Showing 126001 words to 129000 words out of 146738 words
Chapter 43 - JALILAH HAUSA NOVELS BY AYUSHER MUHD.txt
Cikin tashin hankali tace "ni kasa na rasa me ma kake nufi da kalamanka."
Yace "ba sai kin gane ba a wannan lokacin, saboda munacin crisis din da muke bukatar mafita cikin gaggawa, Anjima karfe 10 za'a sauke Inna daga matsayinta a bashi, bawai bashin bane matsala shi din ne matsala, dolene kizo ki kwace company din da mahaifinki da mahaifiyarki suka sha wahala gun ginashi."
Hawaye ne ya cika a idanunta fal, tace "yanzu me ya kamata muyi? Sai dai inaji kamar ina betraying din mijina akan san zuciyata."
Ya runtse ido yace "dan Allah na rokeki da Allah ki tashi daga baccin da kikeyi, ki duba sosai kiga wanene ke betraying din wani tsakanin ke dashi, sannan ki duba mahaifiyarki da mahaifinki."
Mumy tai shiru kafin tace "yanzu me ya kamata muyi?"
Yace "dolene a cikin dayan biyu mu zabi daya, ko dai kiyi amfani da shares dinki ki ja ra'ayin directors din, ko kuma mu nemi wanda yai investing a company din ya baki matsayin."
Shiru tai tana tunani kafin tace "plan din farko ama cireshi dan na riga na bashi shares dina, plan na biyu kuma da matsala saboda investors din gidan mijin yarsa ne."
Inalilahi wa ina ilaihi raji'un Sani ya hau fada kafin yace "ki taimaka ki hadani da Hajiya muyi magana ma tabbatar ita zatasan yanda za'ai."
Mumy ta share kwallarta tace "Inna tana asibiti ba lafiya."
Sani ya runtse ido yace "shikenan magana ta kare,haka Allah yai, ya jikin nata?"
Mumy tace "gatanan dai a kwance."
Yace "shikenan sai nazo dubata, da alama ba sai nake company din bama."
Mumy tai shiru hakan yasa yace "sai anjima."
Ya kashe wayar, Mumy ta dafa kanta dake sarawa, agoggo ta kalla karfe bakwai da rabi na safe, wayar Abubakar ta sake kira, bayan tayi kira biyu ma sai ma taji an kashe wayar gaba daya, shiru tai tana kallan wayar sannan ta kalli Inna, tunowa ta dingayi da kalaman Inna daya bayan daya tun kafin auranta da Abubakar yanda ta dinga neman hanata suna fada akan itafa sai shi, to itakam ai haryanzu tana sansa kuma ta tabbatar akwai wani misunderstanding ne a tsankaninsu dan Abubakar bazai mata haka ba, da kwacewa yakesan yi da ai tuntuni halayensa dake boye sun fito.
Lalai ko saboda Inna tasan ba hakan bane gaskiya dolene ta binciko gaskiyar al'amari ko kuma kila dai da akwai wani abun.
Sai dai ta ina? Taya zai nemi taje gidansu Jalila?
Inna ta kalla wace ke kwance, yanda mahaifiyarta da mahaifinta suke kaunar company din yanda sukasha wahala gun kula dashi.
Idanu ta runtse tana tunani, hawaye ne suka sake zubo mata, kukan Yasmeen ne ya dawo da ita hankalinta, mikewa tai da sauri tazo ta dauketa tace "Yasmeen ganinan."
Yasmeen ta rungumeta sannan ta fara neman komawa bacci.
Tana komawa Mumy ta kwantar da ita sannan tadau waya ta kira Safeena, tana dagawa tace "Mumy lafiya da safan nan?"
Mumy tace "dubamin ko Dadynku na nan."
Nan ta mike tai dakinsu wayar na kunnenta tana cewa "Mumy nikam meke damun Dady wai?"
Tace "me kika gani?"
Tace jiya sai barbaza takardu yake a daki na shiga kamar yana neman wani abun, sannan da na fito kai plate kitchen najishi yana waya yana cewa "nagode yallabai bazan manta da hallacin da akamin ba, kn dai na zama chairman i will definitely fulfil your wishes."
Cikin tsananin mamaki Mumy tace "meyake nema?"
Safeena tace "bansani ba."
Ta karasa maganar tana knocking, jin ba amsa yasa ta tura kofar dakin, bakowa a ciki tace "Mumy ya fita."
Mumy tace "shikenan kidanzo asibiti inasan fita ne."
