Showing 69001 words to 72000 words out of 146738 words

Chapter 24 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt

23 Nov 2025

5783

badai wani abun ya sake faruwa ba?” Itadai Inna batace komai ba, har suka isa kasa.

Dady na kasan beni da alama jiransu yakeyi, Inna na saukowa yace “Inna.”

Kallansa tai tace “badai jiyan kwafsawa kai ba?”
Dady yace “kwafsawa kamar ya?”

Haushi ya kamata tace “ wuce muje, koma menene let’s hear it together.”

Nan sukai falo? Hassan na zaune akan kujera suka shigo su uku.
Kowa ya samu guri ya zauna, Hassan ya gaishesu sannan ya kalli Inna wace itama kallansa take, ya kalli Mumy da Dady wanda suma hanyace “ zuwa nai mahaifin Jalila ya rakani inda mahaifiyarta take, zai sanya hannun sallamarta.”

Inna ta kalleshi sannan ta kalli Dady wanda a ransa yace Oh My God! Wannan wani irin yarone? Ya gama hargitsamin plan dina.

Dasauri ya girgizama Inna kai alamar ba shi bane.
Inna ta kalli Hassan tai dariya tace “Hassan taya za’a sallami mara lafiya? Bayan ba warkewa tai ba?”

Yace “eh wannan damuwarmu ce, dan in aka sallameta hannuna zata koma.”

Mumy d Dady da Inna a lokaci daya sukace mene?

Hassan ya kallesu yace “menene abin mamaki? Ba mahaifiyar matata bace? Banaji cikinku akwai mai hakkinta.”

Inna tace “mene?”
Yace “ why? Bazai yiwu ba? In bazai yiwu ba bari na kira Abba na sanar dashi, ina tunanin kamar zamu amshi kudin mu.”


“kudi?” Hassan ya daure dan kansa wani irin sara mai yakeyi, ya mike ya kalli Dady yace “ina mota.”

Ya juya ya fita alamar wai yana jiran Dady a mota.

Inna tabi kofar daya fita da kallo, sannan ta kalli Dady, takaici da bakin ciki ne suka kamata.

Dady yace “Inna ya zamuyi?”

Cikin takaicinsa da bakin ciki tace “dalla wuce kaje ka rakashi, ko so kake company dinmu ya mutu?”

Dady ya mike ya fita.

Inna takaici ya kamata tace “lalai ba yaran nan bane bashida hankali nice banda hankali dana kawo babban makiyi har cikin gidana da kaina......”

Dady ya shiga mota Hassan yaja suka tafi.

A asibitin premier sukai parking, ya zaiyi?Gashi bayasan asibiti, gashi yabar Jalila agida sabofa bayasan su nemi wulakantata.


#Oneluv💕


🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)



*41*

Tsayawa yai shi bai fita daga cikin motar ba sannan baiyima Dady magana ba, Dady kam wanda yake a zaune yana nazarin yaran ya kalleshi yace “muje?”

Hassan ya fito daga motar sannan ya tsaya yana kallan asibitin, babban matsalarsa bawai shigar bane, zai iya shiga reception ko gun da ba marasa lafiya kamar office, sai dai daga yayi bangaren dakuna na marasa lafiya hankalinsa yake tashi, shiyasa kwanaki yana fara hawa saman beni yaji gaba daya hankalinsa da tunaninsa na neman gushewa.

Da kyar ya daure suka nufi reception din, nan yamusu bayanin abinda sukeso, suka turasu wani office, nan ma sunyi cike cike, suka rubuta kudin da za’a basu, Hassan ya biya, suna fitowa ya kalli saman benin sannan ya kalli Dady dabara ce ta fadomai yace “kaje ka sanar da ita, ka kuma nemi yafiyarta sai ku fito tare ni ina mota.”

Dady ya kalleshi a ransa yace “lalai wannan yaran bashida tarbiyya, ina sirikinsa amma ya maidani dan aike? Kamar wani masinjansa, ko driver? Yana tsaye har Hassan ya fita sannan yai kwafa ya hau saman.

Goggo na zaune tana shafa mai a hannunta, yau kam jikin da sauki, lantana na tattare kwanukan da aka kawo abincin safe zata maidasu gida.

Dady ya turo kofar ba ko sallama, Goggo ta kalli kofa, ganinsa sai dayasa gabanta faduwa, ya shigo fuskar nan a hade ya tsaya yana kallan dakin, kallan Lantana yai yace “ke dan fita.”

