Showing 87001 words to 90000 words out of 146738 words

Chapter 30 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt

23 Nov 2025

5789

yai yanajin wani abu a kirjinsa kafin yace "Jalila Husain......."
Ya runtse ido a hankali wasu hawaye naga sun zubomai masu zafi, hannunsa yakai kan labanta.
Idanunsa ya sake rufewa a hankali ya shiga matso da kansa ya sumbashi bakinta, bakinsa ya bari a kan labanta.
Idanunta ta bude, me zata gani?
Shima idanu ya bude suka kalli juna, da sauri tasa hannu ta tureshi, ya mike tsaye da sauri.
Tace "Yaya!"
Yace "bargona nakesan dauka sanyi nakeji."
Tace "bargo?"
Bargo a.......
Ta kasa karasawa, yace "bargo a me?"
Tace "bakomai, nagane tun jiya kaki kulani, yanzu kuma gashi kanamin magana."
Yace "yanzun ma bakiji me nace miki ba? Bargona zaki bani."
Tace "to in na baka in shimfida me?"
Ya kalleta taya zaiyi yace mata shi kwanan kasan ne bayaso?
Ya hade fuska yace "sai ki kwanta akan gado ni sam laushin katifa samin ciwon baya take."
Da sauri tace "haba? Da gaske na kwanta?"
Ya kalleta sannan ya dau bargonsa ya kwanta akasa.
Murmushi tai sannan ta hau kan gado tana dariya jin dadi.
Can kuma tace "yaya badai barmin kai ba?"
Yace "barmiki? Bakiji me nace ba?"
Tace "oh naji."
Ta kwanta tare da juya baya.
Shiru tai kamar mai bacci tana tunanin abinda ya faru yanzu, hannunta takai kan labanta ta shafasu, shima kwanciya yai yana tuno abinda ya faru, me yakai shi? Baisan ya akai yaji a lokacin sumbatarta yakesan yi ba.
Ahhh kansa ya shafa yace "Hassan!"
#OneLuv💕


🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*


     *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
  (_D home of expert and perfect writer's_💡)

*50*


   Yana cikin barci wajen karfe uku taji ana wani irin numfashi sama sama, yanzu kam ta riga tasan shine da sauri ta sa hannu ta danna waayarta sannan ta kunna fitilar dakin, yau a rufda ciki ta gashi ya tukunkune daga can gefe hannunsa nakan wuyansa gaba daya zufa ce take keto masa, mikewa tai da sauri tazo kusa dashi.
Hannuntasa ta janye hannunsa daga kan wuyansa, idanunta sun ciciko tana kiran sunansa.

  Amma ina, hannunsa ya fizge daga gunta ya rike kansa dake wani irin sarawa, Jalila ta ga yau abin nasa dayawa dan har pillow ya dauka ya danne kansa dashi.

  Cikin tsoro da tausayinsa yasa ta janyowshi ta rungumeshi ta baya tare da sa kuka tana cewa "Yaya! Yaya dan Allah kandaina......."

  Jitai jikinshi duk yanata ketowa da zufa, sakeshi tai da sauri ta kure karfin AC din dakin sannan ta dawo a rikice ta kara janyoshi tana kuka.

  Yau abin ya dade dan ita kawai data rungumeshi ta kifa kanta a jikinsa bata sake dagowa ba.

  A hankali numfashinsa ya dawo, ya bude idanunsa, ganinshi yai a jikin Jalila tanata kuka.
  Shiru yai cikin takaici abinda ke faruwa wanda gashi duk sanda abin ya tashi sai yasa Jalila kuka haka.

  Mikewa ya fara kukarinyi, idanunta ta bude ta daukeshi a kansa, da sauri tace Yaya?
Zama yai sannan ya jawota kusa dashi, jiki a sanyaye take kallanshi.

  Bata an kara ba taji ya rungumeta tsam, ya kwantar da kansa kan kafadarta.

  Bakinta na rawa tace "Yaya!"
"Let's wait like this for a moment......" cikin wata murya mai sanyi ya fadi hakan, shiru tai ta kasa motsi.

  Can yasa hannu a bayanta kamar me lallashi yace " sai yaushene zaki canza hobby dinki?"

A hankali tace " to ya zanyi duk ka canza lokaci daya, ga....."
Yace "are u worried about me or are u scared?"
Tace "zaka fara ko Yaya?"

  Shiru yai kafin ya saketa ya kalleta yace "irin wannan kure mana AC haka fa?"
Ta tashi ta dau remote tana cewa, zufa kaketayi shiyasa na kunna.