Tace "okay bari nai wanka dan naga har ma angama break din da za'a kawo."
Mumy ta kashe wayar tare dayin shiru tana tunani, me yake nema? Sannan wanene yallabai?
Ganin batada mafita yasa ta mike tana zarya a tsakiyar dakin.
Safeena na shigowa ta zari mayafinta tace mata ina zuwa.
Fita tai ta hau motar da aka kawo Safeena dan daka drivern ya shigo duba Inna, tace mai gidan Jalila.
************
Hannunsa yasa a cikin kasan rigarta tasa hannu ta rike hannunsa tare da cewa "Yayah?"
Yace "wai abin haryanzu bai wuce ba?"
Tace "menene bai wuce ba?"
Yace "gashinan gaba daya sai wani mazewa kikeyi, kindai san na fiki iya hade fuska ko?"
Ta kalleshi tare da cewa "nifa ba hade fuska nake ba."
"Ohh tafiya ne bakyasan yi dani ko me?"
Tace "Allah ba haka bane Yaya kawai dai bansan yanda zan sauka kasa bane, nasan yanzu Abba ya fadawa Ummy."
Yace "ikon Allah! To sai me? Ai ko bai fadaba ni zan fadamata."
Cikin shagwaba tace "haba yaya?"
Yace "to naji bazan fadaba, Abban ya fada mata shikenan?"
Ta kalleshi kamar zatai kuka, da alama Yaya bazai gane ba, agoggo ta kalla tace "oh ya kamata na sauka kasa fa."
Ta fada tana neman saukar da kafarta daga kan gado, Yaya ya jawota tare da cewa "yanzun ma fitar za'ai a barni?"
Cikin zolaya tace "ko zamu tare? Sai ka tayani?"
Ganin yanda ya tsaya yana kallanta yasa tai dariya tare da rufamai bargo ta mikomai littafi tace "malam mai karatu ai karatu dayawa."
Ta mike ta fita tana dariya, Yaya kam birgeshi tai, gani nai ya mike ya zura doguwar riga kawai ya sauka.
Jalila kam sam batai tunanin zai kawo wani abun a ransa ba, kitchen ta nufa, yau kam tai sa'a Ummy bata fito ba, dadi ne ya kamata ta wuce kitchen tare da tunanin abinda za'ai breakfast dashi.
Jan nama ta dauko ta shiga wankewa, sannan ta fara yanka albasa tana dan kankane ido.
Jin hannu ta bayanta yasa gabanta ya fadi, a tsorace ta juyo yanda ya riketa yasa tana juyowa ta juyo daf daf da fuskarshi, sumbatarta yai yace "na sauko, da me zan tayaki?"
Kallan kofa tai sannan ta kalleshi cikin mamaki tana kokarin zamewa tace "Yaya!"
Yace "da me zan tayaki?"
Tace "tayani? Yaya in wani ya ganmu fa?" Ta fada tana dan zamewa, yace "ohoo naga ke kika ce na sauko?"
Baki ta bude tace "wasa fa nake maka kaima ka sani."
Yace "wasa? To ya akai ban sani ba? Sannan banaji kema kincemin wasan nan kikeyi."
Baki ta bude tana kallansa tace "lalai yaya, me zance in su Ummy suka ganka anan?"
Yace "me zakice kuwa? Kawai mijinki ne yake taimaka miki."
Dariya tasa tace "a haka sauki fada."
Yace "a can din ma sauki zai.....yi"
Yai maganar yana kara jawota, tace "Yaya Allah kar Ummy ta fito."
Sumbatar wuyanta yai yace " wasa wasa da ke matsoraciya ce."
Tace "naji, nayi surrender, ayi hakuri, hanuna a sama."
Ta fada tana daga hannayenta.
Murmushi yai sannan ya saketa tare da bude fridge, sannan ya rufe yace "yanzu a haka zan tafi?"
Tace "hmm dan Allah yaya jeka ko falo ne,wallahi bansan ya zanyi ba in wani ya ganmu anan."
Baki ya tabe sannan yace "za'asan an koreni wallahi."
Ya juyo tare da hade fuska.
Da sauri tace "yaya?"
Tsayawa yai fuska a hade, ta matso ta dan daga kafafunta ta sumbaci kuncinsa, tace "sorry!"
Kallanta yai fuska a hade yace "wannan karan wannan bai isa ba."