Lantana ta mike tai waje, Goggo ta kalleshi tace “ina kwana?”
Dady bai amsa ba yace “ hankalinki ya kwanta?”
Tace “da me fa?”
“A haka in aka kalli fuskarki ba wanda zaiyi tunanin zuciyarki akwai hassada, bakinciki da tsantsar munafirci.”

Goggo cikin mamaki tace “me kake nufi?”
Yace “sai ki taso ki zo kibi mijin yarki da kikasa ya daukeki daga gunmu.”

Goggo cikin mamaki tace “mijin ‘yata kamar ya kenan?wace yar tawa?”
Yace “ni banda lokacin munafircinki, ki taso ki fito, in kuma bazaki iyaba ki cigaba da zama.”

Goggo gaba daya kanta ya daure ta kasa gane me yake nufi, kwallama Lantana kira yai yace “zo ki kwashe kayan nan an sallameta.
Goggonta mike tsaye tadan dosana kafarta tace “Wai Abubakar me kake nufi ne? Ni na rasa me yasa kullum kai burinka ka jefeni da sharri.”
Cikin takaici yace “sharri? Ai kece kike bina da sharri dan na tabbatar badadan ke ba da tuni Inna ta bani company dinsu, amma saboda tana ganin naci amanarsu na kawoki, daga ke har ‘yarki banda bakinciki me kuke tsinanamin? Da na dauka yanzu zan moreta sai gashi yau ta wargaza komai, ni ki wuce mu tafi dan ganinki ma bakin ciki yake sani.”

Goggo kallansa kawai take zuciyarta na wani irin kunna, tace “nikam menene matsayina agunka? Ma dauka ni matarka ce.”

Wata irin dariya yai wanda yasa ta kallansa cikin wani yanayi, yace “mata? Wa? Kedin? Kema kinsan ni ba sa’an auranki bane ko a can baya bare yanzu, ni ba wani aure ko makamancinsa tsakaninmu, ina zaune dake ne kawai saboda yarki da tazamarmin dole.”

Goggo ta share kwallar ta tana neman yin magana ya fita yana cewa “kuma ki sauko yanzu.”

Lantana ta shiga saukar da kaya kasa, dady ya nuna mata motar Hassan, nan aka bude boot din mota aka sasu, itakam Goggo ta dade tana kuka, nurse tazo ta kara dubata sannan ta taimaka mata ta sauko, shigowar Lantana na karashe suka sauka tare.

Tsayawa tai tana kallan motar, Hassan ya taho da sauri gunta sannan ya kalleta.
Kallansa tai cikin mamaki tace “wanene?”
Hassan ya kalleta sannan yace “bari na kira kuyi magana da Jalila.” Dan baisan me zaice ba.

Matsawa yai ya kira number Sageer.

Sageer na daki lokacin da Hassan ya kirashi, yayi mamakin kiransa ya amsa da sauri yana cewa “yaya lafiya?”
Hassan yace “Sageer ina Jalila?”
Yace “tana sama dazu ta hau.”
Hassan yace “please ka dan kai mata waya.”

Yace to sannan ya mike ya fito.

Jalila tafito daga wanka kenan ta zura wata doguwar rigar atamfa, dan dama kwalliya bata dameta ba saboda ba barinta ake tana yi ba, sannan bama wani iyawa tai ba, balle hankalinta ma ba’a kwance yake ba bare tai tunanin yi.
Mai kawai ta shafa ta dan shafa hoda tasa turare, dan kwalimta kawai ta yafa akanta, ta zauna kenan ta dau wayarta taji knocking.

Mikewa tai ta bude.

Ganin Uncle ne yasa ta tsaya tana kallansa, shima kallanta yai sannan ya mika mata waya yace “Yaya ne.”
Amsa tai bata rufe kofar ba ta juya zuwa ciki tana cewa “Yaya!”

Yace “yauwa.” Tana jiran ya sake magana kawai taji sallamar Goggo, jikinta na rawa cikin rawar baki tace “Goggo.”
Goggo tace “jalila?”

Jalila hawaye ya zubo mata tace “Goggo kina ina?”
Tace “gani a kasan asibitin ance wai wani ne ya zo daukana shikuma naga bansanshi ba, shine ya kiraki, kinsanshi ne?”

Jalila tana kuka tace “ki biyoshi Goggo, ke kadai ce?”
Tace “a’a mahaifinki nanan.”
Jalila tace “Goggo dan Allah karki nuna bakinsanshi ba, ki bishi zai kawoki inda nake.”

