Showing 21001 words to 24000 words out of 146738 words

Chapter 8 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt

23 Nov 2025

5770

din ku bazan taba yarda na barmai gaba daya ba dan kina kallan idanunsa da yanda yake aiki zakisan akwai tsantsar greediness."
Mumy ta mike tace "  Zan sauka."

  Inna ta kalleta ta girgiza kai, tace ba da dan ina nuna mai matsayinsa ba kina tunanin zai ci. A da darajaki ne?"
Mumy tai shiru, Inna tace "jeki ke kika sani."

  Mumy ta sauko ranta ba dadi.

*******

Ummy ce ta turo kofarsa dan tajita ba a kulle ba, yana zaune a kasa yayi shiru sai ma ka rasa me yakeyi shi kadai kullum a zaune, ta shiga ta ajiye tiren abincin sannan ta zauna gefensa kadan tace "tunani kake?"

  Kallanta yai bai ce komai ba, tace "Dazu Abbanka yama magana ko?"
Yanzun ma baice komai ba, tace "Hassan mu iyayenka ne wandanda duk duniya duk wani mai sanka sai dai ya biyo bayanmu, ka fi kowa sanin bazamu zabama abinda zai cutar dakai ba, bazan kuma nemi takura maka ba, sai dai abu daya zan fadama wannan auran ni na fara amincewa akai sannan shine babban burina wanda nakesan ka taimaka ka cikamin shi."

  Ta danyi shiru kafin ta mike tai waje.

  Da kallo yabi bayanta sannan ya runtse idanunsa, Ummy ya takeso yai?


#ONELUV💕
[07/10, 22:19] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

  (_D home of expert and perfect writer's_💡)

*Sisters Always Ask Questions, Borrow Clothes, Tell You When Your Hair Doesn't Look Good, Always Fight but Never Drawn Apart, Love You Always, Encorage You When You Are Dawn...*
_A Small Quote For My Sister Love You Always Ameenah😍_

*NO 13*

A rayuwar Jalila indai tana gaban Goggo jinta takeyi kamar yarinyar goye, shiyasa duk wata tabata da shirme juyema Goggo takeyi, suna kwance zasuyi bacci duk ta isheta da neman sanin asalin labarinta.
Goggo tace "to ya isheni haka nan yanzu sai ki kwanta ko kin manta gobe kunada taro a makaranta?"
Jalila ta juyo inda Goggo take tace "Goggo kinsan yanzu addu'ar da nake yi yanzu?"
Goggo tace "ya wuce shirmen soyayyarki?"
Jalila ta girgiza kai tace "A'a addu'a nake Allah ya kara miki lafiya da tsawan kwana muyi rayuwa tare, banaji zan iya kwana d'aya a duniya in bakyanan."

  Goggo ta hade rai tace "Jalila nikam sai yaushe ne zaki girma? Na dauka in mutum ya tashi cikin wahala yana hankali amma wani sa'in in kikai wani abun sai inta mamakin ki."
Jalila tai murmushi tace "Goggo a koda yaushe in ina tare dake ji na nake kamar yarinyar goye, kece kawata, mahaifiyata, mahaifina, sannan kuma yar uwata, Goggo yanda bana boye miki komai dan Allah kema kidinga sanar dani komai na rayuwarki."

  Kallan tausayawa ta mata dan tabbas tana ji a jikinta wani babban ciwo na cinta domin wasu sababbin canjin da take fuskata a jikinta tasan da matsala,, sai dai fatan Allah yasa abin ba babba bane.

  Jalila tace "Goggo!"
Goggo tace "shikenan Jalila na miki alkawari a daren gobe zan sanar dake komai na kafin a haifeki, yanzu dai ki kwanta."
Tace "yauwa Goggona, saida safe."
Goggo ta daga kai, sannan ta zuba mata ido, kankace me Jalila ta tafi bacci.

  Goggo a dade tana kallanta har batasan sanda hawaye suka gangaro mata ba, hannu tasa ta share sannan ta gyara mata bargo ta juya ta fara bacci.

   Da safe bayan ta gama gyara bangarensu ta fada wanka, an dade ana saba jiki kai kace fatar tata zata canza, ta fito ta bude drawer dinta ta saka kayan makaranta sannan ta shiga duba sababbin dinkin da aka mata, nan ta zabi wani lace mai an karan kyau yasha duwatsu, ta fara kokarin sawa a jakar hannunta da aka sai mata.