Ya fita, kallansa tai tana murmushi har batasan tasa wuka a kusa da bakinta ba sai dataji warin albasa sosai yasa tai saurin sauke hannunta tana dariya.
Yaya ma yana fita yadan harari kitchen din sannan yace "chance din ramawa ya samu."
Yana kokarin bakin falon Sageer na fitowa, kallansa yai yace "Yaya? Daga ina?"
Yace "hmm na fito gaida Ummy ne naga batanan."
Sageer Yace "oh wallahi da sassafe suka fita itada Abba, sunje Bauchi, ka duba wayarka har text ta maka kai da Jalila."
Yace "Bauchi? Wani abun ya faru ne?"
Yace "wallahi ban sani ba, inaji dai zasu je gun dangin Baffanane, sannan kila akwai abin aiki da ya kaisu daga nan."
Hassan yace "Shine baka bisu ba?"
Sageer yace "kasan halinsu, in Ummy taje sai sun mata gori, gwara ni naje daga baya."
Hassan ya jinjina kai yace "Hakan yayi, kace kai kadai ne a gidan kenan?"
Yace "hmm amma nima anjiman nan zan fita zanje office din Abba akwai abinda ya sani."
Hassan a ransa yace "kenan sai mu kadai?"
Amma a fili yace "hakan yayi, ya kamata ka dinga fita ko ka samoma Ummy wata surikar tunda dai kaga ni tafiya zanyi."
Sageer yai dariya yace "kar ka damu an kusa."
Hassan yace "haba? Ka gano wata ne?"
Sageer ya matso sai tin kunnensa yace "na gano amma bansan ko inada chance ba."
Hassan yasa dariya zaiyi magana sukaji ana knocking din kofa.
Sageer ya karasa ya bude.
Mumy ce tsaye a gun, Sageer ya kalli Hassan sannan ya kalleta.
Ganin haka yasa Hassan din matsowa.
Kallan mamaki ya mata kafin yace "Bismillah."
Mumy ta shigo jiki a sanyaye.
Abinda takeyi hakan ya dace kuwa? Anya kuwa ta kyautama Abubakar?
Zama tai a kasa sannan ta kalli Hassann da Sageer.
Hassan ya kalleta yace "lafiya?"
Kallansa tai sannan ta hada hannayenta biyu tace "Hassan ku taimaki Inna ta da ni kaina da kuma Mijina, ku duba girman Allah. Bawai abinda muka aikata ba ku taimaki rayuwarmu."
Yanda take magana da karfi yasa Jalila lekowa.
Ganin Mumy yasa ta tsaya tana kallanta, Hassan ya kalleta sannan ya kalli inda Jalila take, Sageer ka ya kalleshi.
#OneLuv💕
🗯 *JALILAH* 🗯
Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
*71*
Mumy ta kalli Hassan idanunta sun ciciko, idanunta duk sun koma kalar tausayi, ta kara daga hannunta alamar tsananin neman taimako, tama kasa magana sai hannunta kawai datake ta murzawa.
Hassan kam Jalila ya kafa ma ido yana kallanta, wacce tai tsuru tana bin Mumy da kallo.
Sageer ne ya kalleshi yanda yaga yana kallan Jalila ne yasa yace “Yaya?”
Hassan ya kalli Sageer sannan ya kalli Mumy, daurewa yai yace “meke faruwa?”
Mumy ta kara kallansa idanta duk ya canza zuwa tausayi, kallan inda Jalila take tai a hankali tace “Jalilah?”
Jalila wacce gabanta ke ta dukan uku uku tana tsoron kar ace wani ya mutu, tsoron matsowa takeyi, Mumy ta kara cewa “Jalila!”
A hankali Jalila ta fara takowa zuwa inda take, tana tafe gabanta na wani irin faduwa, kusa da Hassan ta matso ta tsaya a hankali itama tace “Mumy menene?”
Mumy ta kalleta tace “Jalila ki rokarmana mijinki da mahaifinsa su taimaka su dakatar da mahaifinki.”
Cikin rashin fahimta ta kalleta tace “dakatar dashi kamar ya?”
Nan mumy ta kwashe abinda ke faruwa ta sanar musu sannan ta dora da cewa “bawai hanashi company din nakesan yi ba, dan ni a gurina yafi kowa dacewa daya mulki company din, sai dai ina tsananin tsoron kar san zuciya ya jefashi cikin wani halin, sannan bansan me yake kitsimawa a ransa ba, ance yanata duba takarda a gida, da farko ban kawo komai a raina ba sai dai bayan na taho ina hanya na fahimci me yake nema, takardun gidan da muke ciki yake nema, dan dama tun shekara uku da suka wuce nasa aka canza sunan gidan daga sunana zuwa nashi, saboda na kwantar mai da hankali, kenan korar mu zaiyi daga gidan, ni duk na rasa me Abubakar yake kitsimawa a kwakwalwarsa.”
