Showing 66001 words to 69000 words out of 146738 words

Chapter 23 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt

23 Nov 2025

5772

samu Goggona?"

Yace "wani abun? Kamar me kenan?"
Tai shiru ta kasa magana, yace "dan uba yazo ganin yarsa sai ya zama sai akwai matsala?"

Jalila ta kalleshi tace "a'a ba haka bane."

Yace "Jalila ni mahaifinki ne, ki daina dararewa da ni."

Ta kalleshi kawai bata ce komai ba.

Matsowa ya danyi kusa da ita yace "jalila magana nakesan muyi."
Kallansa tai cikin tsoro, yace "Nikam ya kukai da mijin naki?"
Tace "wani mijin?"
Yace "wanda kukazo tare mana, badai wani abun kika fadamai ba ko? Naga kamar baiji dadi ba ranar."

Jalila ta kalleshi gabanta na faduwa ta kasa magana, Dady yace "amma yasan Goggo ce ta haifeki ko?"
Jalila ta daga kai alamar eh, Dady yace "ya fadama wani ne?"

Tace "ban gane ba?"
Yace "ya fadama wani kamar mai gidan nan cewar Goggo ce ta haifeki?"
Jalila tai shiru, yace "ba dai duk wani sirri na gida kin fadamai ba?"

Jalila ta kalleshi yanzun ma batace komai ba, ya kalleta ransa a bace, badai duk wahalar da wulakancin da ya hadiye ba lokaci daya wannan yarinyar zata zo ta ruguzamai? Dan ya tabbatar in har Taura ya kwace kudin daya basu tabbas Inna korar sa zatasa ayi daga company din.

Kallan Jalila yai rai a bace yace "Wai Habiba ba magana nake miki ba? Sai dai ki kalleni? Ko kema munafircin uwar taki zaki koya?"

  Jalila cikin tsoro ta kalleshi, hannunya daga a zuciye zai kai mata mari.
Jiyai ance " da alama sararka kenan?"

Juyowa tai da sauri ya kalli mai maganar, Jalila ma kallansa tai kawai sai ji tai hawaye sun zubo mata.
Karasowa yai cikin tafiyarsa ta isa sannan ya kalleta yace " tashi."

Mikewa tai tana kallansa, yace "bakiji me nacemiki ba ne da zaki zo?"

Tace "me kace?"
Yace “sau nawa zan ce miki ki canza tone in zakiyi magana? Meyasa bakyayi da confidence?”

Kallan juna sukai, hawaye ya gangaro mata, juyawa yai ya kalli Dady wanda yai tsuru tsuru.

Hassan ya kalleshi yace “ gobe zanzo muje dakai asibiti inda aka kwantar da mahaifiyarta, a gabanka zakasa hannun sallama mu amsheta.”
Dady yace “me kake nufi?”

Yace “abinda zuciyarka ta baka, u don’t deserve to be a father nor a husband.”

Kallan Jalila yai yace “wuce mu tafi.”

Kallan Dady tai gabanta na ci gaba da faduwa, Hassan ya kalleta ya mata alama data fara fita, nan ta fita tana waiyaye.

Tana fitowa daga bangaren falon taga Sageer a tsaye a jikin bango.
Yana ganin ta fito ya matso da sauri yace “ Jalila”
Hawayenta ta share sannan ta kalleshi, yace “menene?”

Kallansa tai kamar zatai magana sai kuma ta fasa ta juya tai gaba, Sageer yace “Akwai abinda ya faru ko? Naga yaya ya shiga kuma shi bai fito ba.”

Juyowa tai ta kalleshi sannan ta juya kawai ta hau sama da gudu.

A falo kuwa

Hassan ya kalli Dady yace “me ka samu, na saida yarka dakai?”
Dady yace “me kake nufi?”
Hassan yace “yanda kai da manyanka iyayen gidannka kuke nunawa, kunayi ne kamar kun samu wani abu sosai wanda yasa kuka bada yarku.”

Dady ya kalleshi yace “Hassan ta ya zaka ce haka? Kana so kace rashin so ne yasa muka aurar da ita?”
Yace “sosai, inba rashin so ba kun taba tambayar ya mijin nata yake? Wasu halaye gareshi? Me nene aikinsa? Ya mu’amalarsa da jama’a take? Duk kunyi wannan tambayar? A matsayinka na uban yarinya?”