Goggo ta bude labule tana kokarin shigowa, kallan Jalila tai tace "ke da zaki makaranta me zakiyi da kayan gida?"
Ta karasa shigowa da kyar ta samu ta zauna.
Jalila tai murmushi tace "Goggo yau fa ake yaye mu."
Tace "to sai akai ya?"

  Jalila tace "Ana gama taran ai zamu kwabe mu shiga kayan gida ai shagali."

Goggo ta tabe baki cikin rashin gamsuwa tace " Wai yaushe aka fara haka a makarantar Gomnati ma?"

Jalila tai dariya tace " ina kike fita balle ki sani?"

  Goggo tace "Hmm amma ai kyaci abinci ko?"
Jalila tace " Ni bana jin yunwa sannan za'a kawo abin saidawa a makaran........."
Kallan da Goggo ta matane yasa ta zauna da sauri tare da bude kular abincin, tea ne da bread da
farfesun naman kai."

Jalila ta dade kafin ta bude bread din, har goggo tace "menene?"
Jalila tai yake tace "rayuwa kawai nake tunani Goggo, wai yanzu mune ake bamu abinci ba tare da munyi musu aiki ba, Goggo kin manta sanda muke musu wanki? Mu musu komai na gidan?"

  Goggo tace " rayuwa kenan Jalila, insha Allah wahala ta kare miki a rayuwa."
Jalila tai murmushi sannan ta fara cin abincin, bazata cemata iyaye suna zuwa ba dan ta tabbbar zataji ba dadi, gashi ita ba lafiyar kafa ba."

Tana gamaci ta fito, Sultan ta gani yana kokarin shiga mota, tace "Sultan?"
Tsayawa yai har ta iso, tace "ina zaka?" Ta dauka cemai akai ya rakata saboda gama makaranta da zasuyi.
Jitai Yace "In an kaiki makaranta ne zan wuce gidan kawu in amso sako." Sakon me?
Yace " kamar wai lefe za'a kawo."

Jalila cikin mamaki tace "lefe? Lefen wa za'a kawo?"
Yace "ina na sani?"
Ya fada tare da shiga motar.
Jalila ta shiga tana mamaki, bikin Safeena za'ai? Amma bataji labari ba, to ko amsar kayan za'ai kawai a gidan?"
Ganin batada amsa yasa ta share.


  Yau yan mate dinsu Jalila ansha uban kwalliya, sai iyayi akeyi.

  Haka aka fara programs kowa iyayensa da yan uwansa sai zuwa sukeyi, Jalila tana zaune dan tasan ba wanda zata gani.

  Zarah ce ta tabata tace "Jalila Yaya yazo dasu Umma."
Nan sukaje suka gaishesu, Jalila tana zaune daga inda take tana hango Uncle Sagir, insuka hada ido sai suyi ma juna murmushi.
Ganin Uncle ne ma yasa ta cire komai a ranta har aka gama programs.

  Nan sukaje suka canza kaya kowa yasa kayan gida suka dau kwalliya, masu waya sunata yin hotuna, Zahra ma ta zo musu da waya sai hoto ake tayi.

  Wata monitor din Jss3 ce ta shigo ajin nasu, nan ta nemi inda Jalila take ta tabata.
Jalila ta kalleta tace " Hadiza ya akai?"
Mika mata wata yar karamar jaka ta kwalli tai tace "gashi inji Uncle Sagir."
Jalila ta amsa tana bude jakar.
Kwalli ta gani ta jawo,Zahrace ta matso ta fizgi kwallin tana cewa " me muka sa......"
Ganin waya yasa ta kalli Jalila tace " yeee!"
Jalila ta harareta sannan ta fizge wayar tace " muga."
Ganin Wayar ne ya sa ta kallan Zahra, hannu tasa cikin jakar ta zaro wani karamin card.
Bude shi tai taga ansa
_To u my dear!_
_Congratulation on your graduation, here is my small gift, hope you will accept it._
Zarah ce ta kara amsar wayar ta bude ta, wayace mai tsananin kyau Sumsung Note 5 ce.
Kan kice me Zarah ta fara haska Jalila wacce tai tsuru tana kallan ikon Allah.

  Fitowa tai daga ajin ta shiga nemanshi, can ta hangoshi cikin mutane.