Hassan wanda ko kadan baiyi mamaki ba yace “yanzu halayen mijinki kike sanar mana anan? Ko kuma halin da kuke ciki ke dashi?ni na kasa fahimta.”
Mumy tace “Hassan ka dubi girman Allah ka taimaka mana, na tabbatar in wani abu ya samu company din Inna wallahi mutuwa zatai.”
Yace “Rai a hannun Allah yake, in lokacinta yayi banaji ke ko ni mun isa mu dakatar dashi.”
Ya fada tare da juyawa ya wuce sama.
Mumy ta bishi da kallo kafin ta matso kusa da Jalila, hannunta ta riko tace “Jalila?”
Jalila ta kalleta, idanunta sun ciciko itama, Mumy tace “Jalila na san bamu kyauta miki ba ko kadan, ke da mahaifiyarki, mun wulakantaku daidai wulakanci, sai dai inaso ki dubeni ta fuskar fahimta bawai dan ke akayima ba, a’a ki dubeni a matsayinki na mace, ya zakiyi idan wanda kike masifar so rana daya yazo miki da mace sannan da tsohon ciki? Ya zakiyi in mijin da kike masifarso ya nemi ku barsu su zauna a muhallinki? Ya zakiyi in kikaga mijin naki baisan darajarsu ba, basu isheshi kallo ba bare ya nuna damuwarsu akansu?”
Jalila tai shiru tana kallanta, Mumy tashare kwallarta tace “Nasani bazaki fahimceni ba, na kuma san ban kyauta muku ba daga ke har Goggonki ko da Abakar bai nuna damuwarshi akanku ba ni kuma baikamata na maidaku kamar masu aiki ba, sai dai Jalila ki dubeni a matsayin ba kowa ba, dan Allag ki ceshi mai neman bukata, Jalila Inna tana cikin wani mawuyacin hali.”
Jalila tai shiru tama rasa me zatace muryar Sageer taji yace “ Please in kin gama ki fita.”
Shima ya wuce ciki dan shikam gani yake ko kadan basu cancanci a taimaka musu ba.
Mumy ta kalli Jalila ta kamo hannunta tace “Jalila!”
Jalila ta daure tace “Mumy zan shiga ciki.” Ta karasa tana dan zare hannunta.
Jalila ta juya zata tafi,muryar mumy taji “Safeena ta dawo.”
Cikin mamaki Jalila ta juyo ta kalleta tace “ta dawo daga Abujan?”
Mumy ta girgiza kai tace “ba abuja taje ba, fita da ita abroad mukai karatu sai dai alhakinki ne inaga yasa gashi ta dawo ba karatun ba kuma jin dadin, ta fita a banza mun kashe kudi a banza sannan me makon ta dawo cikin farinciki ta dawo cikin kunci.”
Jalila tai shiru tana kallan Mumy, kafin Mumy tace “kinga yanda rayuwa take Jalila, a da bamu daukeki a komai ba, yar mu kawai muka sani yanzu gashi kece a matsayin komai, ki duba darajar da Allah ya baki, ki rokarmana Sirikinki da mijinki su taimaka mana.”
Jalila tai shiru, sai dai ya zatayi? Ko da ace naman jikinta suka dinga yanka, yan uwanta ne, duk duniya batada kamar Safeena, Sultan da Yasmeen, dan jini ba wasa bane.
Yanda Mumy ke kara rokarta ne yasa tace “bari na mai magana, sai dai ko da wasa Mumy karkisa ran zasuyi abinda kikeso, ni dai zan yi iya nawa ne, ba kuma dan kowa zanyi ba sai dan Allah da darajar yan uwantaka.”
Mumy ta hau gyada kai tana cewa “nagode Jalila, nagode.”
Jalila ta shiga kitchen ta rage gas sosai sannan ta fito tai sama, Mumy ta bita da kallo, rayuwa kenan, wai su da sunyi tunanin cutar da ita sukai, sun killace tasu, sai gashi ashe daukakata sukai, hawaye ne ya kara taruwar mata sai yanzu hankalinta kadan kadan yake kai mata manufar Abakar, yanzu kam ta fara tantama ma in har yana santa.
