Showing 129001 words to 132000 words out of 146738 words
Chapter 44 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt
kawai yayi, dan bazata tilastamai akan abinda bayaso ba.
Mumy ce ta kalli Hassan wanda yacemata “fado abinda kikeso ayi muji.”
Nan Mumy tamai bayani kamar yanda Sani ya mata, tace “duk yanzu kudin dake running a company din 80% kudin Mahaifinku ne, hakan yasa kuna da hujjar kwatar company din kuba wanda kukeso in har bamu biyaku kudin da kuke bin mu ba.”
Sageer yace “amma contract din ai kamar lokacin biyan nada tsayi.”
Tace “eh, sai dai nunawa zamuyi kamar abin yazo.”
Hassan yace “nuna wa zamuyi? Har a yaushe muka zama mu?”
Mumy tace “bada wani abun na fada ba, kuyi hakuri dan Allah.”
Hassan ya kalleta sannan yace “na kasa fahimtar wani abu, in an amshi company daga hannun mijinki wa kikeso a ba?”
Tace “ni kaina bawai so nake ba, saboda koda wasa ban taba burin mulkar company din nan ba, ni kaina shi nakeso aba sai dai bata wannan hanyar ba.”
Hassan ya mata wani kallo dan shikam ya dai jitane.
Yace “Sageer ya kake gani?”
Sageer yace “bari na kira Abba muyi discussing.”
Ya fada tareda mikewa.
Ganin za’a barsu su biyu yasa ya mike ya shiga kitchen.
Ta banyanta ya tsaya tana soya yankanken kayan miya akan frying pan.
Tana ganinshi ta juyo tana kallanshi.
Karasowa yai ya sa hannunsa ya zagayo da ita ta cikinta ya kwantar da kansa a kafadarta yace “kallanfa?”
Tace “ya kukai?”
Yace “kawai dai.”
Murmushi tai kafin tace “Thanks alot Yaya.”
Yace “banasan wani thanks kawai zanbi bashi ne dan sai an biyani.”
Murmushi ta sakeyi tace “da alama bashin nan nawa karuwa yakeyi dayawa.”
Sumbatar wuyanta yai yace “da alama zamu dan barki a gida ke kadai na dan wata awa daya.”
Kai ta daga alamar gamsuwa ba tare da ta tambayeshi ba.
Saketa yai sannan ya wuce sama, wanka yai yasa kananan kaya sannan ya sauko, Sageer ya tarar a falon Abba yana rike d wasu takardu yana kuma waya.
Yana ganin Hassan yamai alama dayazo, nan sukai magana su biyu kafin su fito falo.
A tare suka fita, Mumy ta shiga motarta suma suka shiga motar Sageer.
Suna shiga Hassan yace “haka Abba yace?”
Sageer ya shiga yimai bayani, Hassan ya jinjina kai alamar gamsuwa yace “shikenan.”
*************
Ba wani kato bane main branch din nasu, sai dai dayake ajiyar kayan abinci sukeyi daga baya akwai wani tangamemen fili da akai gini inda ake aikin a ciki.
Sani na ganinta ya taso da sauridan dama yana zaune a waje yana jiranta, tanna karasowa ya matso da sauri yace “sun shiga cikin meeting din kamar minti 5 da suka wuce.”
Mumy ta matso ta sanarma Hassan.
Dakin babban taro na hadaka suka nufa, suna zuwa Sani yasa aka bude dakin.
A lokacin kuwa Dady ne tsaye yana bada speech dinsa na yanda company dinsu wai ke cikin matsalar da suke san akawo mafita dan a kwatota daga ciki, Babban director din yace “Bravo! Gaskiya duk company din nan ba wanda yake sanshi da kula dashi kamar kai, shiyasa nazo da babban shawara akan sauke Hajiya wacce girma ya kamata yasa take neglecting din aiyukanta, a baka kai sirikinta wanda ka sadaukar da komai naka akan company din mu.”
Muryar Sani sukaji yace “Investors din da suka taimaki company dinmu sunzo.”
Kowa kallan su ya juyo yai, Mumy ta zubama Dady ido wanda gaba daya shima idanunsa na kanta.
Hassan ya matso inda Dady yake yace “will you please get down?”