Dady ya kalleshi yace “Inna tayi bincike ita ce tasan mahai.......”
Ya katseshi rai a bace “wacece ita? Menene matsayinta agun Jalila?”

Dady yace “bangane ba?”
Hassan yamai wani kallo yace “ karka manta gobe zanzo in banzo ba jibi zanzo, in kuma har kukai tunanin yin abinda bai kamata ba, zan baku mamaki.”
Ya juya bai jira mai zai ce ba ya fita.


Dady haka ya fito gaba daya kansa yayi nauyi, Sageer ne kawai a falon yamai sallama ya fita, yana cemai ya gaida Taura.


Mota ya shiga yai gaba.

Sai daya je kofar gida sannan yai parking a gefen mota ya kashe motar ya fito yana tunanin abinda zai fi mai mahimmanci, danshi rayuwarsa itace gaba da komai, mai zaiyi dan cigaban sa?


Hassan kam yana haura beni kansa na wani juyawa da kyar ya kai kansa daki yana shiga ya kwanta.

Jalila na falo tana ganinsa ta taso dan dama ta kasa ko zama ne.
Yana shiga a shiga dakin itama, akwance ta ganshi akan gado, taje kusa dashi tana san mai magana sai dai ganin idanunsa a rufe tasan bayasan magana, balle ya juya mata baya.

Ta dan dade a tsaye kafin ta fito.

Karfe tara tai shimfida ta kwanta, shikam tunda yai sallah ya sake kwanciya bai sake ko motsawa ba balle ta samu damar magana.

Shikam takaicin abinda ke faruwa a gidansu ne yake damunshi, meke damun Abba? Meyasa ita wannan rayuwarta take a cude? Meyasa abubuwa ke faruwa haka? Yau ce rana ta farko dayai fada da magana mai tsayi haka, gaba daya kansa wani irin sarawa hakeyi, ya dade sosai kafin bacci ya daukeshi.

Jalila kam ta dade a kwance kamar tana bacci, me suka fada da bata nan? Taya uba wanda ya haifeta zai dinga mata haka? Hawayenta ta share data tuno rayuwar da mahaifiyarta tai, lalai bazata bari Goggo ta cigaba da zama dasu ba.

Juyawa tai saitin da Hassan yake, ta haska wayarta, ganinsa tai a dukunkune ta mike ta dan rage A.C din dakin sannan ta matso inda yake, kansa baya kan pillow din, in dagashi? Ganin yanda ya kwanta a takure.

Hannu tasa a hankali ta daga kansa ta daura akan pillow din sannan ta juya ta kwanta.

Shikam tana tabashi yaji ta, har sai data kwanta idanunsa na bude juyawa yai shima saitin da take kwance, duk da ta kashe hasken dakin ba ganinta yakeyi ba, sai dai ya samu kansa da tsurawa gun ido kafin ya maida idanunsa ya rufe.


*************

A kasa kuwa, Ummy ce tasa kayan baccinta ta sa hijab tana neman fita daga dakin.
Abba ya kalleta yace “ina zaki?”

Tace “Dakin Ameera, ni kam kamar munyi kuskure da mun sani dakin can mun gyarashi.”

Kallanta yai yanda take mai magana kamar bawani abu na sabani a tsakaninsu.

Abba ya kalleta zaiyi magana wayarsa tai kara.

Kallansa tai tace anama waya, ta juya ta fita.

Zaliha ce, kashe wayar yai gaba daya sannan ya mike ya fito daga dakin.

Dakin Ameera ya shiga, Ummy tana kade gadon ya bude kofar, kallansa tai tace “ya akai? Ko akwai abinda kakeso?”

Abba ya kalleta sannan ya shigo ciki ya zauna akan gadon yace “ Kinsan gwara kiyi fada?”
Tace “fada kamar yaya?”

Yace “wannan abinda kikeyi it really scared me, gwara ki nunamin ranki ya baci in ma hakuri ne na baki.”

Tace “ munyi fada dakai ne?”
Kallanta yai, tace “ kai da Hassan ne kukai fada akai na wanda ni banaso, sai dai ya zanyi? Banaso naga kuna irin wannan akaina, tunda nake dakai na taba hanaka aure?”

Yace “ kece kuwa kike da yanda zakiyi tunda akanki akeyi, ke kadaice kike da dama hana fadan, sannan maganar aure nasan tunda nake dake ban taba sha’awar kawo wata mace gidana ba, yanzun ma ni kaina bansan meke damuna ba.”