Ya kafeta da ido yace "kin tabbatar dan ni kika kunna?"

Tace " ban gane ba???"
Yace "a'a to haka kawai dan ina zufa sai a kure AC haka?"
Ta kalleshi tace "nikam ko dan ka kwanta a kasa ne?  Naga ka dade lafiya."
Kallanta yai sannan ya girgiza mata kai yace "ko daya."

Ta kalleshi bayan ya mike daga gun tace "Yaya nikam dan Allah meke damunka? Mafarki kakeyi? Ko.......?"
Sai kuma tai shiru, yace "ko aljanu gareni?"

Da sauri tace "ba haka nake nufi na...."

  Ruwa ya dauko yasa sannan ya dawo ya kwanta, kallanta yai da take dukushe a gun yace "Hajiya zan kwanta."

Tace "Hajiya? Lalai Yaya matar da bata taba zuwa hajj ba, batama iya karatu sosai ba itace Hajiya."

  Juyowa yai ya kalleta sosai yace "daki shiga islamiyya ku dinga zuwa da Ameera da kuma ki zauna a gida wanne yafi?"

Tace "in zauna a gida kamar ya?"
Tai tambayar tana kallansa, juyawa yai baice komai ba.

Da sauri ta kalleshi tace "da ka koyamin a gida?"

Idanunsa ya rufe da sauri tare da harde hannayensa, ta sako kanta tace "Yaya dagaske?"

  Bude idanunsa yai, sam baiyi tunanin ganinta daf dashi haka ba, idanunsa ne ya sauka a nata, da sauri ta mike tsaye ta hau kan gado ta kwanta tare da saurin kashe fitilar dake jikin gadon.

  Kwanciya tai tana dan ajiyar zuciya a hankali.

Dakin ne ya baibaye da duhu.
Tana kwance sai dan juye takeyi, can tace "yaya kayi bacci?"

Shiru yai baice komai ba sai dai yana jinta, tadan sake ajiyar zuciya kadan.

  Muryarsa taji yace "baki taba tambayata dan uwana ba, bayan duk wanda yaji sunana Hassan ya tabbatar inada Husain."

Juyowa tai ta kwanta akan tafukan hannayenta ta jiyo ta saitinshi, duk da duhu ya sa bata ganinshi tace "taya zan tambayeka abinda ka kasa fadama kowa?"

  Shiru yai dan harta dauka bazaice komai ba sai taji yace " shekararsa 10 kenan da rasuwa."

Zatai magana taji yace "tare suka rasu da dan kanin Abba, Sudais wanda yazo gidannan karatu."

  Jalila yanzuma hartace "sh........"
Ya kara katseta yace "karkice komai kijini kawai."

Shiru tai tana kallangun da yake.
Yace " karki kunna fitila."

Tai shiru, tare da kallansa, Hassan yana kwance yace "they died because of me......"

Ya fada tare da runtse idanunsa da karfi yana jin wani abu na tokare mai zuciya.

Wasu zafaffan hawaye ne suka zubomai, yace "He is a bright person, mutum ne mai tsananin hakuri, a koda yaushe cikin fara'a yake Jalila..........."

  Nauyin da zuciyarsa taci gaba dayi, ga numfashinsa na seizing ne yasa yai shiru, saukowa tai da sauri har tana buge kafa ta matso kusa dashi.

Tace "yaya!"
Ta dauka abin ne ya tashi.
Jinta a kusa dashi ne yasa yasa hannunsa dan jin a inda take, a durkushe a kusa dashi ya jita.

  Hannunta ya riko sannan ya kwantar da kansa akan kafafunta dake a durkushe.
Da sauri ta kalleshi.
Hannunta ya riko.

Kallansa tai zuciyarta na bugawa da sauri, a hankali tace "karka cigaba yaya inhar zuciyarka bazata iya dauka ba, sannan bansan menene yafaru tsakaninku ba amma na tabbatar ba............"
Yanzu ma katseta ya sakeyi, yace "don't comfort me."
Shiru tai, yace " nikaina bansan meyasa nakesan fadamiki abinda ban fadama kowa a duniya ba, sai dai ina alakanta hakan da zaman da nai dake sannan da yanda nasan komai naki."

A hankali ya lumshe ido zuciyarsa na kunna, yace "later....."
Kai ta daga tace " later Yaya.... sanda kaji zaka iya."

