Showing 57001 words to 60000 words out of 146738 words

Chapter 20 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt

23 Nov 2025

5774

kunya naji."

Kallanta ya tsaya yanayi.
Kanta ta maida kasa tana kara rike kofar, can ta saki dan kara ta rike hannunta tace "wayyo hanuna."

Kallanta yai yace "hannu?"

Jinginna tai da bango tana dan murza hannun, sakin kofar yai ya shigo yana cewa "menene?"

Da sauri tai waje da gudu tana dariya.


Tsayawa yai kawai yana kallan ta, lalai yarinyar nan.

Dariya ta shiga yi tana cewa "yaya wai harka shiga?"

Hassan ya hade rai ya fara nufo ta, ganin yanda idanunsa suka canza yasa ta tsaya cikin tsoro tanayin baya.

  Sai dayaje daf da ita sannan ya zauna akan gado bai ce mata komai ba ya dau littafinsa.
Kallansa tai jiki a sanyaye tace " Yaya bakai dinner ba."

Kallanta yai yanzu ma baice komai ba, tai shiru ta zauna a gefen gado daga karshe.

Shiru ne ya ratsa dakin kafin can yace "Jalilah!"
Kallansa tai da sauri, yauce rana ta farko da ya kirata da sunanta cikin wannan muryar, murya ba mai dauke da zafi ko fada ba.

Idanunta na kansa yace " Jalilah Please take care of Ummy."
Idanunta na kansa tana kallansa ta daga mai kai alamar fahimta sannan tace " Insha Allah."

Haryanzu idanunsa na kanta yace " Nagode."

Kanta ta sunkuyar sannan tace "nima na gode Yaya da taimakon da kamin."

Yace " me kika ce ma Goggon taki?"

Ta kalleshi da raunanan ido tace " ban iya cemata komai ba, bansan ta ina zan bulo ba, bansan me zan ce mata ba."

Ta karasa magana tana share kwalla, kallanta yai yanasan lalashinta sai dai bai san ta ina zai fara bama.
Kansa ya dauke daga gunta, wayarsa ya dauka ya dubo sunan Abba.

Rabon daya kirashi harya manta, sai dai shi Abban ya nemi shi.
Dialing yai yana kallan agoggo, goma saura.
Yanajin wayar har ta gama ringing bai dauka ba, idanunsa ne suka kara canzawa ya sake kira, tana daf da katsewa Abba ya daga cikin mamaki da shakka.

Kallan Abokinsa yai sannan ya mike daga falon ya fito waje.
Ya daga yana cewa "Hassan!"
"Abba kana ina?"
Jalila ce ta kalleshi da sauri, Abba yace "nayi tafiya ne, baka tambayi Ummynka ba?"

Hassan yace " na dauka akan tafiyarne kukai fada?"
Abba cikin mamaki yace "Haka tacem?" Yana mamakin kiran da Hassan yamai da kuma mamakin yanda yake tambayarsa, duk da Hassan na tsananin san Ummy bai taba shiga maganarsu ba, me ke faruwa?"

Hassan harzai sake magana sai kuma ya kashe ya cillar dawayar gefen gadon.

Jalila tai shiru tana kallansa, mikewa tai tai shimfida dan yanda ta ganshi tasan da matsala.

Bata dade da kwanciya ba bacci yai gaba da ita.

Hassan kam ya dade kafin ya mike ya sauko kasa.
Sai daya leka Ummy yaga tana bacci sannan ya juya ya koma sama.

Jalila ya kalla wacce ke bacci, daga gefen gado ya kwanta har bacci ya daukeshi.

Yanda jikinsa ke kadawa da yanda yake abu kamar maiyin kuka yasa cikin baccinta ta farka.

Da sauri ta kunna wayarta sannan ta kunna fitilar dakin.

Bakinsa sai kakkarwa yakeyi, da sauri ta karasa kusa dashi ta kamo hannunsa.

Ganin yana neman fadowa daga kan gadon yasa ta rungumeshi tana hawaye tana kiran sunansa.

Idanunta a runtse, hawaye kawai ke zuba.

Ta kankameshi, sun dade a haka kafin nimfashinsa ya fara daidaituwa.

A hankali ya bude idanunsa ya zubasu akanta, hawaye kawai take tana kiransa.
Yanda ta rungumeshi ne yasa ya kara kallanta sannan yace "Jalila!"

