Showing 102001 words to 105000 words out of 146738 words
Chapter 35 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt
shima yasamu nutsuwa yanzun.
Kad'an tad'ago idonta tasaci kallonsa, saitaga Ashe shima d'in ita yake kallo, murmushi takumayi tareda kauda kanta gefe.
Muryarsa can k'asa yace taji yace "Jalilah!"
Kasa d'agowa tayi ta kalleshi, amma ta amsa da "na'am".
Shirune yaratsa d'akin Jalilah tana wasa da yatsun hannunta, shikam Hassan idonsa k'yam akanta, ko k'yaftawa bayayi, jinsa yake tamkar wani sabon mutum, bayanin Abba yasaka zuciyarsa ta k'ara bud'ewa, dan Abba ya dade da shi bayan su Ummy sun fita yana kara nusar dashi da nunamai ba laifinsa bane, zuciyarsa ta kuma rage nauyi sosai, wata nutsuwa ta musamman ke ratsa dukkan sassan jikinsa, harma yana tuhumar kansa miyasa bai fad'ama su Abba gaskiya ba a duk tsawon shekarunan? miyasa yasaka ummynsa mai sonsa da da k'aunarsa aciki k'uncin damuwa har wannan shekarun, tabbas ya yarda *JALILAH!* alkairice a rayuwarsa, Dan itace ta bashi k'arfin gwiwar canja komai, yafirzo k'aramar iska daga hancinsa...
Jin yayi shiru sai Jalilah takuma d'ago idonta, karaf suka kalli juna itadashi, tafin hannunta tasa tarufe fusakar tana k'aramar dariya.
Shikuma ya lumshe idanunsa yana gyara zama.
Tashi tayi zata barmasa d'akin yai saurin rik'o hannunta dukda jikinsa babu k'arfi sosai.
Gabamta yad'an fad'i tana jira taji ya janyota amma sai taji shiru.
"Dawo ki zauna to, magana zamuyi".
Rintse ido tayi, kusan 1minute sannan tadawo ta zauna, shima zamansa yagyara sosai yadawo kusada ita....
Jalilah!
Kallansa tai yanda yake kallanta yasa tai saurin sauke idanunta, gani tai kawai ya koma ya kwanta akan cinyarta, ya juyo da fuskarta saitinta.
Kallansa tai tare da zaro ido, yace " dazu ba haka kika min ba? Na tabbatar dana bude idona a haka na gani." Ya fada tare da sa hannunta akansa.
Kallansa tai tare dayin murmushi tace "tunda ka gani menene na sake gwadawa?"
Yace "abinda kika fada nakesan ki maimaita."
Ta dan juya kai tace "ni namanta ma me nace."
Murmushi taga yayi, ta zubamai ido batasan a fili ta fada ba sai jitai yace " haba? Kinasan kiga ina murmushi?"
Da sauri ta kalleshi ashe datace murmushi na masa kyau a fili ta fada.
Kallanta yai yace "badai kina kara sona bane inkika ga ina murmushi?"
Da sauri ta kalleshi tace "naam?"
Yace "me? Bakya sona?"
Bakinta na rawa tace "ni bance ba."
Ya kara gyara kwanciyarsa yace "basai kin fada ba kukan da kikai ya bayyana min."
Kallansa tai da sauri, da gaske? Abinda zuciyarta ke tambayarta kenan......
***********
"Ya kukayi da mijin naki?".
Innace mai maganar tana tattara wasu takardu waje d'aya.
Momy tace, " ya amince inna, k'ilama zuwa gobe yaje ya dawo da ita".
"Humm, Ku azatonku zata dawo cikin sauk'i? kokuwa ita Jalilan kuna tunanin zata amince cikin sauri?".
"To amma inna kinsan da hakan miyasa kikace yaje d'in?".
"Kallonta inna tayi da k'yau, kafin tasaki guntun murmushi "Shi dai yaro yarone, aii sometimes bana banbance tunaninki dana Safeenah dama kisamin ido kiga inda na dosa, tunda ke kullum naki hasashen daban, ke ba komai a gabanki sai wannan mijin naki da ba abinda zai tsinana miki."