Kansa ya kara gyarawa, shiru tai sai jikinta dayai sanyi, zuciyarta na bugawa da sauri.

Ya dade a haka kusan minti ashirin kafin yaji an fara kiraye kirayen sallah, ita ta dauka ma bacci ne ya daukeshi, ga kafarta ta fara zafi.

A hankali ya dagata sannan ya mike ya kunna wutar dakin.

Haske ne ya baibaiye dakin, kallan juna sukai, ya dauke kai ya shiga toilet.

Yana shiga ya kalli kansa a madubi, yanzu kam ya tabbatar ya fara san yarinyar nan, garin yaya? How can i??? Ya furzar da wata iska.

A inda ya barta anan ya ganta, ya kalleta yace "me kike anan?"
Da sauri ta mike ta fara ninke bargo tace "bakomai."

Kallan fuskarsa tai, tanaso taga canji a tattare dashi, kallanta yai yace "kallan fa namenene?"

Ta mike rike da bargo tace "bakomai, ba kai na kalla ba."
Yace "then?"
"Uhmm yauwa toilet na kalla."

Sallaya ya shimfida batare da ya kalleta ba, ta mike da sauri ta shiga toilet.

Tana rufe kofar tai ajiyar zuciya tace "meke damun yaya? Ya tone din maganarsa ta koma ta da?"

Shima tana shiga toilet ya kalli kofar toilet din sannan yai ajiyar zuciya shima, ya tadda sallah.

Pad ta canza ta fito, yana sallah ta fito, zama tai a bakin gado tana dan lekashi.

Yana idar da sallah ya bude qur'ani, jitai yace "taso."
Da sauri ta taso tace "gani."
Ya kalleta sannan ya kalli kasa, da sauri ta zauna a kasan carpet, tana kallansa.
Ya kalleta fuska a hade yace a ina kika tsaya?
Tace can karshe, ta fada tana neman taba qur'anin, da sauri ya rike hannunta sannan ya kalleta, itama kallansa tai dan batasan me tai ba.

Yanda yaga tana kallansa ya fahimci batasan ma metai ba, yace "ba asan taba qur'ani izu sittin in mutum na fashin sallah."
Kunya ce ta kamata, ta kalleshi.

Sake mata hannnu yai sannan yace can kasa ina?
Tace "a ikira."

Kallan mamaki ya mata kamar zaiyi magana sai ya fasa.

Nan ya bude ya yafa biyawa, tana zaune a gefe tana biyawa.
Sura daya sukai yace "sai gobe kuma."

Kallansa tai tace "nagode Yaya."
Bai amsa mata ba ya fara karatunsa, mikewa tai ta zauna akan gado, can dai ta fito falo ta kwanta sai bacci.

Hassan kam ya dade yana karatu kafin ya kwanta akan sallayar, bacci yai gaba dashi.



************

Inna ta kalli Mumy wacce ta kirata tace " Abakar ya tafi gun aiki?"

Tace "eh."
Inna ta kalleta tace "haryanzu fishin kikeyi dan nace mijinki yace shine yai komai?"

Ta kalleta tace "Inna dan Allah Abakar yaci darajar jikokinki."
Tace "kamar ya?"
Mumy ta kalleta tace " ki barmai company din nan dan Allah, karfa ki manta yanda yake kokari ganin komai ya tafi daidai, sannan mijinki yarka ne fa? Sai yaushe ne zaki maidashi d'a?"

Inna ta kalleta tai murmushi tace "a koda yaushe in kina abu mamaki yake bani, ke wai sai yaushene zaki fahimci wanene Abakar? Sai yaushe ne zaki gane ba saboda ke yake zaune agidan nan ba, ba saboda ke yakemin ladabi ba?"

Cikin takaici tace "ko ma saboda me yake tare da ni bai dameni ba, tunda ni haryanzu ina sanshi kuma banasan 'ya'yana su rabu da mahaifinsu."

Inna tai shiru tana kallanta, wannan fa bazata fahimci komai ba, tace " to naji, sai ki shirya muje gidan mu basu hakuri, in kuma ni kadai zanje ba laifi bane."

Da sauri ta kalleta tace "da gaske?"
Tace "eh, sannan ki bar maganar bashi company din zuwa wani lokacin, in komai ya daidaita zan nadashi a matsayin shugaba ni kuma nai resigning."

Da sauri mumy ta taso tazo ta rungume inna tace "godiya nake Inna ta."

Inna ta kalleta kawai, cikin murna ta fita.
Inna ta bita da kallo tace "i know she is naive but I don't expect her to be foolish, ta bari yaranan duk ya gama lalatata da dadin baki."