Idanunta ta bude ta kalleshi, bakinta na rawa tace "Yaya?"

Yace "wannan rikon fa?"

Sakeshi tai tana kallansa, ya kalleta yace "baki iya addu'a bane sai kuka da kiran sunana?"

A hankali tace "banyi islamiya ba."

Kallan mamaki ya mata da tausayawa, sannan yace " kukan fa? Are u worried about me? Or are u scared?"

Kallansa tai bata iya cewa komai ba.

Agoggo ya kalla, karfe biyar saura, mikewa yai ya nufi toilet har zai shiga sai yace " forget what I just said."
Sannan ya shiga, ajiyar zuciya tai sannan ta sa hannunta shafi fuskarta.


**********
A abuja kuwa, Abba ya kalli Abokinsa Hafiz yace " sry muna magana yarona ne ya kira."
Hafiz yace " to yaya? In sanar da ita ne ko ka fasa?"

Abba yai shiru kafin can yace "bari dai sai zuwa gobe, in na sake yin nazari."
Hafiz yai dariya yace "nazarin me? Bayan abinda ranka ke so ne sannan ba haramun bane?"

Abba yai shiru yana tunanin yanda idanun Hassan sukai alokacin daya shigo, can yace "sai dai goben."
Hafiz yace shikenan Allah ya kaimu.

Nan Abba ya fito, yana neman fita gate yaji muryarta tace "Ba gaisuwa?"

Juyowa yai da sauri ya kalleta, gani nai ya hadiye wani yawo, Zaliha tayi kyau iya kyau kamar mai shirin zuwa dinner doguwar riga ce a jikinta ba dankwalli balle mayafi.

Gashin kanta kawai ta saukar wanda yasa gyara.

Bakinsa na rawa yace "Zaliha ko?"

Ta dan kashe mai ido sannan ta matso inda yace tace "badai sunan ma an manta ba?"

Yai dariya yace " ina zan manta?"

  Tace "muje ciki mu gaisa, bana iya jurar tsayuwa."

Nan yaga ya juya tana gabe yana binta a baya, komai na jikinta motsi yakeyi.


#OneLuv💕


🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*Thanks for all your comments, it really give me strength 💪🏼lol.....Really Love u 💕 *

*35*

Abba yaje shiga falon ya tsaya yana kallanta, meke faruwa dashi? Me yasa baya iya controlling din kansa? Juyawa yai da sauri yana neman fita, hannunsa yaji ta kamo.
Kallanta ya juyo yai cikin bacin rai sai dai yana kallanta yaji ya kasa cewa komai.
Tace "Tafiya zakai?"

Yace "a'a."
Haka taja hannunsa har cikin falon sannan ta zauna a gefen da yake.
Tace " Sai naga kamar na takura ma."
Yace "kamar ya kenan?"
Ta dan shagwabe fuska tace " gashi nan ka hade rai."
Da sauri yace " ba hade rai nai ba, kiyi hakuri."

Murmushi tai sannan ta zubo mai juice a cikin cup ta mikomai tace " gashi."
Amsa yai yana kallanta yana sha, can yace "Zaliha inaji ya kamata na tafi."

Kanta ta kwantar akan kafadarsa ta sakala hannunta cikin nasa tace "da wuri haka? Ni anya ka damu dani kuwa?"

Taura bakinsa na rawa yace "damuwa dake din danai shiyasa kika ganni anan garin, nabar tarin aiyukan dake gabana."

Murmushi ta saki sannan tace " nikaina mamakin yanda zuciyata ta kamu da kaunar ka nakeyi."
Washe baki yai yace " nikaina ban taba tunanin hakan zai faru dani ba."
Haka tai ta jansa da hira tana kara dirkamai juice din abarba da kwakwa da suka hada wanda suka hadashi da rikaken maganin da aka basu.

Sai dare sosai ya tafi shima harda wani kwallarta wai batasan ta rabu dashi.
Haka ya lalabata ya tafi, da yaso barin garin washe gari amma dole ya hakura sai jibi.

Yana fita ta shiga dakin Yayarta da gudu tace "Aunty !"

Kallanta tai ta mata alama da tai shiru, nai tai shiru ta matso kusa da ita tace "Aunty gaskiyar malamin nan kinga yanda ya mato kuwa?"