Tabe fuska Momy tayi, "to nidai Dan ALLAH koma miye dai kika shirya banason yataba mutuncin Abakar, dan nikam bazan dauka ba."
Sosai inna ta kalleta kafin tace, "bazai ta6aba, tashi kije 'yar gatan miji".
Kuma had'e fuska Momy tayi, kafin tatashi, tasan bak'ar maganace inna ta fad'a mata, itakam koma miza'ayi saidai ayi, bazata bari a wulak'anta mata mijiba ehe.
Nace, "humm".
*************
#OneLuv💕
[30/11, 20:28] +234 803 688 2706: *_🗯JALILAH!!🗯_*
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
*58*
Alhamdulillah zuwa yanzu nutsuwa tazoma hassan, dan a kwanakin nan ko kad'an ciwonsa baya tashi.
Abba da Ummy sunma rasa wani irin farin ciki zasuyi, ga wata k'aunar jalilah dasukeji har cikin jininsu, yarinyar tazamarma zuri'arsu alkairi.
Ummy ta kalli Abbah dake zaune yana kallon labarai, fuskarta d'aukeda murmushi tace, "wlhy bansan wane irin alkairi zamu yima yarinyar nanba mu nuna mata jin dad'inmu akan sauyin rayuwa data kawo a duniyar Hassan".
Kallonta Abba yayi shima yana d'an murmushin, kafin ya maida kansa ga TV "gaskiyane, yarinyar ta cancanci kowanne irin alkairi, Dan ko'a mafarkina bantaba kawo zamu sami wani cigaba ba akan ciwon Hassan, dubi dai irin shekarun damuka d'auka muna famar bin likitoci na kasar nan da kuma na ketare, sosai nake jin dadi da alfahari da auran yarinyar nan."
"Ta cancanci a k'aunaceta kam....."
Maganar Ummy ta katse saboda jin wayarta na ringing .., daga ita har Abba wayar suka kalla, cikin damuwa Abba yace "ina ganin kawai acire layinnan, idan takira taji baya aiki ai dole ta hak'ura ko?"
"Ba cirewa nak'iba, muhimman mutane dake da number d'inne damuwa ta kuma kaga aii suna kira ai, amma kai yakakeji yanzu gameda ita? dan Allah zuciyarka kadai zaka duba karka damu dani ko su Hassan."
Shiru yai yana kallanta kafin yai mata murmushi ya kamo hannunta yace "Hummm....Alhmdulillah, dan kaso mafi yawa yaragu, yanzu sai lokaci-lokaci ma nake tunota, sabanin da danakejinta har raina, lalai ba shakka na tabbatar yanzu wani abun sukamin, sai dai Allah ya rabamu da sharrin mutane ni........
Ummy ta kalleshi tare dayin yar dariya kadan tace
"miye nak'in k'arasawar to?"
Shima Abba yar dariyar yayi "Ummyn Hassan, yanzu da Hassan zai yajini ai sai an samu wata yar karamar matsala, shi da bai had'a damuwar ummynsa data kowaba."
Ummy tai murmushi tace "Kaima kasan Hassan tun yana yaro haka yake, zan iya ajiye Husain nadan shiga ko toilet amma shi yana tsaye a kofa yana jirana, ko ina zani yana biye dani, sannan kaima kasan yanda Hassan ke tsananin kaunarka, na tabbatar abinda yake zargin ya aikata shine dalilin dayasa yake neman janyeka daga jikinsa saboda in kasani kar abin ya wahalar dakai."
Murmushi ya mata shima sannan ya saki hannunta yace "na sani, sannan ko da wasa ni ban dauki abinda yakemin a matsayin haka ba, tunda ni nasan yanda ya damu dani, tsautsayine dai da kaddarar data afka mai, Allah ne kadai yasan yaro dan shekara goma sha ya yai rayuwarsa a wannan dakin...."
