Showing 90001 words to 93000 words out of 146738 words
Chapter 31 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt
wallahi yau na gani sosai."
Tsuke fuska yai yace "yau menene ruwanku da dariyata?"
Tace "ni kuwa nake da ruwa yaya, bakasan yanda abin ke damuna ba, kome fa zakace fuskarnan a tsuke kake fada."
Kallanta yai yace "bakyaso?"
Ta daga kai da sauri tace "sosai ma, wani sa'in in tone din maganarka ya koma cold sai jikina yai sanyi."
Kalaman Ummy ya tuno data fadamai dazu, kallanta yai yace "magana zaki tsaya yi bazakiban abinci ba?"
Ta dan turo baki ta nufi inda ta ajiye abincin, a ranta tana cewa what am I expecting?
Zubamai tai tace "ka sauko."
Yace "yanzun ma kin manta da plate din ne? Dan muci tare?"
Cikin shagwaba tace "yaya Allah fa ba haka bane."
Yace "shagwaba kika koma?"
Ta kalleshi tace "yaya wai meyasa kakemin haka?"
"Menai?"
Ta kalleshi kamar zatai magana sai kuma tai shiru, a ranta tace "rannan kamin kiss bance komai ba, jiya ka kwanta a cinyata bance komai ba amma kai komai nai sai ka fassara."
Mikewa taga yayi ya wuceta ya zauna a inda ta zubamai abincin.
Kallanta yai tana tsaye hannu yasa ya jawota, ta zauna a kusa dashi.
Kallansa tai tana mamaki tace "Yaya!"
Yace "wai ni yaushe nake yayanki ne? Kin kama suna kin rike kamar ke kika samin?"
Baki tadan turo sannan ta zuba abinci a nata plate din, gani tai yasa spoon dinshi cikin plate dinta.
Da sauri ta kalleshi yace "ba haka kikeso ba?"
Tace " bangane ba....?
Bai kara mata magana ba yacigaba da ci, kallansa ta tsaya yi tama kasa ci, sai can ya kalleta yace "kin koshi ne?"
Spoon din ta maida ciki ta cigaba daci ta mamakin wannan abu.
Yana gamawa ya dau key ya bar dakin baice mata komai ba, baki ta saki tana kallan ikon Allah.
Saukowa yai kasa ba kowa a falon, yai hanyar waje.
Mota ya shiga kawai ya fita, Jalila ta dade a zaune kafin ta kwaso kwanuka ta fito.
Ganin bakowa a falon ta wuce kitchen ta wanke kwanukan, tasan Ameera na skul, da alama Ummy na daki.
Sageer fa? Bude kofar daki taji da sauri ta kalli gun.
Sageer ne ya fito sanye da kaya da hula da alama fita zaiyi.
Kallanshi tai shima ya kalleta, da sauri ta dauke kai ta juya zata koma kitchen.
Yace "Jalila?"
Tsayawa tai a inda take sannan ta juyo ta kalleshi.
Ya matso inda take kadan ya kalleta yace "ina making dinki uncomfortable ko?"
Kallansa tai ta girgiza kai alamar a'a sannan tace "a'a
Yai murmushi yace "kiyi hakuri Jalila."
Tace "Uncle sai yaushe ne zaka daina bani hakuri? Bazance ban taba jin zafin abinda ya faru ba, dan da naji zafinka sosai sai dai a yanzu ko kadan banajin zafin ka, na fahimceka, nasan dalilinka."
Kallanta yai yace "nagode Jalila, nagode da fahimtar da kikamin."
Ta kalleshi tace "Ummy tace duk ka canza, ni kaina nasan ba haka kake ba, Allah yasa banice sillar canzawarka ba."
Ido ya kura mata kafin yace "ko kadan Jalila, inma akwai dalili to bazai wuce zuciyata ba wanda kuma basai kin damu da ita ba, zata daina da kanta."
Kallansa tai tace "Uncle!"
Yace "kidinga cemin Sageer kawai, hakan shine daidai a matsayinki na matar yayana."
Shiru tai kafin tace "saidai na kiraka da Yaya sageer yanda Ameera ke cewa."
Yace "hakan yayi, nagode Jalila sannan Please let us take it to our grave, kar kowa yasan abinda ya faru."
Zatai magana sukaji muryar Ummy tana cewa "Sageer fita zakai?"
Da sauri ya juya dan baiji karar kofa ba, Jalila ma ta kalleta.
Ummy ta kalleshi tace "menene?"