Tai kwafa sannan tace "bari na gama tallafo company din, in na ma da Taura zan dawo kanshi.


*********

Ummy ce ta kalli wayar hannunta wacce aketa kira tana rejecting, Sageer wanda kecin abinci yace "Ummy wai waye yaketa kira haka?"

Ta kalleshi kawai tai murmushi dan batasan me zata ce ba, Zaliha ce, sam bama ta gajiya da kiran wayar.

Ummy ta kalleshi tace "ya maganar takardun naka?"

Yace " gamunan dai muna jira basu bamu ba."

Haka suka gama yin break, ta kalli hanyar sama tacema Sageer yau da alama bacci mai nauyi sukeyi naga shiru.

Sageer ya kalli saman shima sannan yai yake yace "da alama kam, sai dai Allah yasa ba ciwon yaya bane ya tashi."

Da sauri ta kalli Sageer tace "kasan Sageer tsabar naga Hassan yanata canzawa sam ina mantawa?"
Da sauri ta nufi hanyar sama.

Jalila bata dade da tashi ba ta kalli agoggo da sauri ta mike cikin mamakin baccin da tai, a hankali ta tura kofar dakin, Hassan na kwance akan sallaya yanata bacci ta wuce toilet.

Wanka tai ta fito a hankalita zura riga da skirt ma atamfa,tana shafa hoda taji knocking.
Da sauri ta kalli Hassan sannan ta taho gun kofar.

A hankali ta bude, Ummy ta gani, Ummy ta kalleta tace "Hassan fa?"

Tace bacci yakeyi.

Ummy tai ajiyar zuciya sannan tadan ja baya, Jalila ta fito ta kalli Ummy sannan ta gaisheta.

Ummy ta kalleta tana murmushi tace "sry Jalila wlh na dauka ko matsalar Hassan ne ya tashi."
Jalila tace "a'a Ummy bacci ne ya daukeni wlh banmasan lokaci yayi haka ba."

Ummy tai murmushi sannan tace "hakan yayi ai ki fito ki dauko muku breakfast."
Tace to, Ummy ta juya, komawa cikintai ta fesa turare dannan ta yafa dankwalinta ta sauko.

Tana fita daga dakin ya bude idanunsa sannan ya maidasu.
Sai dayai sama da minti biyar sannan ya mike ya shiga toilet.
Meyasa batacema Ummy komai ba?

Har ya zauna sai kuma ya fito dan yanasan jin ya ake ciki akan maganar yar iskar yarinyar nan.

Bakowa a falon sanda ta sauko, Ummy ta jiyo a kitchen da sauri ta karasa ciki.
Ba ita ta gani ba, ashe Sageer ne yake dauraye kwanukan da yaci abinci.

Ta gaisheshi sannan ta karasa kusa dagun kadan tace "da ka barshi zan wanke."
Ya kalleta ba tare da ya sake aikin ba yace "yaya fa? Jikin nashi ne?"
Kai ta girgiza mai tace "ba shibane bacci ne kawai ya daukeni."

Yai ajiyar zuciya sannan ya cigaba da wankewa, ta sake cewa "dan Allah ka barshi nayi."

Muryar Umny taji tace "barshi Jalila indai Sageer ne."

Jalila ta fito Ummy na cewa "matar Sageer ta huta dan akwaishi dasan yin aikin girki da wanke wanke, kinsan da har shara yake tayani."

Jalila ta kalli inda yake tai yake tace "lalai akwai kokari."
Ummy ta kalleta tace "Jalila bakida wata kawa ne ki hadasu?"

Da sauri ta kalleta, Sageer ne ya fito hannunsa rike da plate yace "Ummy!"
Kallansa tai tace "menene? Da kacemin da wacce kakeso yanzu kuma naji shiru, kaga kwara ni na mike tsaye."

Tai maganar cikin zolaya, Jalila ta kalleshi.

Ummy tasa dariya tace "meye hakan?"
Hannunsa ya kalla ya ganshi rike da plate, dariya shima yasa yace "Ummy ai duk kece."

Jalila ce ta kalleshi itama tai dariya, Hassan wanda yake saukowa daga kan steps ya tsaya yana kallansu cikin jin dadi, Ummy ce ta fara hangoshi.
Tace "malam Hassan ina zaka bakai breakfast ba?"