  Tsayuwa tai dan bata san ya zatai ba, juyowa yai kawai sai hangota yai daga nesa.
Yaune rana ta farko da ya ganta cikin shiga haka mai kyau dauke da kwalliya, sannan wannan ne rana ta biyu daya ganta ma da kayan gida a iya zamansu, na farko sanda ya fara ganinta sai kuwa yau.

  Kasa dauke ido yai daga kanta wanda har hakan yasata tsarguwa.
Juyawa tai da sauri ta shiga class din.
Zahra ta matso tana nuna mata hotunan da ta mata.

  Jalila kam bata kula taba dan hankalinta nakan Uncle dake waje.

  Daina hangoshi tai hakan yasa ta fito daga class din tana lekensa.
Zarah ce ta miko mata wayar da sauri tace "Zarah Yours na kiranki."
Jalila aji abin banbarakwai, kallan wayar tai a jiki an saka MINE dariya tai sannan ta kalli zahra tace ya ake daga wa?"
Mamaki ya kama Zahra sai dai kafin ta farga Jalila tana gwadawa kawai taga yaja hakan yasa Zahra tai tunanin iskanci take mata.

Jitai yace "Banga kwalliyar nan ba, tunda ba'a ganni ba sai a taimaka azo inda muke haduwa."

  Murmushi tai sannan tace "to."
Kallan Zahra tai sannan tace "ina zuwa."

Nan ta fara tafiya.


  Yau a kan mota ta ganshi, karasawa tai fuskarta dauke da murmushi da kuma kunya.
Tana isa ta gaisheshi, yace "Irin wannan kyau haka ai sai kisa in rasa gane hanya."
Kallansa tai tace "Uncle wannan gift din yayi yawa, bana tunanin zan iya amsa, Goggo ma fada zatamin"
Yace " to Jalila ya kikeso muyi? Kingama skul nima na gama service a ina kikeso indinga jinki? Ke ba waya ba? Sannan ko zuwa zan dinga yi kina tunanin za'a barni nazo kullum?"
Jalila tace kullum? Yace sosai in har bazaki amshi wayar ba sai dai ki amince kullum nazo muyi awa uku tare.

Da sauri ta zaro ido dan tasan wannan inaa bazai yiwu ba.
Ji tai yace "bazai yiwu ba ko? To kinga kawai ki hakura."

  Jalila tace "Amma....."
Yace "mu bar maganar nan please."

Kallansa tai dan batasan me zata ce ba..........

Hira suka shiga yi ta masoya masu tashen soyayya, Kiran wayarsa da akai ne yasa ya kalli wayar mamaki  yai dayaga Mine a jiki dan number Jalila ce.
Nan ya daga yana cewa wayarki na gun wa?
Tace Zahra
Zahra na dagawa tace "Uncle wai Jalila tazo anzo daukarta."
Uncle ya kalleta yace "wai anzo daukarki."
Mamaki ya kamata tace "amma nace sai bayan azahar, gabanta ne ya fadi badai wani abun bane ya samu Goggon ta?"

Kallan Uncle tai a tsorace tace "Uncle bari naje gida."

Zahra na tsaye kusa da motarsu, wayarta ta mika mata ta bata jakarta, nan Jalila ta sa a cikin jakar ta shiga ciki sukai gaba, addu'a kawai take Allah yasa ba wani abun bane ya samu Goggonta.


*£*£*********


  Goggo tana zaune wajen karfe 12 Yasmeen tazo da gudu wai tazo inji Inna.
Tayi mamaki sosai dan tanaji tunda take a gidan Inna bata taba nemanta ba haka kawai.

Samun kanta tai da faduwar gaba.
Haka ta taso da kyar saboda ciwon kafa ta karasa.

  Tana shiga falon taga Inna, Dady da Mumy a zaune.
Faduwar da gabanta ya shiga yi ne kawai ya sa ta shiga yin addu'a dan ta tabbatar ba lafiya ba, shiga tai a hankali.
Mumy ta mata nuni da kujerar dake gefe tace "ki zauna anan."
Goggo ta zauna sannan ta gaida Inna ta gaida Dady da Mumy.

  Bayan sun amsa ne falon yai dan shiru.

Goggo tace "lafiya?"

Inna tace "Gobe za'a kawo kayan lefen Jalila."