Yace ba komai, na fito ne banganki ba nake tambayar matar Yaya.
Tace "ina ciki ina addu'oi.
Yace "Ummy zanje gun Abban."
Tace "to Allah ya bada sa'a."
Yace "Ameen ya fita."
Ummy ta kalli Jalila tace "Jalila!"
Jalila ta matso tana cewa " Ummy nikam banga Ameera ba."
Ummy tace "sun koma skul yau dama hutu ya kare."
Tace "oh shiyasa, naji gidan shiru."
Ummy tai dariya tace "wlh kuwa, Jalila gidan namu is so boring."
Jalila tai dariya itama tace "muma haka gidan yake, Sultan kullum yana daki yana game ko jin kida, Safeena kuma tana gun Mumy ko suna kallo ita da Yasmeen, Inna na sama, Mumy kuma itama ko tana falo ko daki, dama gun Goggo nane muke zama muyi ta hirarmu."
Ummy tace "sanda kowa yake zama, bacci da kallo ke me kikeyi?"
Tace "aiki, girki, ko wanki."
Ummy tace "hmm da alama ya kamata ki kara samun hutu a gidan nan, yanda kikai aiki acan ba hutu yanzu duk sai ki fanshe hutunki gun mijinki."
Jalila tai dariya tace "ai nan gidan ba aiki Ummy."
Tace "ba wani nan, ina mijin naki?"
Cikin kunya ta girgiza kai.
Ummy tai ajiyar zuciya tace "Haryanzu baice miki zai fita?"
Tace "eh, yanzu ma fa....."
Sai kuma tai shiru tare da sa dariya.
Ummy ma tai dariya tace "Jalila bansan ke ba amma i am sure Hassan na sanki, idanunsa kadai sun tabbatar da hakan."
Jalila ta kalleta sai dai batace komai ba.
Ummy ta dafata tace "Jalila godiya, kina sani farincikin dana dade bansamu ba, ganin Hassan na samun sauki yasa kullum zuciyata nakejinta tass, shikansa mahaifinshi yanzu hankalinsa yafi kwanciya har yake fita aiki ya dade haka."
Jalila ta sunkuyar da kai a ranta tace me nayi? Ummy tace "mungode Jalila, sai dai ki kara hakuri sannan ki kara kula dashi, insha Allahu bazaki tabba dana sanin auran Hassan ba."
Dagowa tai ta kalli Ummy sannan ta daga kai alamar to.
Hassan na fita yaje bakin wani shago yai parkin, fita yai ya shiga ciki.
Mai shagon ya tambayeshi abinda yakeso, Hassan yai shiru kafin yace "kawai abashi abunda ya dace."
Cikin mamaki mai shagon yace "abinda ya dace kamar me kenan?"
Gidan mamar matata zankai, ya fada tare da dauke kai.
Mai shagon ya guntse dariyarsa sannan yace "katan din juice fa?"
Hassan yace dame?
Yace sai ka hada ko da kayan tea ne.
Hassan yace "samin to."
Nan mai shagon ya laftamai kayan tea dan kana kallan motarsa kasan da akwai kudi, ya sa mai juice kala uku a bayan boot ya cafki kudinsa.
Hassan na fita yace "Alhamdulila Allah ya kara kawoka."
Hassan ya shiga mota yai gidan Goggo.
Ya dade a waje yana tunanin abinda zaice kafin ya shiga.
Almajirai yasa suka shiga da kayan.
Goggo na zaune tana jin radio ana hada musu wuta a waje ya shiga ciki.
Tanaganinsa ta mike fuska dauke da fara'a tana lale lale.
Ya zauna ya gaisheta ta amsa cikin farinciki, shidai yai shiru.
Kowa ta tambayeshi sai dai yace "lafiya."
Data gama tambayar tai shiru shima yai shiru.
Can yace "ba wuta ne? Naga kamar da wuta a layin?"
Tace "gyarawa sukeyi yanzu, Hassan mungode sosai sosai, Allah yayi albarka ya inganta rayuwa."
Yace Ameen
Shiru suka karayi kafin ya mike yace zai tafi.
Tace "da wuri haka?"
Yace "eh."
Tace "to mungode."
Tana fitowa waje tai karo da kayayaki, nan ta kara mai godiya har ya fita.
Mota ya shiga yai ajiyar zuciya, sannan ya tada kota ya juyo gida.
Jalila kuwa bayan ta gama komai a kasa, ta daura abincin ran.