Dady ya kalleshi zuciyarsa gaba daya ta rage bugawa yanda ya kamata, Hassan ya kalli Sageer yamai alama dakai akan ya matso.
Sageer ya kalli Dady wanda yake saukowa kamar wanda bashida ragowar laka a jikinsa.
Sageer ya fara bayani kamar yanda Abba yamai.
Takarda ya zaro ya daga sama yace “wannan shine contract din da mukai da company dinku akan za’a biyamu 50% na kudinmu a kwana uku da suka wuce.
A cikin wannan contract din munyi bayani time da kuma kudin da za’a fara biyanmu.
Sai dai jiya mun nemi Chaiwoman din company din me makon ta bamu sai ma taki daukan wayarmu, wannan dalilin ne yasa muka sauko kasan contract din wanda yace “in har ba’a biyamu kudin mu akan lokaci ba rabin company din zai dawo namu.”
Nan fa kowa ya fara kananan maganganu, Sageer ya kallesu yace “ saboda haka daga rana tayau zan zama nine shugaban company din nan har zuwa ranar da za’a biyamu kudin mu.”
Nan fa guri ya kachame da kananan maganganu.
Hassan kam abin ya birgeshi wani irin dadi yakeji a ransa, lalai ilimi rahama ne.
Hannu ya daga ya yima Sageer jinjina.
Dady kam ji yai gaba daya wata muguwar zufa na ketomai ta ko ina.
Wani daga cikinsu ne yace “ta ina zamu yarda da abinda ke faruwa?”
Sageer yace “da farko ga signing din Chairwoman din nan sannan ga yartanan zatai duba, dan tana nan akai komai, sannan zan miko muku ku gani kuma.”
Mumy wacce gaba daya dana sani ya gama kamata, jikinta duk ya gama yin sanyi, meke faruwa? Itakam ai ba haka sukai ba, ta dauka ko ita zasu barikon kwarya kafin ta samu Dady ya dawo hankalinsa, ya kamar take ganin anyi amfani dasu?
Haka tace ai komai daya fada daidai ne sannan aka mikama kowa ma ya gani, nan fa ba yanda suka iya aka ba Sageer kujerar shigabanci ya zauna akai.
Dady kam gaba daya ya koma mutum mara amfani dan jiyai ma dakin kamar ba kowa a ciki ba kuma abinda ake cewa a ciki.
Sai zafi da kirjinsa yakeyi......
Mumy kallansa kawai takeyi......
Sageer ya kalli Hassan sukai murmushi, Sageer ne ya tuno kalaman Abba dayace akwai tsuhuwar contract din da suka farayi dama time din da akasa kenan, to shi bai yaga ta ba shine yasa Sageer ya nemo, Abba yace da Jalila tayi nisa a karatu da ita zai sa aba wannan matsayin ko dan mahaifinta ya hankalta.
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
*72*
Gaba daya haka kowa ya fito daga dakin taron zuciyarsa a cunkushe da wannan al'amari.
Ya rage daga Hassan, Sageer, Mumy, Dady sai Sani ne kadai a ciki.
Mumy ta kalli Hassan tace "amma nikam ai ba haka mukai daku ba."
Hassan ya mata wani kallo yace "ke wacece da zaki tsara mana abinda kikeso muyi? Na dauka farincikinki kawai a kwace company din ne daga gun wannan, ba kuma naji kinada wani iko na samu ko hanamu."
Dady zuciyarsa takai makura dan dama daurewa kawai yakeyi, jin kalaman Hassann ya kara tunzuro shi, matsowa kawai yai naga ya daga hannu kamar zai gaurawa Mumy mari, sai kuma ya sauke hannunsa yana hucci, kamar wani kumurci sannan ya bugawa Hassan wani banzan kallo.
Hassan kam ganin yanda yake kallansa yake muzurai yasa shi yin wata dariya tare da cewa "bani na kar zomon ba, sannan ni na taba ganin wannan karfin halin?"
Cikin tsananin fada yace "karfin hali? Karfin hali fa kace, ka san wace irin rayuwa nai har na kawo wannan ranar?" Yadanyi kara cikin karaji yace "who are u? Da har ka isa ka wargazamin abinda nake shiri shekara da shekaru?"