Ummy tai shiru cikin tausayi tace "sai nakeji duk laifin nawa ne, kamar nice ban kula dasu yand......"
Kallan daya mata ne yasa tai shiru.......
Yace "mu ma wadanda suka rasu addu'a mu kuma mu nemi cikawa da imani."
Tace "hakane Allah ya jikansu da rahama, amma zaka fadawa mahaifin Sudais ne?"
Yace "su da basa kasar? Sai dai insun dawo mayi maganar."
Nan ta jinjina kai tare da kara maidakai kan Tv din da yake kallo.
*********
Bayan sun kammala had'a breakfast Ummy tabar Jalila ta karasa sauran dan dama haka suka saba, tana cikin shirya abincin a dinning Sageer ya fito, sotake yau Hassan yafito ayi breakfast d'in dashi, shiyyasa bata d'iba musuba, ta shirya komai a kan dining.
Tsayawa yai yana kallanta yana jin dadin yanda ta canza musu gida, dan da a koda yaushe matsalar Hassan sai ta maida gidan kamar ba kowa, amma yanzu kam Alhamdulila.
Ji tai ance Jalila!"
Juyowa tai ta kalleshi tace "Un.... Ya Sageer ina kwana?"
Murmushi yai sannan yace "Jalila mungode, mungode sosai da farincikin dakika kawoma family dinnan wannan shine abinda naso ki fahimta a waccan ranar, Yaya shine yafi cancanta da samun irinki, amma dan ALLAH ki gafarceni, da. nakula har yanzu kinkasa sakin jiki dani a gidanan, bansan ko har yanzu kina fushi daniba, ni kanin Yaya ne haka kawai zakisa a ranki kinga........."
'Dagowa tai ta kallonshi, wannan yasakashi yin shiru batareda ya k'arasa maganar bakinsaba, ta gyara tsayuwarta tana kallonsa sosai, idonta ya fara tara hawaye tace "Yaya sageer nafad'a maka tuni komai ya wuce agareni, kuma zuwa yanzu na fahimceka, bani yakamata ka godemawaba, kaine ka cancanci a godema, domin ka sadaukar da farincikin ka saboda d'an uwanka, samun irinka a wannan rayuwar sai an tona, kazama mai rama alkairi da halacci, ta share kwallar data zubo mata akan kumatunta sannan tacigaba
"Ya Sageer ka cancanci kowanne irin godiya, amma kayi hak'uri da rashin sakin jikina agareka, nasan ahankali komai zai zama labari insha Allah, kaima Allah na tabbatar bai manta dakai ba zai baka mace tagari wacce tafini komai sannan mai sanka da k'aunarka".
Kallanta yai tare da sakin murmushi wanda har hakoransa suka fito yace "nagode Jalilah, sannan dan Allah ina rok'on wata alfarma agareki".
Kallansa ta sakeyi tace "ina jinka, Allah yasa bai fi karfina ba."
Sageer ya kalleta yace "Jalilah inason koda wasa kar dan Allah kar wanda yasan wata alak'a tataba shiga tsakaninmu, sannan dan Allah ki kuma nika kulawar dakikema Yaya akan tada, kullum burina yadawo normal mutum kamar kowa, inga yana farinciki, yana shiga jama'a, yana mu'amullah acikin mutane kamar kowa."
Kanta ta gyad'a a kunyace, tace "Allah ya bani iko Ya Sageer, zanyi iya k'ok'arina kai ma sai kai naka, har cikin rains ina tsananin tausayin halin da Yaya yake ciki nima, dan babu abinda yakai k'untatar zuciya a rayuwa, mutum bacin ran yini d'aya yashiga ya yake tsintar kansa, bare tsawon shekaru irin haka"
"Gaskiyane, mucigaba damasa addu'a, inaji ajikina zaki sauya komai insha Allah, nima kicigaba damin addu'a Allah yabani wadda zata tallafeni irin haka."