Yana shiga yaji motsi a kitchen, lekawa kitchen din yai, hangota yai tana aiki, yanka vegetables takeyi, tsayawa yai daga inda yake ya kura mata ido, gaba daya yanayin fuskarsa ya canza.
Ya dade yana kallanta har itama jikinta ya bata ta juyo.
Ganinsa tai a tsaye da alama ya tafi tunani, ta matso tace "Yayah!"
Kallanta yai yaganta a gabansa, tace "yaya naga kana......"
Da sauri ya wayance yace "kallan yanda kike aiki nakeyi, kin tabbatar kin wankesu kafin ki fara yankawa dai ko? Dan naga kamar baki wanke ba."
Cikin mamaki ta kalleshi, juyawa yai ya fita, da kallonta bishi,, yanzu kam ranta ya sosu, me yake nufi?
Haka ta cigaba da aikin ta ranta a bace, dan bakin cikin har kwalla ce tadan zubo mata.
Shikuwa yana hawa sama ya bude drawer ya dauko hoton Husain yana kallo, a fili cikin wata murya yace "Husain ya zanyi? Nasan bai kamata ba, bai kamata nai sha'awar rayuwa ta jin dadi da wata ba, ban cancanci yin farinciki ba, ban cancanci a soni ko inso wani ba sai dai bansan meke damuna ba, Husain i am really hurting her, wanda nakeji kamar na fita jin zafin abinda nake aikata mata."
"Zuciyata na kwadaitamin yin rayuwa da ita, zuciyata na san ta kyautata mata, inasan ingana cikin farinciki, Husain inajina kamar bani ba."
Yai shiru tare da rutse idanunsa, ya koma ya jingina da jikin drawer din, a ransa yace "Husain zan sanar da ita komai, dan abinda zuciyata ke rayamin kenan, in har na sanar da ita zan barta tai deciding abinda taga ya dace, inhar tana tunanin rabuwa dani shine mafita shikenan, in kuma....."
Sai yai shiru, tare da kara runtse idanunsa,shiru yai ya dora hannunsa akan goshinsa yana tunanin abinda ya faru a baya.
Baisan hawaye sun zubo mai ba.
**********
Mumy ce ta kalli Dady bayan ta amshi hular dake kansa tace "Dadyn Yasmeen! Inna ta yarda."
Yace "dame?"
Tace "bazata daurama laifin abinda ya faru ba."
Yace " meyasa kike takurama kanki? Nacemiki bakomai, zan iya yin komai indai a kanku ne."
Ta ajiye hular ta rungumeshi tace " karka damu, na fadama it's my turn to protect you"
Kallanta ya shafa sannan yace " nine ya kamata nai protecting dinki ke da yarana."
A tare sukai murmushi......
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
Thanks alot for the love 😍May Allah Subhanahu Watta'ala always help and guide us👏🏻
*52*
Yanajin motsin shigowarta ya mike ya maida hoton sannan ya fito daga dakin, da kallo ta bishi tace "yaya!"
Ko kallanta baiyi ba bare tasa ran zai amsa mata, saukowa kasa yai ya zauna a garden.
Ita kuwa ganin yanda ya giftata ko kallanta baiyi ba tace "me kuma nai? Ni Habiba?"
Abba ne ya dawo, yana sauka daga cikin mota ya hango kan Hassan, gunsa ya nufa.
Jin motsin tahowar mutum yasa Hassan juyowa.
Ganin Abba ne yasa ya juya yana kara tunani, Abba ya karaso ya zauna daf dashi.
A hankali yace "sannu da zuwa."
Abba yai murmushi yace "Eldest me kake tunani? Naga ka dade banganka anan ba."
Hassan yai shiru sai dai ya kalli Abba.
Abba ya sa hannu a kafadarsa kamar abokinsa yace "Mata ne?"
Da sauri ya kalleshi.
Abba yai murmushi yace " na canka kenan."
Yai saurin cewa "a'a ko kadan."
Abba yai dariya sannan ya sauke hannunsa daga kafadar Hassan, yadan yi shiru.
Hassan bai kalleshi ba yace "ina yarinyar? Ka daina tunaninta?"
Abba shima yana kallan kasa yadan hade hannayensa gu daya yadan matsa, yace " ba kamar da ba."
Hassan ya dan kalleshi yace "kana tunanin santa kake?"
Abba yace "yanzu gaskiya kakeso na fadama ko kuma abinda nasan zai kwanta maka?"
Hassan yace "gaskiya!"