Cikin mamaki Goggo tace “inda kike? Kedin bakya gida?”
Jalila tace “inkinzo zan sanar dake komai.”

Goggo tace to, sannan ta kalli Hassan ta mikamai waya, baice ma Jalila komai ba kawai ya katse wayar.

Jalila ta juyo inda Sageer yake tana hawaye, tace “Uncle!”

Shikam hankalinsa ya tashi ganin tana kuka yace “menene? Wani abun ya faru ne?”

Gani yai tana dariya tana kuka, tace “Uncle, Yaya ya daukomin Goggona.”

Tsayawa yai sai dai yanzu baisan me zai kwatanta abinda yakeji ba, yai murmushi yace “duk da bansan meke faruwa ba, it look like abin farinciki ne, sannan alama ce ta shakuwa na shiga tsakaninku, tunda gashi har yasan abinda ba wanda ya sani, sannan lafiyarsa ma nasan samun kusanci dake ne yasa, uhm congratulation, Allah ya barku tare.”

Ya juya jiki a sanyaye da kallo ta bishi zuciyarta na tausayamai, ta tabbatar Uncle na santa sosai bawai ya rabu da ita bane dan kansa sai dai zumunci da kaunar da ke tsakanin shi da yayansa.
Hawayenta ta share sannan ta zauna abakin gadon tana tunanin me zata ce ma Goggo?

Hassan kam Goggo na shiga mota ya kalli Dady yace “Allah yasa akwai kudi a jikinka”
Dady yace “babu, menene?”

Hassan ya sa hannu a aljihu ya dauko 1000 yace gashi ka hau mota dan gida zan wuce daga nan.”

Dady yace “mene? Kai ni na haifi Jalila fa, bawai dan aikin gidansu bane, wai me yasa......”
Ganin Hassan yai ya shiga mota kamar ma badashi yake ba yaja yayi gaba, ran Dady a bace yabi motar da kallo.

Hassan kam jan motar yai sukai gaba, Goggo da Jalila na baya, suna fara tafiya Goggo tace “meke faruwa? Ya akai Jalila tabar gida?”

Hassan ya dan shafi kansa dake ciwo yace “ Jalila zata miki bayani, zaifi cancanta ta miki bayani da kanta.”

Goggo tai shiru tana addu’a aranta, Allah yasa Jalila ba wani mugun abu ta fada ba, sai dai kallan Hassan yasa wannan ya tafi daga ranta.

Kallan tangamemen gate din da aka bude yasa Goggo ta kara cewa “tana cikin nan?”

Yace “eh.”

Kallan gida take har yai parking, da gudu Jalila wacce ke tsaye a waje ta taho bude kofar inda Goggo take a zaune.

Kallanta Goggo tai sannan ta kalli gidan zatai magana Jalila ta rungumeta ta saki wani irin kuka.

Hassan ya juyo ya kalleta, me yasa ta fita kuka ne? Shifa bayasan kukan nan.

Kallanta yai yace “ kuka zaki tsaya yi ba zaki taimaka mata ku shiga ciki ba?”

Ta share hawayenta tana cewa “Goggo muje.”

Hassan ya fito ya wuce ciki bai jira su ba, a falo ya taradda Ummy da alama fitowarta kenan, kusa da ita yaje yace “Ummy ina Abba?”
Tace “yana falon sa.”

Yace “Ummy muje akwai maganar da zamuyi.”

Kallansa tai cikin jin dadi tace “da alama Hassan dina yanzu bakinsa na kokarin yin magana akai akai.”

Hassan ya juya ya kwankwasama Sageer kofa ya fito, yace “muje.”

Nan suka shiga kofar falon Abba.
Yana zaune rike da qur’ani dan suna shigowa Ummy ta dauko ta mikamai itakuma da bata sallah tadau littafin addu’oi.

Shigowar su ne yasa ya kai aya sannan ya ajiye ya kallesu.

Zama sukai Abba yace “lafiya?”
Ummy tace “Hassan ne zaiyi magana.”

Abba ya kalleshi yace “Hassan!”
Zama yai sannan ya dansa hannunsa na haggu akansa dake ciwo yace “tare nake da bakuwa.”

A tare sukace “bakuwa?”
Hassan yace “eh, tunani nake boys quarters din mu zansa a gyara sai na maida ita can.”

Abba yace “naji ba wai wannan bace maganar, wacece bakuwar? Itace tambayarmu.”