Jalila ce ta tura kofar dakin, yanna zaune yana latsa waya ta shigo, kusa da kafarsa ta zauna dan yadan jasu sama.
Sa kanta tai saman gwiwoyinsa, ta dan karkato da kanta gefen da wayar take tace “Yaya! Shine ka gudu ka barni?”
Kallanta yai tare da ajiye wayar yace “Bansan me zance miki bane, shiyasa na taho.”
Ta dan rufe baki kadan kafin tace “me zaka cemin kamar me?”
Yace “mahaifinki ne, me zance?”
Kanta ta kwantar akan gwiwar tasa kafin tace “mahaifina ne sai dai tunda nake dashi Yaya ban taba zama dashi munyi maganar mutunci ba, duk maganar da zata fito daga bakinsa zakaji san zuciya ne da tsantsan san kai.”
Hassan yai shiru yana mata kallan tausayi, murmushi tai kafin tace “ sai dai Yaya duk yanda naso na gane na kasa fahimta.”
Ya mata kallan rashin fahimta, tace “wani irin uba ne Dady? Yaya duk yanda naso na kasa gane wa.”
Fuskarsa ya sa ko kusa da tata, yace “wanda baisan baiwar da Allah ya mai ba?”
Tace “baiwa?”
Kiss ya mata yace “baiwar yarinya kamarki mana.”
Idanu ta kankance tana kallansa kafin tace “ahh yaya.”
Murmushi yai kafin yace “yau kinsan mu biyu ne a gidan nan?”
Murmushi tai sannan tace “kafin mu zama mu biyu kadan taimakamin kadan.”
Name? Tayaki breakfast din zanyi? Ya fada yana dan kamo gefen cikinta.
Dariya tasa tace “kai Yaya!”
Yace “ba su bane?”
Tace “ka taimakeni kar Dady zuciyarshi tai nisan da bazata taba waiwaye ba.”
Yace “kamar ya?”
Tace “banaso mahaifina idanunsa ya rufe, ina tsoron halin da zai afka, baya tunanin komai sai kansa, shiyasa nakeso a dakatar dashi haka daga kan san kansa da yakeyi, ya fahimci yanada responsibility’s da kuma abinda yafi shikansa daraja.”
Yace “yanzu me kikeso ayi a tsayar dashi?”
Tace “dan Allah ka taimaki Mumy, hakkinsu ne company din nan, mahaifinta da mahaifiyarta sune sukasha wahala gun ginashi, taya Dady zai zo lokaci daya ya nemi kwacewa? Bayan na tabbatar da yayi hakuri Mumy yanda take sanshi da kanta ma zata bashi, kaga alama ce ta san zuciyata da tsantsar burin rayuwa ne yake damunsa, wanda ya rufemai ido daga taimakon da aka mai, yake ganin kamar komai ya cancanta ne shiyasa ake mai?”
Hassan ya sa hannunsa yaja kumatunta kamar wata baby sannan yace “ohhh wannan babyn da alama ta mike tsaye.”
Bai saki kumcin nata ba ta shiga kokarin magana tana cewa “Yaya Please!”
Dariya yai yanda tai maganar yace “to ni kinsan bansan kan harkar ba, ta ina zan taimaka miki?”
Tace “ muje mumy sai tama bayani, lokaci yana kurewa.”
Yace “Hmm umm.” Cikin shagwaba yai tasa dariya tace “da alama in an gama wannan zan kara nema amin abin nan.”
Fuska ya hade yace “haka kawai ina murna zamu zauna mu biyu yanzu kuma kinzo da wani zance daban?”
Tace “sry yaya.”
Ajiyar zuciya yai sannan yai gaba.
Da kallo ta bishi sannan tai murmushi, bin bayansa tai.
Kasa suka sauko Mumy nata amsa waya tanata magana da Sani.
Tana ganinsu ta kashe wayar tare da gyara zama.
Hassan ya sauko kofar Sageer ya nufa tare da yima knocking.
Sageer da ya bude kofar ya kalleshi.
Hassan yace mai “Sageer dan fito plx.”
Fitowa yai tare da rufe kofar.
Jalila kam na saukowa kitchen ta nufa kawai ta cigaba da harkarta.
Duk da hankalinta nakan abinda ke faruwa a falo sai dai ta sa wa ranta abu daya, duk abinda Hassan ya yanke