Abba yadanyi murmushi kadan yace " inayi sosai, sai dai kamar yanda mahaifiyarka tace zanyi kokari ganin na cireta a raina, dan ina ji a jikina ni kaina ba san daya kamata nake mata ba."
Hassan yai shiru kafin ya jinjina kai yace " nagode Abba da kake kokarin cire ta aranta dukda abin ba mai sauki bane."
Abba ya riko hannunsa yace "kasan yanda hankalina ya tashi? Lokacin da naga kana fada akan abin? Nayi tir da zuciyata nayi dana sani wanda bazan iya misaltamaka ba."
Hassan ya kalleshi sannan yace "bansan nima sanda na hau haka bane....."
Abba ya kalleshi yace "naji dadi a kasan raina, at least inada wanda nasan zai hanani, kaga kamar Sageer na tabbatar bazai dage akan abinda nakeso ba, balle Amira, kai kuma ba lafiya ce dakai ba, balle ka hanani abinda zuciyata ke neman jefani, sai dai bansan har jikinka yayi sauki haka ba ina can ina shirme."
Ya karasa maganar jiki a sanyaye.
Hassan yai shiru kafin yace "Abba a koda yaushe ka dinga tuna wacece Ummy a garemu, in har wannan tunanin na zuwa maka na tabbatar ba abinda zai gifta zuciyarka."
Kai ya jinjina yace "ni kaina bansan ya akai zuciyata ta nemi kawomin shirme haka ba, bayan nasan irin kaunar da kakema Mahaifiyarka, bayan kai din kaine rayuwata."
Hassan ya kalleshi cikin wani yanayi na tausayawa.
Can ya dauke kansa da sauri saboda kwallar dake neman taruwarmai a ido, ya juya kansa da sauri.
Abba ya sake dafa kafadarsa yace "ya ya? Fada kukai da matar taka shine kai yaji?"
Hassan ya kalleshi sannan ya dan murmusa kadan.
Cikin tsananin mamaki Abba yace "Hassan murmushi kai?"
Yace "wa? Ni?"
Abba yace "sosai ma kuwa, na tabbatar kayi murmushi yanzun nan.
Hassan ya mike da sauri, Abba ya jawoshi ya zauna ya riko hannunsa yace "nagode Hassan."
Hassan ya kalleshi yace "name?"
Yace "na komai ma, kai d'a na ne wanda na haifa sai dai ban taba alfahari da komai a rayuwa ba kamar ka."
Jiki a sanyaye yake kallansa kafin yace "bancancanci samun wannan matsayin ba."
Abba ya dan harareshi yace " in tuno ma?"
Da sauri Hassan ya mike dan ya fahimci abinda yake nufi yai hanyar ciki, Abba na cewa "in ban tuno ma ba na tunawa matarka."
Da sauri ya shiga ciki, Abba ya bishi da kallo cikin tausayawa, har idanunsa suka dan canza, ya juyo tare da dan runtse ido yace "Alhamdulila!"
Tana kasa taga hawansa sama, da kallo ta bishi, shigewa yai.
Bata hau sama ba sai bayan magrib, dan sunatare da Ameera da Ummy bayan ta dawo daga makaranta, bayan magrib din ma Ummy ce tacemata dare yayi.
Ameera tai dariya tace "kai Ummy ba kara?"
Ummy tasa hannu tadan kwadeta tace "zaki fara ko?"
Mikewa tai ta hau sama, Ummy ma ta mike tace "ke kuma sai kiyi ta zaman gulma.
Ameera tace "bari na jira Ya Sageer ya dawo muyi hira, tunda dai ni kowa ya watse ya barni."
Ummy tai tafiyarta tana cewa "bari ma na kirashi naji naga ya dade bai dawo ba."
Jalila tana hawa sama ta ganshi a kwance, yau ba karatu yake ba sai dai a kwance kawai yake shiru, ta shiga da salama.
A hankali ya amsa wanda ita kanta bataji ba, shiga ciki tai tana kallansa.
Yaci abinci, a ranta tace yau ba jira?amma rannan harda jin haushinsa.
Hartana neman zama a kan kujera sai ta juyo ta fito falo ta zauna, ta kunna Tv.
Shiru tai tana tunani, meke damunshi? Ko bashida lafiya ne?
Da sauri ta mike ta shiga dakin, tazo jikin gado tace " Yaya? Bakajin dadi ne?"
Kai kawai ya girgiza mata alamar a'a idanunsa a rufe.
Tai shiru kafin ta juya, har zata fita sai kuka ta shiga toilet.