Hassan yace “mahaifiyar Jalila.”

Abba cikin mamaki yace “me kake nufi? Taya zaka dauko mata a gidan mijinta da arzikinta da komai ka kawota boys quaters?””
Hassan yace “bansan ta ina zan fara bayani ba, sai dai ita zatayima Ummy kudan bata lokaci kadan, abu daya zan iya fada, wacce kuka sani a matsayin mahaifiyarta ba ita ta haifeta ba, ban kyauta ba na kawota ba da saninku ba sai dai wannan ne kadai solution din da yazomin”
Ya mike saboda kansa dake ciwo ya fita.
Abba yace “meke faruwa takamaimai? Ni na kasa ganewa.”

Ummy ta dafashi tace “ mu jira kamar yanda yace, na tabbatar yana da dalilinsa, kasan Hassan mutum ne da baya shiga abin mutane, tunda kaga ya shiga wannan i am sure da dalili.”

Sageer ta kalla wanda yai shiru yana tunani, tace Sageer taimaka muje mu shigo da ita, sai mu sata a dakin Ameera inyaso gobe sai a gyara can din.”
Nan suka mike suka fita.

A waje sukaga Goggo ta tsaya tana cema Jalila, “nifa bazan shiga ba sai naji inane nan.”

Jalila ta daure tace “ Goggo dan Allah mu shiga wlh zan fada miki.”
Goggo tace “Jalila.”
Jalila ta rike hannayenta tace “ Goggo gidansu mijinane.”

Goggo tace “me? Miji? Miji kamar ya?”

Sageer har zai fita ya tuna Goggo fa ta ganshi ta kuka san sunanshi, kallan Ummy yai yace “Ummy bari na dan shiga toilet it’s urgent.”

Dariya tai tace “to a fito lafiya.”
Ya juya da sauri, yana cewa gwara mu mata bayani kafin ta fada cikin mutane.

Ummy tana turo kofar taji Goggo na cewa “Jalila aure kamar ya? Aure bansani ba? Auran dole aka miki?”

Cikin mamaki Ummy a karasa tace “meke faruwa? Bangane aure mahaifiyarki bata sani ba, meke faruwa Jalila?”

Jalila ta kalli Ummy idanunta fal tace “Ummy.”

Ummy ta kalli Goggo sannan ta kalli kafarta dake ciwo, tace “muje ciki sai muyi maganar a nutse.

Goggo bata musa ma Ummy ba suka shiga ciki.

#OneLuv💕


🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*


     *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
  (_D home of expert and perfect writer's_💡)

_Should i start with sending my special greetings? Special greetings to u all my fans, thanks alot for the love and support, a sincere thanks to you all from the bottom of my heart 💕Luv u all._

*42*

Ummy ta zauna akan gadon kusa da Goggo akwai abubuwan da takesan ji, sai dai ta tabbatar matarnan ba lafiya ce ta isheta ba, dan ga kafartanan.
Kallan Goggo tai tace “ki kwanta ki huta dan Allah karkiyi tunanin komai har sai hankalinki ya kwanta.”

Goggo ta kalli Ummy tace “Hajiya ta ina zan kwantar da hankalina, aure? Bansani ba?”
Ummy ta kalli Jalila ta mata alama da ta fita, sannan ta kalli Goggo bayan Jalilan ta fita tace “ sai yanzu na fahimci me yasa yarki batada walwala duk kuwa da yanda naso ta saki jikinta da gidan nan, na fahimci an cutar dake, an munafurceki, sai dai bayanda za’ai a maida hannun agoggo baya, ki nutsu ki kwantar da hankalinki, inkin huta anjima sai muyi magana, sai kiji abinda ya faru nima naji abinda ya faru, amma yanzu ko saboda ‘yarki da kwanciyar hankalinta kiyi hakuri, lafiyarki itace abin dubawa a wannan lokacin.”

Goggo kallanta kawai take tana mamakin yanda mace mai kudi, mai aji, mai kyau haka take magana cikin sanyi da nutsuwa, da alama Matarnan macece mai tsananin imani, da kaunar jama’a da sanin darajarsu.

Kasa musama Ummy tai ta daga mata kai alamar fahimta, Ummy tace “nagode, ga toilet nan in zakuyi amfani dashi.” Ta fada tana kallan Lantana.

Goggo tace “Angode.”
Ummy tai waje ta turo kofar.
A waje taga Jalila a tsaye, murmushi ta mata tace “me kike anan?”
Jalila ta kalleta da idanunta da sukai raurau tace “Ummy kiyi hakuri, sannan nagode....”