Auntyn tai dariya tace " an fadamiki barno gabas take? Sanda malamin yace mu koma gida zaizo da kansa me nace miki?"
Tace "ai ni ban dauka abin zaizo da sauki haka ba."

Tace " kedai kiyi abinda malam yace karki kuskura ki nemi jin rayuwarsa da matarsa ko 'yayansa har sai mun amso dayan maganin."
Tace "To Aunty zan kiyaye."
Nan ta fito tana murmushi, dolene ta fara rubuta abubuwan da take bukata intayi aure da irin wayar da takeso, da motar da takeso da gidan da takeso.
Dan bataso a wuce wata daya basuyi aure ba.

Taura kuwa yana shiga hotel dinsu yai sallah sannan ya kwanta akan gado yana kara tunano abinda ya faru dashi, yaushe zuciyarshi ta koma budurwar zuciya? Me zai cema Ummy? Sagir? Ameera? Has......... goshinsa ya dafa dan ya tabbatar akwai gagarumar matsala babba in Hassan yasan halin da ake ciki, dan tabbas shikansa tsoron abinda zai biyo baya yake.

Baisan sanda ya dau waya ya kira Zaliha ba, nan ya baje sukai ta hira har sha biyu sannan ya kwanta.

*********

  Jalila kam batai baccin safe sosai ba dan karfe takwas ta sauko danyima Ummy abinci, dankali ta fara firewa bayan ta saka tafashen naman kaza, tana suya tana dan kara gyara kitchen din har masu aikin gidan suka iso.

  Bayan ta gama suya ne tadan tafasa indomie tai awara da ita sannan ta jera akan dinning.
Dakin Ummy ta nufa ta kwankwasa.

Ummy ta taso ta bude mata, Jalila ta rusuna ta gaisheta sannan tace "Ummy ya jikin?"

Ummy tai murmushi tace " Jalila na warke, na barki da aiki ko?"
Tace "kai Ummy wannan ne aiki?"

Ummy ta riko hannunta suka fito falo tana cewa "Hassan fa?"
Tace "bacci yake sanda na fito."

Ummy ta dan tsaya sannan tace "Jalila haryanzu a kasa kike kwana?"
Jalila ta sunkuyar da kai saboda kunya sannan tace "Ummy yaya ya fara canzawa, yanzu yana amsawa in namai magana."

Ummy ta jinjina kai cikin jin dadi tace "na gani Jalila, ai tunda ya fita dake a mota nasan Hassan ya fara canzawa, ko Ameera bai taba fita da itaba a motarsa."

Jalila tai murmushin jin dadin yanda taga Ummy na farinciki.

Ummy ta kara rike hannunta tace "Jalila nagode sosai, nagode har bansan yanda zan miki godiya ba, nasan kina shan wahala da kuka da Hassan."

Jalila ta sunkuyar dakai tace "Ummy ki daina fadar haka dan Allah."
Ummy ta jawota ta rungume tace "Jalila mu dauki junan mu a matsayin uwa da yarta, mu ajiye surukantaka a gefe."

Ta dagota tana kallanta tace "Ameera bata fiya zama muyi hira ba, saboda makaranta in ta tafi tun safe sai uku da rabi sannan islamiya karfe hudu, tana dawowa assignment da gajiya su hanata zama ayi hira, Sageer kuwa shine ma muke hira dashi shikuma kinga namiji ne, balle kuma ince Hassan."

Tai ajiyar zuciya tace "inaso mu dauke junan mu da mahimmanci."

Jalila ta daga kai cikin jin dadi tace "To Ummy insha Allah."
Haka suka karasa dinning, Ummy ta bude kulolin sannan tai murmushi tace "inama Hassan zai sauko muci abinci dukan mu?"

Jalila ta kalleta, Ummy tace "later, mu bi abin a sannu, kar san zuciyata yasa mu rikita komai."
Jalila ta daga kai tare da cewa to Ummy.

Ummy tace kizo ki kaimuku naku, Jalila tace "ke fa? Ke kadai zaki yi breakfast?"
Tace "Sagir na nan nasan ya kusa fitowa."

Jalila ta zo ta zuba musu ta hau sama dashi.

Tana tura kofar yana kokarin saukowa daga kan gado da alama tashinsa kenan, Jalila ta ajiye tiren sannan tace "Yaya ka tashi? Ya jikin?"