Ummy ta kalleshi tace “ saboda kanasan ta shine ka hauni da fada waccan zuwa akan zaka koma Abuja, sannan yanzu kace bakasan meke damunka ba? Ni mubar wannan maganar, ni matsalata da damuwa ta akan Hassan ne, dan Allah ka daina barin yana sanin abinda ke faruwa a tsakaninmu, kafi kowa sanin halinsa in har yasan ina cikin damuwa, banaso Sageer ko Ameera ma susan wannan maganar, na rokeka da Allah, in aure zakayi kayi, wannan ra’ayinka ne sannan rayuwarka ce amma Please karka bari yarana su shiga wani hali a dalilin abinda kakeso.”

Abba ya runtse idanu cikin takaicin abinda ya dade yana ginawa, wato farin cikin gidansa na neman wargajewa a dalilinsa.

Ummy ya kalla cikin wani yanayi na tausayawa sannan yace “Maimuna ina cikin wani hali........”

Yanda yai maganar ne yasa ta tsaya tana kallansa sai dai tausayinsa ne ya kamata, dan bazata taba manta irin wannan muryar ba daya zo mata da ita a can baya shekaru masu yawa, a lokacin kalmar nan sai data sata kuka mai yawa, yanzun ma hannunta tasa akan nashi sannan ta zauna a gefensa tace “ In kanasan ta ka aureta, in dai shine matsalar, ni zanma Hassan magana, sai dai kafi kowa sanin baka isa ka zaunar da ita a gidan nan ba, in har baso kake danka ya mata illa ba.”

Kallanta yai cikin rauni yace “ba santa ne matsala ba, ni gaba daya abinda ke damuna ne matsala, n rasa a yaushe na fara santa, a yaushe naji in banganta ba bazan iya rayuwa ba, na rasa a yaushene na fara amsa mata akan duk abinda tazomin dashi.”


Ummy ta kalleshi cikin mamaki tace “me kake mufi?”

Ya kalleta yace “kizo mu kwanta, banajin dadin abinda mukeyi, me kike tunanin zai faru in Hassan ya ganki anan? D’a nane sai dai duk duniya nafi shakkarsa akan kowa, sannan shikuma indai akanki ne ba abinda bazai yi ba.”

Ummy bata musa ba ta mike sukai daki, kwanciya sukai, tace “baka fadamin matsalar ba.”

Yace “gobe zan gaya miki mike faruwa wanda na kasa ganeshi.”

Ummy tace “Allah yaa kaimu.”

Nan sukai bacci............

Sageer kam gaba daya ya kasa bacci, daga bayama mikewa yai ya zauna akan gado ya kunna fitila yana tunani, anya bashine sillar komai ba?

Gaba daya tausayin Jalila ya hanashi rintsawa......
******

A can gidan Inna kuwa, Inna sai kiran wayar Dady take bai dauka ba, yana kallan kiranta yaki dauka, sai data kira sau hudu sannan ya daga yace “gashinan zuwa.”

Ajiye wayar yai ya koma mota, dan ya gama tunanin mafitarsa, yasan kuma yanda zai buloma abinda ke faruwa dashi..........



#OneLuv💕


🗯 *JALILAH* 🗯

Written By : *AYUSHER MUHD*
✔ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*


     *HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
  (_D home of expert and perfect writer's_💡)



*40*

Washegari......


Jujuya cokali kawai takeyi a cikin cup din tea din, jefi jefi tana kallansa ta kasan ido tanasan mai magana, shikuma yana zaune a kasan yanacin abincinsa kamar ba wani abu dake damunsa.

Can dai ta tattaro dauriyarta tace "hmm yaya nace......"
Kallan daya mata ne yasa ta maida bakinta ta rufe tare da kallan cup din ta cigaba da juya cokalin.

  Yana gama ci ya mike ya shiga toilet, wanka yai sannan ya fito.
Kallansa tai ta ganshi daga shi sai towel dake daure a kasa, da sauri ta juya baya tare da rufe fuskarta da tafin hannunta bai bi ta kanta ba harya saka kayansa, sannan ya dawo gaban madubi yana shafa mai, yana gamawa ya fefesa turare.
Jalila ta juyo ta kalleshi, matsowa kusa dashi ta danyi kadan tace "Yaya bakacemin komai ba."

  Bai tanka mata ba ya dau wayarsa da makullin mota ya fita, tana tsaye ya rufo kofar.
Kallan kofar tai cikin mamaki a fili tace "mekenan?"