Ummy tai murmushi tace “wanda zakima godiya daban bani bace.” Sannan ki barta ta huta zuwa anjima, amma meke damunta?”
Tace “hawan jini da diabetes.”

Ummy ta kalli kofar dakin cikin tausayawa sannan tace “shikenan mu barta ta huta.”
Jalila ta daga kai alamar to sannan tai hanyar sama.

Hannu tasa tana neman bude kofar dakin, tsayawa tai tana rike da hannun kofar amma bata bude ba, tana tunanin abinda zata cemai, da wani bakin zata fara mai godiya?

A hankali tai ajiyar zuciya sannan ta tura kofar, a kwance ta ganshi kamar mai bacci, kusa dashi taje ta tsugunna tana kallansa, hawaye ne yazobo mata wanda batasan ya diga akan kuncinsa ba, a hankali ya bude idanunsa.

Kallanta yai tana share hawayenta, a hankali ya ke magana yace “Menene? Wani abun ya faru ne?”
Hawayenta ta karasa gogewa da sauri sannan ta girgiza kai tace “bakomai.”
Yace “and why?”

Tace “bansan me zance maka bane, kawai sai naji hawaye....”
Idanunsa ya lumshe kansa na sarawa yace “ it looks like it’s ur hobby.”
Tace “kukan?”
Ya lumshe ido kawai, kallansa tai sannan tace “bakajin dadi ne?”
Bai tanka ba sannan bai bude ido ba, hannunta tasa a kansa wanda ke mai ciwo kamar zai tsage, jin zafi rau akan tai, da sauri ta kai hannu wuyansa, nan ma zafi a rikice tace “Yaya bakada lafiya, zazzabi ne a jikinka, jikinka zafi.”

A hankali ya bude idanu yace “why? Are u worried about me?”

Da sauri tace “sosai ma, ka tashi muje asibiti.” Ta fada tare da mikewa tana kokarin dagashi, hannu tasa ta riko hannunsa tana neman dagashi.

Jawo hannunta yai, ta fada jikinsa, shiru ne ya ratsa dakin, ita kuma zuciyarta na harbawa da sauri da sauri, a hankali ta kalleshi, idanuwansa a rufe suke, sai cewa yai “ sai yaushe za’a daga ni?”
Ta kalleshi ta kalli kanta data danneshi, neman dagawa tai sai taji hannunsa na rike da ita gam.

Tace “to ai.....”
Idanu ya bude a hankali ya kalleta, a hankali tai kasa da idanunta.
Saketa yai ta mike ta zauna a gun, bata tashi ba tace “Yaya dan Allah muje asibiti.”
Yace “bana zuwa asibiti, sannan ni nasan jikina kawai nayi abinda bansaba bane shiyasa, karki damu.”

Idanu ta kuramai bayan ya maida idanunsa ya rufe, a hankali tana kallansa tace “Yaya nagode, ban taba tunanin wannan ranar ba.”

Bai tanka mata ba, idanunta ne suka ciciko tace “Kayi hakuri Yaya nagode sosai har bansan ta ina zan fara ba.”
Yace “hakurin me?”
A ranta tace “da na dauka kai mutum ne mara tausayi da mutunci.”

A fili tace “for everything.”

Idanunsa ya bude a hankali sannan ya kalleta, itama kallansa takeyi, sai dai da sauri ta maida idanunta gefe.

Yana kallanta yace “ya zakiyi?”
Tace “name?”

Idanunsa na kanta tana kallansa taga ita yake kallo ta dauke idanta da sauri, yace “ya zakiyi insu Ummy sun tambayeki?”

Tace “ bansan ya zanyi ba, wata zuciyar na sanar dani in fadi komai, wata kuma na tunanin abinda zai faru da Dady dan na tabbatar Inna bazata barshi ba.”

Kamar bazaiyi magana ba, dan harta mike zata nemomai maganin zazzabi ragowar tata wanda takaima Ummy taji muryarsa yace “ kiyi abinda ya kwanta miki a rai.”

Juyowa tai ta kalleshi tace “In na tuno abinda yama Goggo tundaga haduwarsu zuwa yanzu, sai naji kome zai sameshi bazan damu ba sai dai bansan meke damuna ba, I wish nima inada dauriyar zuciya ko rabin taka ce.”

Alama yamata da hannu akan ta matso, matsowa tai gunsa, ya mata alama data

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login