa"
gwaggo tace "tho ina ruwansa ya zingureta haihuwarta yayi kuma karya kake karyata yayi"
"haba gwaggo yarinyar da aka karya zata iya kawo kanta gida har ta iya faɗa miki an karya ta ai saidai a kawo miki ita"
saki kwalarsa gwaggo tayi ta nufi Mairo ta shiga duba k'afar.
aiko nan mairo ta k'ara marairaicewa tana "wayyoh k'afata" gwaggo ta duba bata ga alamun kariya a k'afarta ba ko alamun jimuwa babu barre karaya ta data gwaggo tayi tsaye "tashi kiyi tafiya na gani"
nan ta lak'e kafar "wayyo bazan iya takata ba gwaggo ta riga ta karye"
cikin dabara halilu ya cire takalminsa ya jefa mata iya karfinsa aiko da gudu ta faɗa ɗaki tana ihu.
matsowa yayi kusa da gwaggo ya ɗauki takamin yana faɗin "yanzu wadda aka karya zata iya wannan gudun?"

shiru gwaggo tayi halilu yace "gwaggo wata rana saita saki kunya matukar duk abunda tazo ta faɗa miki kina yarda dashi tho ko zaki ɓata da kowa"
tsaki gwaggo taja "mtsss tho sai mi dan na ɓata da kowa akanta so kake na zuba ido ina kallon ana cin amanarta? ko kai ka taɓa ta saina taɓa ka bare wani can"
halilu bai kara cewa komai ba banda kan da ya girgiza ya fice ya barta tana masifarta.
saida Mairo taji fitarsa sannan ta fito tana kukan munafurci.
nan gwaggo tayi cikinta ta masifa "Allah mairo in kina zuwa kina min karya saina ɓata miki rai kuma na ɓata dake na fita harkarki"
    kwantowa tayi jikinta tana kukan shgwaɓa "tho ai ba karya nake ba Almu ya dakeni kuma Halilu ya zaggamin bulala"
tureta gwaggo tayi "amman ai cemin kikayi shiya buga miki ecce Almu kuma ya karyaki"
turo baki tayi
"eh karya nake amman dai sun dakeni dukansu"
"tho miyasa kika min karya kuma halilu yace ai tsohuwa kikayiwa rashin kunya"
"tho gwaggo ai itace ta samin baki a magana kuma tace min masifaffiya"
"amman ai kinsan na hanaki rashin kunya da karya ko ni daga yau babu ruwana dake"
kuka ta shiga rerawa "na daina gwaggo dan Allah kar kiyi fushi dani ba zan kara ba"
gwaggo bata so kuka mairo ko kaɗan janyota tayi jikinta "shi kenan bazanyi fushi dake ba amman ki daina kinji ba kyau kuma bana so"
"na daina daga yau ni ko kallon mutane bazan sakeyi ba"
gwaggo tayi dariya tace "rufe da ido zaki rika yawo kenan?"
"eh bazan sake kallon mutane ba bare suce nayi musu rashin kunya"
gwaggo ta shafa kanta "a'a kawai ki rika jin magana kibar rashin kunya yayi basai kim rufe idoba"
dariya mairo tayi "ai wasa nake miki gwaggo ya za'ayi na rufe ido kina son na fada rijiyane ko rame?"
dundu gwaggo ta kaimata a baya tana dariya "oh baki daina karyar ba kenan ko?"
"na daina Allah yanzu ko zanyi kaɗan zanyi"
gwaggo ta girgiza kai "a,a ki daina gaba ɗaya dai wai ina kika baro min tulu?"
"yana can kogi ni gaskiya gwaggo daga yau bazan kara zuwa ɗiban ruwa ba kullum ni nake zuwa kuma yar k'ank'anuwa dani shi halilu da yake k'ato bazai jeba sai ni shiyasa suke dukana sunga ni banida girma"
cike da shagwaɓa take maganar tana son yin kuka.
gwaggo ta shafa bayanta "shikenan bazaki sake zuwa ba halilu ne zai rik'a ɗebowa"
rumgumeta mairo tayi tana murna.