Tausayi yabama Jalila, dan haka takuma k'asa dakanta, karka damu Ya Sageer dan Allah kaima ka dawo yanda kake da mai walwala, dan Ummy ta bani labarin bahaka kakeba abaya, duk da bazata nunama ba na tabbatar abin na damunta."
Murmushi yai yana k'ok'arin barin wajen, "karki damu, zan canja insha Allahu."
"ALLAH yasa" itama tafad'a tana fara tafiya domin duba Hassan.
Da sauri Hassan yakoma baya dan karta hangoshi, tun farkon maganar tasu yana tsaye, amma basu ganshiba, saboda sun juya masa baya, yaje yana kokarin shiga falon yaji suna zancenshi, fuskarsa dauke da murmushi ya tsaya a bayan bango yana jikinsu, a hankali kunnensa ya dinga juyo mai hirarsu.
Yana zaune bakin gado Jalilah tashigo cikin d'akin da sallama.
Bai kalletaba amma ya amsa, da 'yar fara'arta takaraso inda yake tace "Laa Yaya ashe katashi? nifa wai hawowa nai na tasheka."
"Na tashi!"
Haka kawai yace ba tare da ya kalleta ba, kallon data masane yagane shima maganar tasa tafita da tsauri, amma saiya dake.
Jalilah batayi zuciya ba tace "Yaya mai zai hana yau kazo kaci abinci tareda Ummy da Abbah, kodan kakuma saka zukatansu cikin nutsuwa?"
Yanzu kam bashida zabi. daya wuce kallonta da kyau, yarasa wane irin mahaukacin so zuciyarsa takema Jalilah, baikamata yaji zafin maganganunsu da Sageer ba, musamman idan yai dubi da sadaukarwar dasukayi suduka agareshi, yadad'e yana mamakin yanda kokad'an Jalila bata sakewa da sageer dan Sageer mutum ne mai faran faran yasan sageer da saurin sabo da yawan barkwanci.
Ashe akwai abinda ke tsakaninsu, ya akayi haka ta faru? tayaya iyayensa suka aura masa budurwar k'aninsa? shin basu sani bane? Da wani ido zai kalli Sageer? Ace shi da yake babba bai barma kaninsa abu na sai shine kanin nasa zai barmai? kai amma yasan babu yanda za'ayi Abbah ya aura masa wadda yasan Sageer na nema amatsayin matar aure kuma, to meke faruwa.......?"
Girgiza hannunsa da jalilah tayine yakatse masa tunanin nashi.
Tace "Yaya lafiya kuwa?"
Baice komaiba, amma yamik'e tsaye, gani tai yanufi hanyar fita, sai da ya bud'e k'ofar sannan yajuyo ya kalleta yace "kona koma na zauna ne?"
Da Sauri tamik'e tana murmushi tace "a'a Yayah ina fa."
Karasowa tai kusa dashi a hankali tace "Nagode."
"Da akayi me fa?"
Yai maganar yana karasa fita daga dakin.
Ta biyoshi tace "daka amince."
"Hmm" kawai yace, yacigaba da tafiyarsa.
Suna sakkowa kuwa saiga Abba da Ummy suma sun fito.
Hassan ya karasa kusa dasu ya gaishesu, duk cikin fara'a suka amsa masa, Sageer ma dake zaune a falo yataso, gaishe da su Abba yafarayi, kafin ya gaida Hassan shima.
Cikin danne abinda ya tokare mak'oshinsa ya amsa, harda mik'ama Sageer d'in hannu tareda daga kafadarsa, a tare suka mike suka nufi cikin falon.
Ummy da Abba suka bisy da kalli cikin jin dadi, haka suka k'arasa kan dining suka zauna, Jalila ta shiga ajiye musu plate, kowa ka kalla fuskarsa a sake take.
Abba da Ummy kuwa cikin mamaki suke da kallon Hassan daya ja kujerar dining ya zauna, alamar yau taredasu zaiyi breakfast.
Cikeda jin dad'i Sageer yace "Yaya yau zakaci abinci damune?"
Kansa ya jinjinama Sageer din.