Kallanta yai sannan yace "Ummy fa?"
Ta dago tana cewa tana falo, ya mike ya nufi toilet.

  Tana gyara gado ya fito, dayan bangaren ya karasa yana tayata gyarawa, kallansa tai tace "yaya barshi, ka zuba abinci."
Bai tanka mata ba har ya gama sannan ya zauna ya mike kafa yace "zo ki zubamin, tunda kin damu sai naci yanzu."

Jalila tana murmushi ta matso ganin zata wuce yasa ya shiga kokarin janye kafarsa daya mike, ita kuma da sauri ta taho yana kokarin janye kafar ita kuma bata kula ba tai tuntube, tahowa tai zata fadi ta gaba, da sauri yasa hannu dan tareta, duk da haka sai da shima ya kai kasa, ta fada kansa kif.

  Hannunta na hagu ya bugi bango, da dan sauri tai kara, da sauri ya kalleta yace "Jalila? Menene?"

Kallansa tai tace " bigewa nai."

Harararta yai yace " raguwa, shine harda wani kara haka? Ni da kika danneni fa?"

Ta dan dago ta kalleshi, yace "sai yaushe za'a dagani?"

Da sauri ta murgina gefe sannan tadan hade rai kadan, ya kalleta yace " karki ma fara shirin yin pretending I won't fall for it twice, ki zubamin inci ko ki dauke abincinki."

Jalila bata san sanda tai dariya ba tace "au in ban zuba ba sai kaki ci?"
Yace "Ehem, kina wasa ne?"

Tace "a'a ina na isa in hana dan Ummy abinci?"

Ta fada tana zubamai a plate, kallanta yai bayan ta gama zubawa sannan ya fara ci.

Itama ta xuba taja gefe tana ci, batai auni ba taji yace " yaushe zaki koma?"

Kallansa tai tace "Ina.....?"
Sannan ta kara fadada dariyarta tace " Gun Goggo?"

Bai kalleta ba, da sauri ta tsame hannunta ta matso inda yake tace "Yaya da gaske?"

Kallanta yai sannan yace "me kike shirin yi? Yanzun ma pretending din faduwa zakiyi dan in tare ki?"

Kallansa tai tana dariya sannan ta matsa daga matsowar da tai tana cewa "wlh dazu faduwa nazo yi."

Bai kalleta ba, ta jawo kwananta kusa kadan tana cewa "Yaya yaushe zamu? Yau? Gobe?"

Tea yadan kurba sannan yace " yanda kika damu da Mahaifiyarki me yasa kike tsoro?"

Har tayi shiru kamar bazata amsa ba kafin tace "a haka na taso, daga ni har Goggo bamu da daraja bare matsayi."

  Idanunsa na kanta yana dan nazari kafin yace "ki binciki mahaifinki, banaji akwai igiyar auranta akanshi."

Jalila ta kalleshi tace " To yaya, ni tsoro nake karma su kara dauke Goggon."

Kamar bazai tanka mata ba sai taji yace "sai ke ki dauketa kafinsu su dauke ta."

Da sauri ta kalleshi tace "kamar ya?"
Abincinsa ya cigaba da ci, yana gamawa ya mike yai toilet, shiru tai tana nazari kalamansa wanda bata fahimta ba sam.........


*******

Inna ce ta kalli Mumy tace " waccen sokon yaje gun Jalilan?"

Mumy tace "Inna wai dan Allah meyasa kike haka ne? Karfa ki manta mahaifin jikokinki ne."

Tai dan tsaki tace "ni tambayarki nake yaje ko baije ba?"
Tace "wai tayaya zaije gidan sirikansa yana namiji?"

Inna tace " ta yaya zaije? Ki tashi ki sanar dashi in har shi ya kasa zuwa ya ja mata kunna ni zan yi abinda ya dace, tun kafin zance yakai gun matar Taura har yaje gunta"

Mumy tace to ta mike ta sauko fuskarta a hade.


*******

  Zaliha zaune a cikin mota tana jiran Abba wanda ya fita siyo musu abu ya dawo, ta sa hannu ta dau wayarsa, ba security hakan yasa kawai ta bude ta shiga gallery tana kallan hotuna, ba wasu pictures bane a ciki yawanci na aikinsa ne, sai Matarsa da ta gani wace ta riga dama ta santa, sai Ameera data gani daga baya wace taga tsantsar kamar matarsa a fuskarta.