Tana rufo kofar ya mike, ya kalli kofar toilet din.
Mikewa tsaye yai ya dau makullin mota ya dau wayarsa.
Tana fitowa ya kalleta ya mika mata hijab dinta, kallansa tai tace "me?"
Gani tai yayi gaba, da kallo ta bishi tace "yau maganar ma wahala take?"
Fitowa tai dan ta fahimci ta biyoshi yake nufi.
Haka ya fita, tana kokarin fita Ameera ta fito jitai tace "Amarya sai ina?"
Harararta tai tace "inda kika aikeni, kicema Ummy zamu fita."
Da gudu Ameera ta taho tace "ina zaku? A daren nan?"
Jalila ta in fada miki?
Tace eh ina? Ta fada tana matso da kunne Jalila tai dariya tace "inda Ameera ta aikemu."
Tai saurin yin waje tana dariya, dan tana tsoron karta dade a tsaye tai laifi.
Yana cikin mota harya tada ta bude gefensa zata shiga yace " shiga baya."
Komawa tai baya ta shiga tana yan kunkune, tana rufe mota yaja suka fita.
Suna fita motar Sageer na shiga gidan.
Tafiya yake, ba mai magana a cikin motar, ita kuma haushin ce mata dayai ta shiga baya yasa batai magana ba.
Kanta ta sunkuyar, jin alamun an tsaya yasa ta dago.
Gidan Goggo? Kallan gidan tai sannan ta kalleshi cikin mamaki.
Kashe motar yai sannan ya kwantar da kansa jikin kujera.
Jalila cikin mamaki tace "gidan Goggo?"
Shiru yai har tana tunanin bazaiyi magana ba, cikin wata murya taji yace.
" Jalila?"
A tsorace tace "naam."
Shiru ya sakeyi na wasu lokuta kafin yace " Zan fadamiki abinda ke damuna, abinda na aikata wanda a koda yaushe dana saninsa shike hanani sukuni, a duk sanda na tuno da abin ko cikin bacci ne nakan ji kamar nima na mutu, nakanji gaba daya duniyar ta zamarmin bakinkirin, nakanji komai na cikin duniyarnan ba abinda yake birgeni, zan sanar dake a gaban gidan mahaifiyarki idan harkinga bazaki iya zama dani ba, sai ki bude kofar ki shiga gida gun mahaifiyarki, in kuma har........."
Sai yai shiru, dan bayasan yasa ransa akan abinda bazai samu ba.
Shiru ne ya kara ratsa cikin motar, ita kam Jalila tayi tsuru tsuru.
" Abdullah Taura shine mahaifina, tunda ya tafi karatu kasar Egypt suka rikeshi ya fara musu aiki a can, gaba daya mutum ne mai tsananin san aiki, hakan yasa ba ruwansa da mace balle aure.
Ganin yanda bashida niyyar yin aure yasa mahaifinsa ya masa kamun mata, wacce take 'yace ta abokinsa.
Amininsa ne tare suka taso, yanada 'ya'ya dayawa sai dai duk maza ne su uku ne mata.
Babbar yarinyar Uwargidan ce, su kuma biyun matarsa ta tsakiya ce ta haifesu, dan matansa uku.
Babbar tanada mijinta sai aka bashi ta tsakinyar mai suna Hauwa'u suna kiranta da Jidda.
Daga can aka sashi ya dawo, yana zuwa ya ganta ya aminta da ita akai aure a sati biyu da zuwansa dan dama sun shirya komai, anayi ya dau matarsa suka koma garin Egypt.
Bazaka taba tunanin auran hadi ne tsakaninsu ba dan suna kula da kaunar juna.
Basu dade da aureba Allah ya bata ciki.
Irin girman cikin yasa hankalin Taura ya tashi, ba shiri ya ajiye takarda akan yana bukatar hutu mai yawa suka taho.
Gidansu ya kaita dan hankalinsa da nata sai yafi kwanciya.
A lokacin da suka iso dama ana ta fama da bikin kanwarta, ganin yanda Yayarta ke shan wahala yasa sam hankalinta ya tashi, tana kuka muraran aka kaita gidan miji, haka aka gama biki lafiya ta tare, aka dukufa da mata rubutu da kula da ita, saboda cikin yasata ta kumbura sosai.
Taura a koda yaushe yana gidan, kai abin makulashe, magani da duba jikinta, har Allah ya kawo lokaci.
Satinta daya tana nakuda wanda ya kara wahalar da ita, aka dauketa aka kaita asibiti aka bata gado.
A wata