Baa mumy taja saboda tsoron da Dady yake bata, Hassan ya hade fuska yace "rayuwar dakai? Wani ne ya saka? Kai fa ka sa kanka, sannan kai tambayar who am i? Nine wanda har karshen rayuwata indai har inada dama bazan taba barinka ka saci abinda ba naka ba."
"Sata? Sata nai? Uban waye yacce haka ake sata?"
Yace "To sanar dani in ba sata ba menene? Tsabar san zuciya ka wulakanta iyayenka, matarka, yarka, sannan yanzu kake neman ka sace abinda dayan matar da 'ya'yanka ke da shi."
Cikin tsananin zafin rai ya matso ya sa hannu da karfi ya hankade Hassan, baya yai saura kadan ya fadi ya rike teburin dake gun.
Dady yayo kanshi cikin fada yace "uban waye ya baka damar shiga rayuwata? Uban waye?"
Yanda yake yi ne yasa Hassan ya kura mai ido yana kallan ikon Allah, gaba daya ma mutanen dake gun ma kowa kallan mamaki yake mai, Mumy kam hawaye ne kawai ke zubo mata, cikin masifa yake kallan Hassan yace "Uban waye nace? Duk duniya duk wanda ya kuskura yace zai hanani abinda nasa gaba wallahi zan iya mai abinda ni kaina ban san zan iya ba."
Mamaki ne ya kara kama Hassan yace "ya zamuyi?"
"Dame?" Dady ya fada a harzuke, Hassan yace "dan banaji zan dakata daga nan, har kasa na fara zakuwa naga mai zaka iya aikatawa."
Cikin tsananin zafin rai da bakin ciki, Dady yakai hannu ya naushi Hassan, wanda sai da ya fasa mai gefen bakinsa, ya daga hannu zai kara Sageer ya rikeshi, Dady ya juyo cikin tsananin masifa yace "menene hakan?"
Hassan ya mike ya goge bakinsa, yace "ya zamuyi yanzu kuma?"
Dady ya mai wani kallo, Hassan yace "Sageer baka tunanin ya kamata a koreshi daga aiki?"
Sageer yace "ai ba sai ka bata bakinka ba Yaya, Zakai resigning ne ka fita da martabar ka ko kuma kafisan mu koreka?"
Dady yace "mene?"
Sageer yace "ba dai kana tunanin duk wannan bugun dakai a banza kayi shi ba? Sai dai fa kayi hakuri dan duk na dau video ina jiran naji uzurinka dayasa ka naushi investors din ku."
Dady ya zaro ido ya kalli Hassan gani yai Hassan ya mai wani murmushi sannan ya matso ya danyi ajiyar zuciya yace "in zaka saida shares dinka na company in gari yama zafi ka kawo Jalila zata siya."
Hassan yai gaba ya barshi a gun, cikin takaicin hali irin nasa, Sageer yace "sai naga resignation letter gobe a sabon office dina." Ya juya ya fita.
Dady ya saki wani irin ihu wanda ya kara razana Mumy.
Sani ma juyawa yai ya fita dan shikam hankalinsa ya kasa jawomai cikaken abinda ke faruwa.
Dady ya matso kusa da Mumy ya daga hannu ya sharara mata mari, ya kara daga hannu ya sake mata wani sannan ya nunata da yatsa yace "ke har kin isa ki sa wannan dan iskan yaran yacimin mutunci?"
Kallansa tai tana hawaye tace "Dear."e
Da yatsa ya kara nunata yace "don't you dare call my name like that."
Ya matso kusa da ita sosai yace "ni kika ci amana saboda bakyasan na zama wani abun ko? Na miki saki daya."
Kawai taga ya juya ya fita, gaba daya jitai kanta na wani irin juyawa dan ta kasa tantance takamaimai meke faruwa.
Batasan yawan mintinan da ta kwashe a tsaye ba kamar mara numfashi.
Yanda wayarta ke ta zuba kara ne yasa ta farga, daga wayar tai ba tare data dubama wanda ya kira ta ba.
"Mumy ki zo gida yanzu." Muryar Sultan taji a rikice yana fadar haka.
Da sauri ta fito ta fada mota sukai gida, wasu gardawa ta gani a cikin harabar gidan, gefe kuma Sultan ne a tsaye.
Tana zuwa ta karasa gunsu tace "lafiya?"