Gaba d'ayansu farincikin ya bayyana a fuskokinsu, Ummy harta kasa boyewa ta furta " Alhamdulillahi ala kulli halin".
Abba ma abinda yafad'a a zuciyarsa kenan.
Sageer kam harda d'an rungume Hassan saboda jin dad'i, Ummy tace "inama Auta tana gida yau taga abinda take buri a rayuwa?"
Jalila ai murmushi tace "Ameera yar makaranta."
Hassan ya juya yana kallon Jalilah da itama jin dad'in yasakata taketa murmushi, ganin yanda dukkansu suke farinciki, sai itama takema nata dangin irin wannan fatan wataran.
Kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru.
Abba ne yalura da hakan, yace "Jalila taho mana ki zauna."
A kunyace ta matso zata ja kujerar kusa da Ummy, Ummy tace "Malama Jalila zauna kusa da mijinki, nima bakiga a kusa da nawa nake ba?"
Da saurin tai kasa da kanta saboda kunya, Ummy ta kalli Sageer tace "wanda yasan gauro ne sai yai sauri ya kawo tashi matar."
Sageer ya kalleta sannan ya kalli Abba cikin shagwaba yace "Abba kaji Ummy ko?"
Abba yace "gaskiya kar a sake cema d'ana gauro inba haka ba kuma yanzu nai zuciya namai aure."
Kallansa Sageer yai yace "aure?" Ya matsa daga gun Abba da sauri.
Tuntsirewa da dariya sukai yanda ya matsa din, Hassan ya kalleshi cikin wani yanayi da shikansa baisan wani iri bane.
Yaukam cikin far in ciki sukayi break d'in nan, dukda Hassan baya magana, kuma koda komai yafito fili dama har yanzu bawai yana yawan magana baneba, baikuma saki jiki dasuba gaba daya, amma abinda yazama dole yayi magana akansa yanayi.
Bayan sun gama Abbah yafita aiki cikin tsantsar farim ciki.
Suko duk a falo suka zauna suna hira, harda Hassan, dukda shikam ko k'ala bai ceba a zaman nashi, amma yana saurarensu, gaba daya hankalinsa nakan abinda yaji, kodai zuciyarsa ce take kara mai? Kodai ba wani abu tsakaninsu? Kallansu yai yana nazarin su, soyake yagano abinda ke faruwa? suna son juna har zuwa yanzu kokuwa? Su kuwa basusan dawan garinba, damage itama jalilan bawani baki take sakawa a hirarba, k'arfin hirar Sageer da Ummy ne, dan Sageer ya iya barkwanci, sai dai daga anyi abin dariya zata sa dariya.
Wajen karfe 12 Hassan ya mike ya hau sama, Ummy ta bishi da kalli cikin jin dadi.
Jalila ma bata dadeba ta mike tahau sama, a kwance taga shi kamar mai bacci.
Toilet ta shiga ta fito sannan ta kara kallansa, kamar bacci yake kamar kuma ba bacci yake ba, kamar tai magana sai kuma ta jona wayarta a charge kawai ta fito.
Sunkai tsawon lokaci suna hirar, har karfe biyu tai Ameera ta shigo.
Tana shigowa ta baje a falo wai ta gaji, Ummy tace tashi malama ki wuce kitchen.
har agogo yanuna 2, Ummy tace, "Ameera tashi kishiga kitchen, yau kece zakiyi abincin rana, kullum sai dai kici ki kwanta."
''Wayyo Ummy, nikad'ai zanyi?yanzu fa na dawo daga makaranta."
Ummy tace "to kedawa zakiyi? Tunma kafin rana tamiki kitashi kije ki d'ora, dan abbanku da wuri zai dawo yau, inya dawo baki gama ba kinga sai ki bashi amsa."
Ameera ta shagwabe tare da kwanciya akan kujera tace "Ummy wlh....."
Kallan da Ummy ta mata ne yasa tai shiru ta mike tsaye kamar zatai kuka.