  Takaici ne ya kamata ta zauna a bakin gadon dabas tama rasa me zata ce.

Hassan yana sauko kasa ya sa hannu ya kwankwasa kofar dakin Abba.
Bude kofar Ummy tai sannan ta kalleshi, tace "Hassan kaine?"
Ya gaisheta sannan ya kafa leka dakin yace "Abba fa?"
Tace "yanzun nan yadan fita waje gun garden waya zaiyi."
Waya? Waye ya kirashi?
Ummy ta kalleshi tace "Hassan!"
Kallanta yai fuskarsa ta fara canzawa, tace "Please Hassan ka dinga sama zuciyarka salama, ka dinga hakuri, Abbanka namiji ne yanada hakkin auran duk wacce yakeso..........."

Juyawa yai bai jira ta gama magana ba yana neman tafiya, tace "Hassan magana nake."
Ya juyo ya kalleta yace "Yahkuri Ummy abu zanyi ne cikin gaggawa."

Kamar zata sake magana sai ta fasa, ta bishi fa kallo, Allah sarki Hassan tafi kowa sanin irin kaunar da yake mata.

Garden ya nufa, Abba na tsaye yana waya ya karasa gun, kallan Abba yai kallan zargi, Abba yace "Hafiz Please ka barni tukunna."
Bai kara jiran yayi wata magana ba ya katse layin, Hassan ya kalleshi kamar zaiyi magana sai kuma ya gaisheshi.

Abba ya amsa yace "Hassan."
Kallansa yai yace "kai da wanene haka?"
Yace "business ne ba wani abun ba uban yan zargi."
Hassan ya juya kai sannan yace "me kaba iyayen Yarinyarnan a maimakon auranmu?"

Abba ya kalleshi cikin mamaki yace "Hassan menene?"

Hassan yace "bakomai, kawai dai so nake nasani, dan na tabbatar give and take kukai da rayuwar ta."
Abba yai shiru kafin can yace "Bakasanta ne ko me? Ko wani abun ne ya faru?"

Shiru yai baice komai ba, kamar kuma zai saie magana sai ya juya zai tafi, Abba ne yace "Company dinsu ne ya ke neman yin Bankrupt shine na taimaka musu."

Hassan ya kalleshi sannan yace "yarinyar fa? Have u take care of her?"
Abba yace "kamar ya kenan?"
Hassan ya kalleshi yace "Abba ina dai sone a komai zakayi ga dinga tuna wacece Ummy a garemu."

Abba ya kalleshi yace "Hassan just pray for me, wlh nikaina bansan meke damuna ba."

Hassan yai shiru yana kallansa, Abba yacigaba "yanzu zan fada mata abinda ke faruwa itama, Hassan kafi kowa sanin family na are above komai na rayuwata ciki kuwa har da ni kaina, kasan yanda zan iya sadaukar da komai saboda su, sai dai i feel like there is definitely something wrong with me, na rasa yanda zanyi in cire yarinyar daga raina, as if samin ita akai a ciki."

Hassan kallansa yake, sai dai yasan mahaifinsa tabbas wannan kalaman daga zuciyarsa suke fitowa.

Kallansa yai yace " nafahimceka sai dai bansan meyasa zuciyata take blaming dinka ba, bawai baka iso kaso kowa bane sai dai Ummy doesn't deserve this treatment."
Abba cikin takaici yace " Ba so kadai bane a raina Hassan, mata nawa nake hulda dasu? Zance ba macen da ta taba burgeni ne? No kawai na riga nasa Ummynka ne beyond every woman, sai dai wannan karan it look like obsessed, inaji kamar dolene sai na sami yarinyarnan ko ta wani hali ne."

Hassan zaiyi magan, Ummy wacce hankalinta ya kasa kwanciya gani take kamar yanzun ma fada sukeyi yasa ta biyoshi, jin kalaman Abba ne yasa ta tsaya tana jinsu, sai dai yanzu kam idanunta ne suka zubo da kwalla, muryarta na rawa tace "it look like akwai babbar matsala a tare dakai"

A tare suka juya suka kalleta, Ummy ta karaso tace "just one month, ka bamu one month, ka daina kiranta sannan mu dukufa da addu'a musa nalamai ma su maka, in har a wata dayan nan dukda haka bakaji santa ya ragu a ranka ba ni na amince ka aureta."