Maza biyu ta gani sunsa kaya iri daya da alama basu ma san sanda aka musu hoton ba saboda kallon wani gun da sukeyi, dayan fuskarsa a hade ba alamar dariya da alama labarin ba burgeshi yai ba, dayan kuwa fuskarsa a sake take.

Kurama wanda ya hade fuskar ido tai, waye wannan haka? Waye haka??????


Nace kece inaji kika koma haka😏

Ajiye wayar tai tare da kallan titi, ita ba tsarin soyayya a ranta ba kuma ta tunanin soyayya shine abunda ya dace da ita, abu daya ta sani a rayuwa ta ganta a katan gida a katuwar mota da waya mai masifar tsada, to komai ya biyo bayan wadannan.....


#OneLuv💖

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*


     *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
  (_D home of expert and perfect writer's_💡)



*36*


Ameera ta kalli Aina’u tace “dan Allah kizo mu tafi tare.”

Aina’u ta maida kanta ta kwanta kan gado tace “dan Allah kimin uzuri, kema kinsan bazan iya zama a gidan ku kamar da ba.”

Ameera ta dan hade rai tace “kin san da haka me yasa ke da kike yar uwa har kika bari bare ta aureshi in har kinsan kina sanshi?”

Aina’u ta mike ta zauna akan gado tace “Ameera ni kike so in kai kaina gunsa?”
Tace “daga baya kenan, kema tun farko kinso rigima kinfi kowa sanin Halin Aunty Nana da yanda ta daura buri akanki, me zaisa ki wani fito da zancen wai kinasan yaya?”

Aina’u ta kafe ta da ido cikin rashin jin dadin kalamanta, Ameera ta mike tace “ in ba so kike zumuncinmu yai rauni ba ki cire wannan zancen, ki ajiye shi a cikin dakin nan, na rokeki da Allah.” Ta karasa maganar tare da shiga toilet.

Aina’u ta bita da kallo tasan gaskiya ta fada mata amma duk da haka sai dataji zafinta.

Komawa tai ta kwanta cikin takaici.

Ameera na fitowa ta kalleta sannan ta bude kofa ta fita falo ba tare da ta mata magana ba.

***********

Jalila tana zaune a falo tana kara tunanin kalaman Hassan, haka ta sauko tana girkin rana amma tana kara maimaita kalaman a ransa, me yake nufi? In ta dauketa ta kaita ina to?

Batama san Ummy ta shigo kitchen din ba sai ji tai ta tabata.


Kallanta tai da sauri tace “Ummy!”
Ummy tai murmushi tace “tunanin me kike haka? Kin kunna fanfo yanata zuba?”


Jalila ta kashe fanfon da sauri tana cewa “wlh ban kula ba sam.”

Ummy ta karaso ta dau cabbage ta fara yankawa tana cewa “ Hassan ne?”
Da sauri tace “ba shi bane.”
Tace “Nice?”
Jalila ta tsame hannunta tana cewa “ke kuma Ummy?”
Tace “eh mana, kinsan dan Adam ajizine, to ko Sagir ne?”
Tace “wlh ba kowa Ummy kawai abu nake tunani.”

Tai murmushi tace “ to ki rage yawan tunani haka, in kin kasa fahimtar abu ki tambayi wanda ya saki a duhu ko kuma ki nemi wanda zai fahimceki.”

Kai ta daga cikin jin dadi tace “nagode Ummy.”
Sannan ta ce “ina zuwa.”
Da gudu tabar kitchen din ta haw sama, tana hakki ta shiga cikinn dakin, yana kwance kamar me bacci ta shiga.

Kai ya girgiza kawai ba tare da ya kalleta ba, dan yasan in ba ita ba waye zai banko mai kofa haka?
Jalila ta isa kusa dashi tana hakki tace “Yaya!”
Idanunsa a rufe sai dai yadan yi motsi da hannunsa daya yake kan goshinsa, ta kara gyarawa sannan tace “Yaya dan Allah me kake nufi? Naga ni ba gida ba, ba yan uwa ba, in na dauketa in kaita ina?”
Ta karasa maganar tana hakki.

Bai bude idanunsa ba yace “ni zaki tambaya?”

Ta sa gwiwowinta a kasa sannan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login