'''        * * *'''

_2:13pm..._
gwaggo ta kare dahuwar giɗar ta ta zuba a gwango.
ta kwalawa Mairo kira da sauri ta fito tana ɗaurin ɗankwali rabin fuskarta duk fodace da bata shafu ba.
"na'am gwaggo kin kare?"
saida ta kare lisafin sannan ta ɗago ta kalleta tace "ta ɗari biu da arba'ince"
ɓata fuska mairo tayi "gaskiya gwaggo saidai ace ta ɗari biu da talatin dai dan gaskiya zan ɗauki ɗaya"
gwaggo tace "ɗauki ko nawa kike so mairo waya isa ya hanaki?"
murmushi tayi ta duka ta ɗauki turen tana faɗin "yau duka zan siyar"
"tho Allah bada sa'ah amman dai hodarki bata shafu ba mairo"
turo baki tayi "nidai gwaggo bana son haka bani na shafa ba nidai haka zanje"
hannu gwaggo ta ɗaga mata "jeki jeki Allah bada sa'ah inda yanzu kuma ban faɗa miki ba ki hauni da masifa"
batace komai ba ta ɗora turen samsn kai ta nufi kofa.
gwaggo ido ta sakar mata a ranta tana _Allah ya shirya minke mairo ya tsare_

© *Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*3*

tafe Mairo take ɗauke da turenta na giɗa saman kai tana yan wakewakenta.
saida tayi nisa da tafiya sannan ta tuno da ɓanɓaramar da tayi jiya da sauri ta chaja hanya harda haɗawa da ɗan gudu tana waigen bayanta.
saida taga ta shanye kwana sannan hankalinta ya kwanta tafiya ta rik'ayi a hankali tana kwanɗalar giɗar tana ci.

kashe kunne tayi tayi gefen dashi tana son ta tabbatarda abunda kunnuwanta suke jiyo mata.
wak'ar india ce _ghajiniguzarish_ ke tashi cikin wani kiɗan taushi mai daɗi
taɓe baki tayi "tho wai wayasa wannan kiɗan mai ɗaɗi cikin ɗaji kodai buki ake?" magana take tana kallon giɗar dake hannunta kamar wata taɓaɓɓiya.
kara kasa kunne tayi har ta gano gefen da sautin ke tashi dariya tayi "Allah buki ne ake bari na leka na gani amman ba zan daɗe ba sai na dawo"
haka ta kunna kai daga wani ɓangare na hanyar ta rika tafiya tana bin inda taji sautin wakar na tashi harta iso wani guri mai kamada lambu.
tsayawa tayi tana kallon etacen dake gurin "lahhh ashe ma haka gurin yake ni kan ban taba zuwa ba sai yau"
rabon ido ta shigayi saida ta kare kallon gurin sannan ta cigaba da tafiya.
a hankali ta fara hango wasu mutane sanye da wani yadi kala ɗaya.
da sauri ta laɓe gefen ecce tana lekensu ,

duk kansu sanye suke da yadi kala ɗaya mai ja da kore (red and green) kana gani kasan fadawa ne in banda mutun biu dake zaune saman wani k'aton carpet na alfarma ɗayan sanye yake da riga da waddo na turawa ɗayan kuma sanye yake da riga doguwa mai kamada jalabiyar fakistan _golden color_ Mai kyau sai kyali take.
ya dora wani ɗan kyale saman wuyansa daya sauko har saman rigarsa.
gashin kansa ya kwanta lum kamar balarabe ya lankwashe kafafunsa wata rekoda na gefensa tana bada sauti shi kuma yana fuskarta ɗayan suna karta ko wannensu kuɗi yake azawa in aka cinye ya kara wasu.

        sosai abunda suke ya burge Mairo aje turen giɗar tayi tayi zaune tana kallonsu tana dariya amman baki rufe dan kar suji
ta daɗe a haka can dai taji bazata iya jurewa ba ta ɗauki turenta ta nufosu tana Murmushi.
"Assalamu alaikum"
sallama tayi musu tana k'ok'arin k'arisawa kusa dasu
   da sauri suka tare wadda ke zaune saman carpet ɗin wasu kuma suka nufota rik'e da takobi.
tsaye tayi tana kallonsu kamar hoto har suka karaso kusa da ita,
wani zarare cikinsu ya ɗaga takobi zai sara mata ɗayan yayi saurin  rikewa yana faɗin "Yarima yace a dakata"
da sauri ya janye takobin yayi baya.
ɗaya daga cikin fadawan ya fisgota da karfi har giɗar dake saman kanta ta watse ya nufi gurin yarima da ita.
yana tsaye yana kallonsu har suka iso da ita kallo ɗaya yayi mata ya gane bata cikin hayyacinta ganin yadda idonta suka k'afe kuma bata motsi.
    ido ya ɗan tsura mata sannan ya bada umarnin a zuba mata ruwa,

da sauri bafaden ya dauki ruwan gora ya watsa mata
sai a lokacin ta matsa alamar ta dawo hayyacinta zubewa tayi zaune ta ɗaga kai tana kallonsu
suma ita suke kallo har yarima saida ta kare kallonsu ɗaya bayan ɗaya sannan ta saki wata irin kara iya karfinta mai shiga cikin kwakwalwa faɗuwa yarima yayi zaune ya dafe kunnunwansa shida wadda ke kusa dashi.
mari daya daga cikin fadawan ya watsa mata saida ta faɗi can gefe ta fashe da kuka
     ɗagowa yarima yayi ya watsa masa wata mugunyar harara da sauri bafaden ya faɗi kasa "Allah ya huci zuciyarka Yarima banyi dan ranka ya bace ba"
kawarda kai yayi yana sauraren sautin kukanta dake tashi tare da sautin waka