Ya karaso kusa da ita yace "ba fita zanyi ba."
Sageer ne ya kalleshi yace "Yaya."
Kallansa yai yace " mikakeyi da plate?"

Yai dariya yace "Ummy ce take neman tadamin hankali."
Ya kalli Ummy, dariya tai sannan tace Wani abun kake so?"

Jalila ta kalleshi, gani tai ko kallanta baiyi ba, a hankali ta mike ta shiga kitchen.
Sageer ya biyota, wanke wanken ya karasa ya dauraye hannayensa ya fito, har yaje kusa da kofa sai ya juyo kamar zaiyi magana sai kuma ya fita.

Da kallo ta bishi sannan ta fara hada kayan abincinsu.

A falo kuwa Hassan ne ya kalli Ummy yace "ya maganar yarinyar nan?"
Tace "dazuma tayita kira ina rejecting."
Yace "sim dinshi na gunki ne?"
Tace "eh."
Yace "in har bata daina kira ba zuwa dare kimin magana, ni zan mata magana, in ta kama ma sai inje har gidansu naci mutuncinta."

Ummy tai dariya tace "Ba sai ankai ga haka bama, insha Alla, Allah na tare damu."

  Jalila ce ta fito rike da tire.
Ummy ta kalleta tace "Jalila! Goggo tace ya kamata a saki a islamiya, shine nace zan fadama." Takarass maganar tana kallan Hassan.
Itama Jalila shi ta kalla, hartace "Ummy ai......"

Hassan ne yai saurin cewa "karki damu da wannan Ummy, zansan yanda za'ai."

Jalila ta kalleshi jiki a sanyaye tai sama.
Ummy ta kalleshi tace "kai Hassan! Wannan magana kamar ranka na bace?"
Ya kalleta yace " haka kika gani?"
Tace "bani kadai ba har ita Jalilan, kalleta ka gani mana.

Juyawa yai ya kalleta, jiki a sanyaye take taka matattakalar.

Shiru yai tare da kura mata ido.
Ummy ta kalleshi sannan tace " kaje kuyi breakfast."
Ta fada tare da mikewa.

A hankali ya mike shima ya nufi saman, taje bude kofar, ya sa hannu ya bude mata.
Juyowa tai ta zuba mai ido.....
Shima kallanta yake.......


#OneLove💕

🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)

*51*

Kallanta yai yace "bazaki shiga ba?"
Juyawa tai ta shiga dakin, ta ajiye tiren sannan ta kalleshi tace "Yaya abinci."

Bai kalleta ba yace "sai nayi wanka."
Ya fada tare da nufa ciki,, da kallo ta bishi tana mamakin halayensa.

Harta bude zata zuba sai kuma ta maida murfin kular ta rufe.

Hannu tasa ta janyo littafin da yake karantawa ta dauko, ta bude cikin littafin.
Ajiye littafintai sannan ta kalli hanyar toilet, ta mike ta fito falo.
Tv ta kunna tai shiru tana tunanin abinda ya faru tsakaninsu a daren jiya.

Kalamansa na kara dawo mata, meya faru a can baya? Wanda yake hanashi bacci? Yake hanashi shiga mutane? Yake hanashi murmushi? Yake hanashi zama cikin yan uwansa?

  Shiru tai tana tunani, da alama shima yanada painful past wanda yafi nata.

  Yana fitowa daga wanka ya shirya, ganin bata dakin ga motsin karar TV a falon yasa yasan tana can, sai dai bazai iya kiranta ba.

Zama yai akan kujera yana kallan kofa yana jiran shigowarta, dan yunwa yakeji.

Jalila kuwa ta shiga tunani sai can ta dawo daga tunanin nata, ta mike ta bude kofar, a zaune taganshi tana shiga suna hada ido, yana kallanta yai saurin dauke kai.
Ta shigo ciki tace "Yaya ka fito shine ba magana?"
Bai kalleta ba yace "inyi magana ince me?"

Ta kalleshi tace "kacemin ka fito in taso."
Ya kalleta yace "gashinan ai ban kiraki ba kin taso."

Tace "lalai yaya, to bari nakoma sai ka kirani." Tai maganar cikin zolaya.
Yace "nidai kafin ki koma bani abinci naci inyaso sai ki koma."
Ta kalleshi tadan canza fuska tace "ba kara ma kenan? Bari na fadama Ummy to nace kace ba sai naci abinci ba."

  Baisan sanda ya dan murmusa ba yace "yaushe kika koma haka?"

Matsowa tai tace "yaya wlh yanzu bakinka ya motsa,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login