Ummy!" Hassan ya fada yana kallanta, tai murmushi tace "in har a wata dayan kaima ka amince dani, karka nemeta sannan ko ta nemika ko a wayyane karka daga ko ka canza number"

Abba yace "na amince."
Hassann ya kallesu yana sanyin magana, Ummy tacee "Hassan please."

Idanunsa ya runtse, Abba yai murmushi tare da dafashi yace "Hassan bakasan dadin da nakeji ba, sauki ya fara samuwa da alama wannan auran rahama ne a gareka damu baki daya."

Hassan ya kalleshi sannan ya kalli Ummy, juyawa yai sannan yace "Shikenan Ummy tunda ke kikeso, sai dai ni ba one month ba ko shekara kikaba Abba bazan aminceba."

Ummy tai murmushi tace "nagode my eldest."

Juyawa yai yabar gun, mota ya shiga sannan ya fita daga gidan.


Jalila kam ta dade a zaune kafin ta dauko tiren abincin.

Akan dinning taga Sageer yana breakfast, da alama ma fitowarsa kenan dan tea yake hadawa.

Yana ganinta ya kura mata idanu har ta iso inda yake, gaisheshi tai, idanunsa na kanta yana nazarin fuskarta ya kasa amsa gaisuwar.

Kallansa ta sakeyi, yanzu kam ita kanta ta fahimci da abinda ke dakunsa dan duk fuskarsa ta canza,  tace "Uncle bakada lafiya ne?"

   Flask din ya ajiye sannan ya zauna yace "a'a me kika gani?"

Tace bakomai, wuceshi tai ta ajiye tiren abincin, kallanta yai yace " Yaya fa?”
Tace “ya fita.”

Shiru yai sai binta da kallo da yakeyi.

Jalila ta ajiye sannan ta fara dauraye kwanukan da sukai amfani dashi.


***********

Hassan na fita ya hau titi yana tafe yana tunani, meyasa yarinyarnan bata iya fita a ransa? Ya rasa me yasa in yaji ko yaganta cikin damuwa hankalinsa baya kwanciya.

Daren jiya ya tuno wajen karfe uku da rabi, kansa dake ta sarawa ya hanashi bacci, jin kamar ana kuka da magana, mikewa yai ya kunna fitilar gefen gado.

Jalila ce da alama mafarki take, kusa da ita yaje ya zauna yana kallanta, alamar kuka takeyi tana magana kasa kasa, kunensa yasa kusa da bakinta dake motsi.
“Dady, Mumy, Inna na kuyi hakuri karku kori Goggo dan Allah, na daina, na daina......”

Abinda take cewa kenan, hankalinsa da tausayinta sune suka kara ratsahi, addu’oi ya mata sannan ya kamo hannunta ya rike yana kallanta.

Ya rasa me yake tunani a sanda yake kallanta, meke faruwa dashi? Is he feeling guilty? Tunda yasan dalilinsa ne yasa aka mata auran dole? Sai dai abinda yakeji ya banbanta...... ya dade sosai har sai dayaji anata kiraye kirayen sallah sannan ya mike yai alwala.

A kofar gidansu yai horn ya shiga, Mumy da Dady na zaune a falo, Yasmeen na gefe tana shan chocolate tana wasa aka sanar dasu zuwansa.
Ba Dady kadai ba har Mumy sai da gabanta ya fadi, ta kalli Dady da sauri tace “ Dadyn Yasmeen meke faruwa? Cikin rawar baki yace bansani ba nima wallahi.” Yafada yana tuna kalaman Hassan badai zuwan dayace zaiyi yau ko gobe ba shine yai?

Mumy ce ta bada umarnin akan a shigo dashi, ita kuma tai sama da sauri.

Inna na zaune tana jiran Dady wanda tun jiya take sa ran ganinsa amma baizoba haryanzu.

Shigowar Mumy ne yasa ta kalli kofar ta dauka Dady ne, ganin Mumy yasa tace “ya akai kuma?”

Mumy da sauri tace “Inna yaran ya dawo.”

Tace “yaro? Sultan?”

Da sauri tace “bashi ba, mijin Jalila.”

Inna ta kalleta da sauri tace “ya dawo ina?”

Mumy tace “yana gidan nan, bansan dame yazo ba.”

Inna ta mike hankali a tashe tace “gidan nan?”

Mumy tace “yana falo.”

Inna ta dau mayafi ta fito, mumy ta biyota a baya tana cewa “Inna

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login