"Karki damu, tashi muje natayaki kinji Ameera". Jalilah tayi maganar tana dafa hannun Ameera.
Cikin murna tace "yauwa matar yayana"
Hararta Ummy tayi "Jalila kiyi zamanki, taje tayi ita kad'ai, zauna ki huta".
Jalila tace "Ummy bangajiba aii, bara na tayata yanzun nan sai kiga mun gama."
Bata bari Ummy tasake maganaba taja hannun Ameera suka tafi kitchen da sauri.
Ummy tabisu da kallon sha'awa da tsantsar k'auna.
********
Tunda Abba yafito daga gida Zaliha kebin motarsa abaya abin da zai baka mamaki a ina tasan gidansa?tun jiya da yamma tashigo garin, a hotel ta kwana, yau kam da farar safiya tazo unguwar tasu take jiransa, guri tasamu tayi parking tana dakon fitowar Abba daga gida. tana hango an bud'e gate tafara addu'ar ALLAH yasa shine, ganinsa kuwa tasaki wata ajiyar zuciyar dan dad'i, haka taita binsu abaya har zuwa office.
Yana zama a kujera yayinda Secretary d'insa kemasa bayani akan wasu bak'i, dakuma wasu abubuwan da suka faru a jiya sukaji ana knocking d'in k'ofar.
Atare suka kalli k'ofar Abba yace, "munada bak'ine?".
Yace "a'a gaskiya Alhaji, amma bansaniba ko shigowarmu nan suka zo"
"OK, jeka gani to".
Yana bud'e mata, batajira komaiba taturo kai cikin office d'in tana yauk'i, sanye take cikin wani shegen leshi, daya gama had'uwa, ga d'inkin yayi mata k'yau sosai tamkar zata fashe saboda matsetan dayayi, takawo siririn gyale ta d'ora a kafad'a, bak'amar fad'uwar gaba Abbah yajiba azuciyarsa, saida ya had'a da addu'ar " Hasbinallahu wa ni'imal wakil".
Ganin haka Secretary din yafita, dan hannu zaliha tad'aga masa alamar yafita.
Yanda kasan gunki haka Abba ke zaune yana bin Zaliha da kallo, harta k'araso inda yake.
Mai makon ta zauna akan kujerar dake gaban desks din, saita zauna a saman desk d'in kawai tana juya idanu "haba myT! babu fad'a miya kawo gaba kuma?".
Yanda tayi maganar cikin matuk'ar salo, dole Abba ya tsirama labbanta dasukasha janbaki ido, bai iya cewa komaiba sai ajiyar zuciya ya sauke, jiyake kamar yajawota jikinsa, amma ya daure yana ambatar dukkan addu'ar datazo bakinsa, yana neman d'aukin ubangiji yafiddashi akan wannan masifa daya tsinci kansa aciki.
***********
#OneLuv💕
[30/11, 20:28] +234 803 688 2706: *_🗯JALILAH!!🗯_*
Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_💡)
Day
*59*
Ummy tabi Sageer da kallo, yanda ya ajiye waya da sauri yamik'e bayan yagama ansa kiran da'aka masa, sama yahau da sauri, Hassan na kwance ya shiga bai ko jira ya amsa sallamarsa ba, yasan Jalila na kasa.
Hassan na kwance yana tunanin abinda ke faruwa tsakanin Sageer da Jalila yaji shigowar mutum.
Sageer ya matso ya masa bayani, ai bai bi takan Sageer ba naga ya sauko da sauri ya dau key din mota ya fita "Ummy ina zuwa" abinda ya fada mata kenan a sanda ya ganta a zaune.
Kafin ta amsa masa yafice, tad'anji zanyi aranta, tunda yau ga Hassan zai fita harda fad'in yana zuwa, tamance shrkarun daya d'auka bai Sanar mata zai fitaba.
Sageer na saukowa yaga har ya ja motarsa ya fita, motarsa shima ya shiga yana tunani, ya bishi ne?
Can kawai yaja motar sa shima ya fita.
***********
"Alhajina