Abin yazoma Goggo a ba zata wanda yasa tace "lefen Jalila kamar ya kenan? Dan banaji ta taba sanar dani tanada miji."

  Inna tace " ba sai ta sanar dake tana da saurayi ba, dan kuwa hakkin mahaifi ne ya zaba mata mijin da yaga ya dace da ita, sannan shi Abbakar ya fitar da nasa hakkin na yi mata miji yanzu hakkin 'ya ne tabi umarnin mahaifinta."

Goggo ta kalli Dady da sauri tace " Abbakar me kenan?"
Yace "hakan da kikaji shine."

Cikin daga murya tace "da tunda aka haifeta bakasan da hakkin ta akanka ba sai yanzu? Dama wlh ni jikina yaban mutuncin da kuke mata da wani abin a kasa, ashe aurar da ita zakuyi? Mijin mahaukaci ne ko dan shaye shaye? Ko kuwa barawo ne? Ko kuma nakasasshe? Ko kuma dan fashi ne?"

Mumy tace "ya zaki fadi haka, Abbakar fa ubanta ne ta ya za........."

Goggo cikin tsawa tace "Ba dake nake ba."
Yanda tai maganar ne yasa Mumy tsorata dan bata taba ganin Goggo  na fada haka ba.

  Goggo cikin fada tacigaba " me ka mata a matsayinka na ubanta? Me ka mata?"
Dady shim ya kasa magana dan bai taba ganin tana fada haka ba.

  Goggo fa mike da kyar idanunta sun canza tace " duk abinda kuke ma tunanin ku ajiye dan wlh ba wanda ya isa ya yima Jalila auren dole."

  Juyawar da zatai taji wani jiri na debanta, kan kace me tayi baya luuuu jikake tim ta fadi a kasa.

  Da sauri suka mike suna jijigata.

Jalila wacce ta shiga bangarensu da gudu taga ba Goggo jakarta ta cilar a dakin sannani ta fito ta nufi bangarensu Mumy dan tambayarsu,ganin Goggo a kasa su Dady da Mumy na kanta yasa ta karasa da gudu jikinta na bari.



#ONELUV💕
[08/10, 02:02] ‪+234 803 222 1758‬: 🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*

(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*No 14*


  Dady a rikice ya nufi daki ya dauko key din mota ganin yanda Goggo take a kwance ga Jalila sai wani irin kuka takeyi.
Jiyai ance "ABUBAKAR."
Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalli Inna, kallansa tai tace "ina zaka?"
Yace "Asibiti."
Tace "dawo ka zauna."
Tsayawa yai yana kallan Goggo sannan ya kalli Inna.

Mumy ce ta kalli Inna tace "Inna kingafa......"
Kallan data mata ne yasa ta yin shiru, Jalila a rikice ta jawo gwiwarta ta iso inda Inna take tace "Inna dan Allah ki bar Dady ya kai Goggo asibiti, duk da bansan me ya hadaku da Goggo ba har take nan bangaren sai dai na rokeki da ki yi hakuri."
Hannunta ta hada guri daga tana ta murzasu tana kuka alamar tsantsar neman taimako.

Ganin Inna batada niyyar kulata yasa ta ja gwiwa zuwa gun Dady ta rike kafaraa tace "Dady ka taimaka dan Allah, karka manta Goggo matarka ce, sannan mahaifiyatace."

  Gani tai Dady ya kalli Inna, hankalin Jalila ne ya kara tashi ta matso kusa da Mumy ta rike gwiwowinta tace "Mumy ki taimaka min, bazan sake yima Safeena laifi ba, sannan zan cigaba da yi muku aiki, dan Allah ku taimakeni ku kai Goggo Asibiti."

  Muryar Inna ce ta katseta da cewa " kinaso a ceci ran mahaifiyarki?"
Jalila a rikice tana kuka shabe shabe ta shiga daga kai ba kakautawa, Inna tace " akwai hanya daya mafi sauki, wanda in kika amince da ita bama kaita asibiti ba hatta kula da ita zamu samo wanda zai dinga yi, sannan asibiti duk tsadarsa zamu kaita indai zata samu lafiya."

  Jalila a rikice tace "ko me kukeso ku fada zanyi dan Allah."

Inna tace "ki amince da auran da Mahaifinki zai miki."