Turo mu akai akan ku tattara kayanku ku bar gidan nan.
Cikin mamaki tace "mu bar gidan kamar ya kenan?"
Yace "ko ku bar gidan gaba daya ko kuma yace ku koma boys quaters."
Yanzu kam ta gane wanene ya turo su, waya ta daga ta kirashi.
Kamar bazai daga ba sai taji ya daga, cikin mamaki tace "Abakar me kake nufi akan munar gidan da mahaifina ya gina?"
Yace "kema kiji in aka kwacema abinda yake naka ya kakeji."
Tace "ni menene naka dana kwata?"
Tambaya kike?
Tace "badai company dinmu kakeso kace ba?"
Yace "ko ma menene magana ta kare, ke kika bani gidan nan da kanki sai kisan inda dare ya miki."
Tace "zan san inda dare yamin amma 'ya'yanka fa?"
"'Ya'ya? Ki tabbatar kin kwashesu."
Hawayenta dake zubowa ne ya karo, tace "nikam Abakar tunda nake dakai ka taba min so na tsakani da Allah kuwa?"
"So? Wasan yara kika koma yi kuma?"
Mumy ta toshe bakinta saboda kuka na neman cin karfinta, kawai kashe wayar tai ta kalli Sultan tace "wuce kaje gidan Kawu, ni zan koma asibiti."
Yace "wai mumy meke faruwa ne?"
Tace "jeka in na dawo mayi magana."
Shiru yai kamar ya sake magana sai kuma yace "to."
Tana ganin ya fita kawai ta tsuguna tasa kuka, ba kowa a wajen sai ita dan mutanen ma sun tafi, itakam me tayi? Laifin me tayi da rana daya rayuwa ta juya mata haka? Hakkin bayin Allah da kukaitaci.
Kuka ta sake sawa, ta dade tana kuka kafin ta mike ta tafi asibiti.
Safeena na ganinta ta taso tace "Mumy menene?"
Mumy hawaye ne yazubo mata tace "Safeena ya zamuyi?"
Hankalin Safeena ne ya tashi tace "menene?"
Nan mumy ta kwashe komai ta fada mata tana kuka, sam basu san kafin su fara labarin Inna ta farfado ba.
Kuka sosai sukeyi itada Safeena, Safeena tana kuka tana cewa "yanzu Mumy haka Dady ya mana? Kema Mumy kamar baki da wayau kina ganin yanda ya banzatar da abinda ya haifa duk rashin mutuncin mutun ko duk mutuncinsa indai har bai daraja abinda Allah ya bashi ba banaji zuciyarshi a tsarkake take, kina ganin duk abinda za'ama Jalila bai taba sa baki ba, bai kuma taba nuna damuwa ba, tunda kikaga haka ai kema kinsan Dady ba mutumin kwarai bane."
Mumy tana kuka tace "duk laifinane Safeena, Inna tasha nunamin gaskiya amma banaji, yanzu gashinan ai."
Yanda Inna ke yi ne yasa suka juya inda take da sauri, hankalin Mumy ya tashi tace "Safeena kira likita."
Da gudu ta fita, Mumy ta kamo hannunta kawai ta sa kuka.
Inna ta fizge abin hancinta cikin wani irin murya tace "Fatima!"
Mumy ta dago da sauri tana kuka, Inna tace "ki daina kuka, ni nasan tawa tazo karshe, ke nakeji Fatima bansan wace rayuwa zakiyi ba."
Mumy tana kuka tana girgiza kai tana cewa "Inna ki daina fadar haka."
Inna ta girgiza kai cikin tsananin ban tausayi tace " ki duba kasan katifa ta akwai key na safe dina akwai takardun gida dana siya kwanaki can da suka wuce, kisa Sani ya kaiku gidan.
Fatima kiyi hakuri duk nice na cuceki, duk nice na dauraki akan rayuwar da kikeyi, san kaina da sanki yasa bana tunanin komai, Fatima bansan ya zakuyi ba, shares dina basuda yawa sai dai nasan zasu rage muku na cin abinci.
Yanda numfashinta ke kara sama ne yasa hankalin Mumy ya kara tashi, Inna tace "karkima Abakar magana, kar kuma ki nemi kwatar gidan, ki barshi rayuwa ce, gashinan nima na gani dayawa sun gani shima kuma zai gani, sai dai ki taimakeni da abu daya.