ya daɗe a haka sannan ya ɗago cike da isa yace "kashe sautin nan" da sauri ya tashi ya nufi rikodar sa hannu ya kashe ya dawo ya risina gaban Yarima yana faɗin "Allah karawa Yarima martaba na kashe"
ba tare daya kalleshi ba yace
"jeki ka rarrasheta"
"am gama Yarima" tashi yayi da sauri ya nufi gurin Mairo.

tirgewa Mairo ta karayi tana kuka tana kiran gwaggo tana murza hannayenta da kafafunta cikin kasa,
yayita rarrashinta har ya gaji tak'i tayi shiru sai ma karawa take.
ganin tak'iyin shiru yasa Yarima yayi mata alamar tazo da hannun tashi tayi ta share hawayenta ta nufoshi tana murmushi kamar ba ita ba.
kallonta yake harta karaso kusa dashi tun kamin yayi mata magana ta zauna saman carpet ɗin kusa dashi.
       da sauri ɗaya daga cikin bafaden ya unkuro zai mata magana Yarima ya ɗaga masa hannu nan dukansu suka ja baya kowa ya shiga harkar gabansa.
kallonta yayi a natse cikin isa yace

"ya sunanki?"
washe masa hauru tayi
"Mairo"

"Mairo?"

"eh sunana Maryam amman Mairo ake cemin kaifa ya sunaka?"

bai amsa mata ba ya jefa mata wata tambayar "an garin kike?"
"eh kai amman dai ɗan birni ne ko?"
nan ma wata tambayar ya sake jefa mata batare daya amsa mata ba
"mi kikazo yi nan?"
"talla nake zan wuce sai naji kiɗi na ɗauka bukine ake shine nace bari nazo na gani saina koma shine na ganku sai na taɓe"
shiru ya ɗanyi yaɓa kallonta sannan yace
"tho miyasa kika fito?"
abunda ke gabansa ta ɗauka ta nuna masa "wasan da kuoe da wannan abun ya burgeni shiyasa na fito"
bai sake ce mata komai ba ya janyo wayarsa ya shiga danne2

sai a lokacin Mairo ta tuno da giɗarta
hannu ta ɗora saman kai ta fasa kuka
"wayyo na shiga uku giɗata"
wani mugun tsaki wadda ke kusa da Yarinan yaja yana hararta.
a hankali Yarima ya ɗago kai ya kalleta
"ina giɗar take?"
"nima ban saniba ɗazu dai kamin nayi bachi nasan tana saman kaina"
kallon rashin fahimta yayi mata "bachi kikayi?"
"eh ɗazu da suka nufoni da takobi ba sai naji bachi dana farka sai naganni nan kuma banga giɗar ba"
murmushi yayi dan ya gane suma take nufi da bachi.
ɗaya daga cikin fadawansa ya kira da sauri yazo gabansa ya risina cikin isa Yarima yace
"ina giɗar Yarinyar nan?"
"gata can kusa da ecce ta zubar"
"jeki ka ɗauko mata"
tashi yayi da sauri ya nufi gurin yana faɗin "am gama Yarima"
kallon Yarima tayi tana dariya "na gode"
kai kawai ya ɗaga mata
ta sakar masa murmushi tace
"kai baka fada min sunanka ba?"
yi yayi kamar bai jita ba ya mai yarda idonsa wani gefen
nan mairo ta ɓata fuska ta buro baki
"ni inna tambayeka saika kyaleni nima amsar da na baka ban yafe ba lafira saika biyani"
cikiciki take maganar amman hakan bai hanashi ji ba
dariya ce tazo masa da sauri ya mayarda ita murmushi ya kara kawarda fuskarsa.

*© Khadeeja Candy*
[11/5, 9:39 AM] Khadeeja Candy 🍧: *♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*4*

suna haka nafaden ya kawo mata turen giɗarta ya aje yana faɗin "gashi Yarima Allah ya kara maka daraja"
hannu ya ɗaga masa bafaɗen ya tashi.
kallonsa Mairo tayi "na gode"
banza yayi mata kamar bai jita ba sun daɗe a haka sannan ya juya ya kalleta yace "amsar da kika bani zan biyaki lahira?"
shru tayi tana kallonshi dan batayi zaton yaji ba can tace "eh mana tunda kai baka banu amsar tambaya ta ba"
shiru ya ɗanyi sannan yace "mi kike tambayeni?"
"ba nace ka faɗa min sunanka ba"
ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login