Gabanta ne ya fadi ta kalli Dady idanunta jagab da hawaye, yana ganin sun hada ido ya juyar da kansa gefe.
Jalila tace "ban gane ba Inna."
Inna tace "in baki gane ba sai ki bar Goggon taki ta karasa rayuwarta anan."

  Wani irin fitar da numfashi da Goggo tai shi yasa Jalila rikicewa ta karasa gunta da gudu tana kuka.
  Inna tace "kina tunani ne akan maganar? Ashe baki dauki ran mahaifiyarki da daraja ba kenan tunda kina tunanin yanda zakiyi tsakanin lafiyarta da farincikin ki."

  Jalila ta kalleta tana kuka tace "ko ma dawa zaku hadani na amince ni dai dan Allah ku kai Goggo asibiti."
Inna tace "yanzu kikai magana, Abbakar kai Mahaifiyarta asibiti, sannan ki sani gobe za'a kawo lefenki da sa rana."

  Jalila kam kuka kawai takeyi, haka Dady da Mumy sukasa Goggo a mota Jalila ta shiga baya suka fita.

Asibitin Standard sukai parking, Jalila kam banda kuka ba abinda takeyi, ana shiga da Goggo nurse ta nufi office din likita dan sanar da ita halin da Goggo take ciki.

  Jalila na zaune a kasan beni kuka kawai takeyi tana addu'ar samun lafiya ga mahaifiyarta.

Dady na zaune shida Mumy, sunyi shiru suma.
Sai da suka samu da taimakon Allah numfashinta ya daidaita sannan suka shiga yi mata gwaje gwaje.

  Sai da suka gama sannan suka fito aka kira Dady.
Likitan ce kalleshi tace "wani maganin hypertension take amfani dashi?"
Yace "hypertension?"
Tace "kanaso kacemin bakusan tanada shi ba?"
Dady ya girgiza kai alamar rashin sani, tace "diabetes fa?"
Dady yai shiru nan ma.

Tace " menene tsakaninka da ita?"
Kunya tasa yace "yar uwatace."
Cikin rashin jin dadi tace "wannan wani irin abu ne? Batada miji ne? Ko kuwa neman kasheta yakeyi?"

  Dady yai shiru, tamai bayanin ciwon ta wanda ya riga ya ci jikinta sosai, tace " ta ya za'ayi ku bari diabetes har yai nisa ya ci kafarta?"
Dady yace "ai mun dauka ciwon kafa ne na girma."
Tace "ko ciwon kafa ne na girma ai kwa gwada zuwa asibiti, da kunzo da wuri ai za'a sanar daku ba shi bane." Sosai ta nuna masa laifinsu sannan ta bashi takardar magunguna tace yaje pharmacy dinsu.


  Jalila na zaune kusa da Goggo tana kuka, ko mayafi babu a jikinta dan kwalli ne kawai a kanta.

  Dady sai da ya gama biyan kudin komai sannan ya shigo dakin, Jalila ce ta kalleshi batace komai ba.
Dady yace "ya jikin nata?"
Kasa amsa mai tai dan gaba daya yau tana tir da kasancewa  uba a gareta.
Duk wani mutum mai imani bataji zai yiwa matarsa abinda dady ya ma Goggo yau.

  Dady ganin yanda Jalila ta dauke kai daga kansa yasa ya fito.
Mumy ya tadda a zaune yace " mu tafi."
Tace ya jikin nata?"
Bai bata amsa ba ya wuce mota.
Suna shiga ya kalli Mumy yace " yanzu abinda Inna tai dazu ta kyauta?"
Mumy ta riko hannunsa tace "nima banji dadi ba sai dai kafi kowa sanin duk abinda Inna takeyi tanayinsa ne saboda mu, na tabbatar ba a san ranta itama tai haka ba."

Shiru yai baice komai ba yaja motar sukai gaba.



  ******



  Ummy ce take ta buga mai kofar yanaji sai dai ya kasa mikewa ya bude, yana takure a gefen bandaki ya matse kansa da karfe, zufa nata karyomai, jikinsa sai rawa yakeyi.

  Ummy ganin ba alamar budewa yasa ta sauka kasa da sauri tana kwallama Sagir kira.
Sagir na kwance a falon kasa yasa waya a gaba sai gwada number Jalila yakeyi sai dai tai ringing har ta gaji ba'a daukaba.
Jin yanda Ummy ke kiransa yasa ya mike da sauri yana tambayarta Ummy lafiya?

Ummy

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login