Mumy ta kara runtse ido hawaye na kara zubo mata "Jalila! Da Mamanta!"
Idanunta ne suka shiga lumshewa tace "Fatima ki nemarmin yafiyar........."
Yanda ta kara birkicewa ne abu na ta zubowa daga bakinta ne yasa ta kasa magana, Dr ne ta shigo da sauri ta matso kusa da Inna.
Kafin ta yi wani abu har rai yayi halinsa.
Wani irin kuka Mumy ta saka, Safeena ma ta sa kuka abin tausayi.
***********
Abubakar kam yana zaune a dakin hotel din daya kama, idanunsa sunyi jaa in ya tuna abinda aka mai sai yajii zuciyarsa na kara tafasa, Fatima? Sai kaga ya naushi gefen da yake zaune, can ma sai gani nai ya mike a zuciye ya nude window kawai yana kallan waje.
Bai taba tunanin wani abu zai kawo mai cikas ba a wannan lokacin, ihu ya saka tare da cizar lebe.
************
Goggo kam hankalinta ya kwanta dan yanzu kam taje taga yan uwanta data dade tana kewa, sun dan dade suna waya da yayanta wanda ta amshi numbersa sukai ta gaisawa da yan uwa suka mata ban gajiya sannan ta kashe, wai yanzu itace yan uwanta ke nuna mata kauna haka? Lalai duniya juye juye.
***********
Suna shiga mota Sageer yace "Yaya wannan mutumin kansa daya kuwa?"
Hassan yace "kansa daya kawai tsabar greediness ne ke damunsa."
Sageer yai tsaki yace "ji fa abinda ya maka?"
Murmushi yai yace "kar ka damu ba komai, sannan dan Allah mu bar abin nan mu biyu."
Sageer yai dan tsaki sannan ya cigaba da tukinsa.
Suna isa gida ya kalleshi ya mai alamar zip da bakinsa.
Sageer ya bishi da kallo, shikam da sauri ya shiga ciki, Sageer kam juya kan mota yai ya fita dan dama akwai abinda zaiyi.
Hassan na shiga ya wuce kitchen da sauri, ba kowa a ciki, da alama harta kammala yanda yaga har kitchen din ta gama gyarawa, juyowa yai ya wuce sama.
Kallan kanta tai a madubi tace "kai inaa.... bazan iya sa kayan nan da Ameera ta ban ba."
Rigace iya gwiwa, ba dogon wando, tace dama taban wando ne kila dana saka.
Ta juya jikin wardrobe tana neman cirewa ya turo kofar dakin.
Ta manta kayan dake jikinta, gani tai ya taho inda take da sauri, yana karasowa ya rungumeta tsam a jikinsa.
Shiru tai a hankali yace "Baby wannan shigar fa?"
Tunowa tai, ta kasa cewa komai, dagota yai ya kalleta daga sama har kasa, kunya tasa ta juya baya da sauri, kara juyo da ita ya rungumeta yace "saura kadan fa na fadi."
Kallansa tai tace "kai Yaya."
Sumbatarta yai zaiyi magana sai ya fasa yanda yaga ta kura mai ido.
Yace "menene?"
A hankali takai hannunta gefen bakinsa tace "me ya faru?"
Hannunta yadan ture yace "ba wani abun bane ina sauri ne ban kula ba na danji."
Idanunsa ta kalla sai dai ta rasa me yasa bata yarda ba.
Kamar zatai magana sai kuma ta fasa, gani yai idanunta sun fara cicikowa yace "Menene kuma?"
Ta fara kokarin shanye kwallar tace "ba saboda fitar dakai bane wani yama haka? Ko dad......"
Kara jawota yai ya rungume yace "ki bani abinci, yunwa nake ji."
Shiru tai cikin rada yace "mu biyu ne a gidan, na dauka Sageer zai shigo sai naga ya juya, kinga yau sai mu....."
Sai ya kara matsowa kusa da kunneta yace "sai a biyani bashina duka."
Dagowa tai ta kalleshi, kamar zatai magana kuma sai yaga tayi murmushi tace "ka dainajin yunwar ne?"
Cikin shagwaba yace